← Book details Neehal Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 118

Sashe 63

Neehal Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Ƙarfe huɗu da mintuna ta fito daga exam ɗin kuma Alhamdulillahi ta mata sauƙi, masallaci ta nufa ta yi sallah sannan ta kira Haneefah dan su je su dubo Ameen dake fama da zazzaɓi. Haneefah ta sanar mata bata gida sun fita kasuwa da ƙanwar Mommy, kasancewar bikinta ya gabato saura sati uku, dan ma exam ɗin da suka fara ne da tuni an yi bikin. Yanzu sai bayan Babbar Sallah da sati biyu za'ayi. Sallama Neehal ta yiwa k'awayenta ta tafi. Sai wajen biyar ta ƙarasa gidan. Babu kowa a falon ƙasa hakan yasa ta nufi sama, a nan ta tarar da k'awayen Hafsat su uku zaune a falo. Ta musu sallama ta shiga, suka amsa suna bin ta da kallo. Ta zauna a kujera sannan ta gaishe su. Cikin fara'a Fadeelah ta ce "Laa Neehal ke ce, ai ban gane ki ba da farko sai yanzu." Neehal ta yi murmushi ta ce "Aunty Hafsan tana ciki ne?" Fadeelah ta ce "Eh wanka take, ki shiga Yayan naki yana cikin ɗakinsa." Neehal ta ce "Toh." Tare da miƙewa ta shiga ɗakin. Ɗaya daga cikin k'awayen Hafsat ta ce "Wannan yarinyar kamar mai aiki a ASTV ko?" Fadeelah ta ce "Ita ce, ƙanwar Ameen ce fa." Wadda tai maganar ta ce "Allah sarki, Ni kam tana burgeni, yarinyar a nutse take bata da rawar kai." Fadeelah ta ce "Ga ta da kirki wallahi so friendly babu ruwanta."

Neehal ta tura ƙofar ɗakin Ameen a hankali bakinta ɗauke da Sallama, bayan ta yi knocking ya ba ta izinin shiga, k'amshinsa ne ya fara mata Welcome. Yana kwance akan gado jikinsa sanye da jallabiya brown colour idanunsa a lumshe. Neehal ta ƙarasa ta zauna akan bedside locker tana kallonsa cikin tausayawa, ya ƙara haske kuma ya ɗan faɗa. Hannunta ta kai a hankali ta taɓa wuyansa ta ji jikin nasa da zafi, Ta zare hannunta a hankali daga jikinsa ta ce "Allah ya baka lafiya Yayana." A hankali ya buɗe lumshashshun idonsa ya sauke su a kanta. Ta ce "Yaya! Sannu, ya jikin?" Bai amsa mata sai tashi zaune da ya yi yana taune lips ɗinsa. Cikin murya mara sa lafiya ya ce "Yaushe kika zo?" Neehal ta ce "Yanzu na zo, ya jikin naka?" Ya ce "Da sauƙi, ina Mum?" Ta ce "Tana gida daga school na biyo ta nan." Ya jinjina kansa tare da lumshe idonsa, daga gani babu tambaya ka san yana jin jiki. Neehal ta ji duk hankalinta ya tashi dan baza ta iya tuna sanda ya kwanta ciwo irin haka ba, hannun damansa ta kalla ta ga abun ƙarin ruwa. Kamar zata yi kuka ta ce "Yaya me yake damunka? Mama ta ce mun zazzaɓi kake, kuma na ga kamar ba iya zazzaɓin ba ne kawai." Kafin Ameen ya bata amsa wayarta dake cikin jakarta ta fara vibrate, ta zuge jakar ta ɗauko wayar tare da d'agawa ganin Sadik ne. "Hello Yaya Sadik." Jin haka yasa Ameen ya juyo da sauri ya kalle ta, ta ce "Eh na dawo, ina gidan Yaya na je duba shi." Ta ɗan yi shiru na wasu sakanni sannan ta ce "Tom sai ka zo." Tare da kashe wayar. Ameen ya mayar da idansa ya lumshe a hankali ya ce mata "Bani ruwa." Da sauri ta ɗauko ruwan dake gaban gadon ta buɗe sannan ta tashi ta miƙa masa tare da faɗin "Sannu Yaya Allah ya sauwaqe." Ya d'aga mata kai tare da karɓar ruwan ya sha. Ganin yanda ta damu sai ya kamo hannunta a cikin nasa yana kallon fuskarta ya ce "Menene?" Ta yi ƙasa da idonta ba ta ce komai ba, ya d'ago hab'arta  da ɗayan hannunsa ya ce "Don't cry." Dan ya san halinta, ai ko kamar zugata ya yi sai ta fara hawaye, ita haka Allah ya halicce ta idan ta ga mutum ba shi da lafiya duk sai ta ji ta damu sosai, musamman ma Yayan nata da take jin kamar ta mayar da ciwon nasa jikinta. Ya ɗan tauna lips ɗinsa murya ƙasa_ƙasa ya ce "Kukan na mene?" Ta ce "Yaya baka da lafiya, na ga duk ka rame." Ya ce "Ai na ji sauƙi, kuma soon zan warke Insha Allah." Ta gyaɗa masa kanta. Ya yi ɗan murmushi sannan ya shiga goge mata hawayen fuskarta da tattausan tafin hannunsa ɗaya, ɗayan kuma yana riƙe da hannunta har lokacin. Dai_dai time ɗin Hafsah ta turo ƙofar ɗakin ta shigo.........✍️
[7/21, 9:30 AM] Zee data: *âš¡ NEEHALâš¡*

_By_
_Zeey Kumurya_

*3️⃣8️⃣*

Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*

*I selling MTN data with this cheap price*

*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500

Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*

*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp OR*
*Call 08066268951*
Chapter 63 · 0% Book details