← Book details Neehal Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 100 OF 118

Sashe 100

Neehal Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

Jikin Hafsan da sauƙi ta tarar da ita, tunda tun daren jiyan akay mata ƙarin jini da wankin ciki. Tana kwance akan gadon marasa lafiya, sai mahaifiyarta da mahaifinta a ɗakin. Mama tay mata ya jiki, suka gaisa da parent ɗin nata cikin fara'a da mutunta juna. Kusan wuni Mama ta yi a Hospital ɗin tare da mahaifiyar Hafsah, Daddy ma ya zo ya duba ta da rana, da yamma kuma su Aunty A'isha da Aunty Sadiya suka sun zo. Mama ta kira Driver ya kawo su Dije tare da abincin data saka su, su girka. Ƴan'uwan su Hafsat ma suna ta zuwa duba ta. Tun zuwan Mama ta fuskanci Ameen yana cikin damuwa da b'arewar cikin Hafsat, ko tantama bata yi ya k'walla fa ransa akan cikin ne Allah kuma ya yi ba mai fitowa doron ƙasa ba ne. Tay masa addu'ar Allah ba su wani. Sai can yamma Mama ta dawo gida, lokacin Neehal itama bata jima da dawowa ba. Mama ta sanar mata abun da ya faru, ta ji ba daɗi sosai akan barewar cikin itama, dan duk sun san Hafsan na da ciki, har tana ta murna a ranta sun kusa samun new Baby. A daren ranar aka sallame su Hafsah, mahaifiyarta ta so tafiya da ita gida amma Ameen ya nuna bai so hakan ba, Mahaifin Hafsah kuma ya goya masa baya, ya ce tunda jikin nata da sauk'i ta wuce gidanta kawai. Dole mahaifiyar ta_ta, ta haqura, ta ce zata samo mata dattijuwar da zata na kula da ita har ta samu sauƙi, kamar wata wadda ta haihu, bayan kuma already tana da masu aiki ƴan'mata har guda biyu.

A daren Mama tana part ɗin Daddy suna hira ya ce mata. "Son fa ya kira ni d'azu in nemar masa alfarma a gurin ki." Mama ta ce "Alfarmar me?" Ya ce "Wai Daughter yake son ki ba su ta je ta musu ɗan kwana biyu, kafin Hafsah ta gama warwarewa." Mama ta ce "Ba tana da masu aiki ba, me kuma Neehal zata je tay musu?" Daddy ya ce "Kin san ɗan naki, ba ya cin abinci masu aiki." Mama ta ce "Ohh girki zata je tana yi masa kenan? To ban yarda ba, idan dan abinci ne zan na badawa akai musu." Daddy ya ce "Dama sai da ya ce mun baza ki bari ba, shi yasa ma ya kira ni, in lallame ki, ki barta ta je Doctor, kin ga akwai abubuwan da dole masu aiki baza su iya yi masa ba tunda matarsa bata da lafiya, amma ita Neehal ɗin zata iya masa." Mama tay shiru, Daddy ya ce "A taimaka mana ƴar Amaryata." Ya ƙarashe zancen da dariya. Mama ta ce "Ka ce mun amarya mana tunda zaku yaudare ni kai da ɗanka." Ya yi dariya sosai ya ce, "Yanzu dai kin bari ya zo ya ɗauke ta da safe? Just 1 week za ta yi ta dawo." Mama ta ce "Ka san ba zan iya har 1 week babu ƴata a gabana ba." Ya ce "Idan kuma da Allah yasa an yi auranta fa?" Ta ce "Aure daban, wannan na san gidan miji na kai ta ba gidan Ameen da basa shiri ba, Neehal rigima da shiririta shi kuma masifaffe, ta yi abu kaɗan ya rufe mun ƴa da masifa, na yarda dai tay musu kwana biyu ta dawo." Daddy ya ce "To hakan ma, mun gode, bari na kira shi na sanar masa.

Washegari wajen ƙarfe tara na safe Neehal tana breakfast a ɗakin Mama. Maman kuma tana karatun Alkur'ani mai girma, bayan ta kammala ta ce "Ki yi ki gama uwar janjani, Ameen zai zo ya ɗauke ki, ki je gidansa ki musu kwana biyu." Neehal ta d'ago da sauri har tana k'warewa ta ce "Mama kwana biyu kuma?" Mama ta ce "Eh, kin ga Hafsan bata da lafiya, zaki ɗan taimaka mata da wasu ayyukan, ita kuma ba k'annena ba bare su je su taya ta." Kamar zata yi kuka ta ce "Amma Mama tana da masu aiki fa." Mama ta ce "Ki je dai Neehal, mene in kin je kin taimaka mata, Dad ne da kansa ya ce ki je." Neehal ta fara hawaye tare da ture abincin gabanta, ita ba zuwan ne damuwarta ba, yanda zata zauna gida ɗaya da Ameen har na wasu kwanaki ne damuwarta, dan tun ranar da ta dawo daga gurin Sadik suka haɗu a bakin part bata ƙara bari sun haɗu ba, wasan b'uya take da shi, saboda tsoron punishment ɗin da ya ce zai mata. In ya zo gidan tana nan har ya tafi bata fitowa daga ɗakinta. Tana matsar hawaye ta ce "Mama aikina fa, kin ga ban jima da komawa ba, kuma ina siwes." Mama ta ce "In kin je can ɗin ma zaki na zuwa ba wai daina zuwa zaki ba, kina gama ayyukan ki sai ki tafi, idan Ameen ɗin yana gida da kansa ma zai dinga kai ki." Ta saka kuka ta ce "Ni dai Mama....." Mama ta haɗe rai ta ce "Bana son iskancin banza, mene a gidan Ameen ɗin da baki son zuwa? Ko yayyanka naman jikinki za'ai in kin je? Ki tashi ki je ki yi abun da na ce, tunda kin gama cin abincin. In kuma ban isa ba ne to." Ta tashi tana kuka ta fice daga ɗakin. Mama ta bi ta da kallo, tana sane da su kwana biyu ita da Ameen ɗin, da wasan b'uyan da take da shi, shi kuma idan ya zo gidan ya dinga baza ido kenan yana neman ta inda zata ɓullo. Ta girgiza kai tare da yi musu addu'ar shiriya a cikin ranta.........✍️
[7/21, 9:32 AM] Zee data: *âš¡ NEEHALâš¡*

_By_
_Zeey Kumurya_

*5️⃣5️⃣*

Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*

*I selling MTN data with this cheap price*

*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500

Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*

*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp OR*
*Call 08066268951*131*4#*
Chapter 100 · 0% Book details