← Book details Neehal Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 108 OF 118

Sashe 108

Neehal Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Haneefah data ƙura mata ido tana sauraren ta, ta numfasa ta ce "Yanzu Neehal ke a karan kanki kin kasa zaɓar wanda zuciyarki ta fi so, ta yaya wani zai iya zaɓar miki? Ke baki san wa kika fi so a cikin su ba?" Cikin damuwa Neehal ta ce "Wallahi ban sani ba Besty, na kasa tantancewa, idan ina tare da wannan sai in mata da waccan." Haneefah ta ce "To duk ba son su suke ba." Neehal ta dube ta cikin mamaki tare da faɗin "Kamar ya?" Haneefah ta ce "Kamar yadda kika ji na faɗa, ai shi wanda zuciya take so baya b'uya, Neehal da ace kina son Sadik ko Ahmad idan kina tare da ɗayan su ba zaki taɓa mantawa da wanda kikewa son gaskiya a ba a cikin su. Daga Sadik har Ahmad tausayin su kawai kike ji, ko kuma wani a cikin su yana miki wani abu da yake burge ki, and kuma kina duba halacci ko kyautatawar da sukay miki a rayuwarki, amma so dai da k'auna na soyayya ba kya yiwa Sadik da Ahmad. Ni nafi tunanin akwai wanda zuciyarki take so, wanda ke kanki baki sani ba." Neehal ta ɓata fuska ta ce "Ni babu wani wanda nake so daban kuma, to wani saurayin ne dani bayan su da zan so shi?" Haneefah ta ce "Wanda ba kya taɓa mantawa da shi a cikin ranki, ko da kuwa kina tare da Sadik da Ahmad. Indai akwai wanda kike jin haka a kan shi to shi kike so." Neehal ta tab'e baki ta ce "Babu shi gaskiya, kema kin sani." Haneefah ta ce "Lokaci ne zai faɗa mana haka, amma now back to our business, wa kike ganin hankalinki ya fi kwanciya da shi a tsakanin su?" Neehal ta ce "Wannan ita ce tambayar da Mama tay mun, kuma na kasa tantancewa, shi yasa na zo mu haɗu mu tantance." Haneefah ta ce "Indai a yanda kika bani labari ne gaskiya zan fi so ki auri Sadik, saboda yanda yake da rauni akan soyayyar ki, kece mace ta farko da Sadik ya fara so a rayuwarsa, idan kika rabu da shi saboda Ahmad kin zalunce shi, saboda sai da ya gama sakankancewa ya samu mata sannan kuma ki canza zance. Time ɗin da Ahmad ya dawo cikin rayuwarki already kuna tare da Sadik, dan haka yanzu idan kika bar shi kin yaudare shi, kuma hak'k'in shi ba zai barki ba. Sannan kuma ki duba yanda danginsa ba kowa ke son ku tare ba, idan kika rabu da shi kika watsa masa ƙasa a ido za ai masa dariya, ace shi yana ta wahala a kanki ashe ma ke ba k'aunar sa kike ba, kuma Sadik ya riga Ahmad fara sonki." Neehal ta yi sauri ta ce "Uncle Ahmad ya riga, na faɗa miki fa tun ina yarinya farkon haɗuwar mu yake so na." Haneefah ta ce "Ai wancan lokacin daban, kuma ya wuce. Zancen yanzu ake da girmanki, amma ni dai shawara nake baki, dan ni Baban twins ɗin nan ma bai wani mun ba, ya miki tsufa, gwara ki auri saurayi ɗan shawalwali wanda zaku fi jin daɗin rayuwar auranku. Kuma na lura kalaman Ahmad da iya tsara mace ne suke rud'ar ki a kansa, dan na san ki da son soyayya, da son a nuna miki k'auna." Neehal ta ce "Ni duk ba wannan nake dubawa ba, ina duba taimakon da yay mun a baya, ni kuma yanzu yana buƙatar nawa sai in ƙi taimaka masa? Kuma ga yaransa da muka shak'u da su, bana son rabuwa da su" Haneefah ta ce "Idan dan Allah yay miki ba zai yi wannan tunanin ba dan baki zaɓe shi ba, su Afrah kuma dan kin yi aure ai ba yana nufin kin rabu da su ba kenan, zaki cigaba da zumuncin ki da su, tunda Allah ne ya haɗa ku." Neehal ta yi shiru na tsawon mintuna biyu, sannan kamar zata yi kuka ta ce. "Haneefah! Uncle Ahmad yana so na Sosai, kuma duk abun da kika faɗa akan Sadik gaskiya ne, ya cancanci zama miji a gare ni, amma ban san da idon da zan kalli Uncle Ahmad na faɗa masa wannan maganar ba, Allah na yi dana sanin haɗa two dating at one time." Haneefah ta ce "Haka nan Sadik ɗin shima idan kika zaɓi Ahmad zaki ji nauyin sanar masa kin zaɓi wanin shi a matsayin miji. Neehal! matar mutum kabarinsa, tun kafin ki zo duniya Allah ya riga ya rubuta wanda zaki aura, ki yarda da wannan, ki kuma dage da addu'a da neman zaɓin Allah, tunda kin san dai baza ki auri maza biyu ba ko?" Neehal ta ce "Haka ne ƙawata, daren jiya ma kusan kwana na yi ina kaiwa Allah kukana tare da neman zaɓin sa." Haneefah ta ce "Yawwa, kisa a ranki kawai wanda kika zab'a shine mafi Alkhairi a gare ki, kuma shi Allah ya rubuta zai zamto mijinki." Neehal ta ji wani ɗan sanyi a ranta, lallai ta yarda shawara tana daɗi. A hankali kamar wadda aka tilasta mata ta ce "Na zaɓi Ya Sadik, Allah yasa haka shi yafi Alkhairi." Haneefah ta ce "Amin ya Allah, shi kuma Ahmad Allah ya bashi tasa matar mai Alkhairin." Kamar zata yi kuka ta ce "Amin, amma ban san yanda zai ɗauki wannan al'amarin ba, ina jin kamar ban kyauta masa ba." Haneefah ta ce, "Musulmi ne fa shi, kuma ya san qaddara mai kyau da mara kyau, Insha Allahu zai fahimce ki. Amma fa ba forcing ɗinki nake akan Sadik ba fa, kawai ina baki shawara ne kamar yadda kika nema daga gurina, idan kin ji zuciyarki ta fi k'aunar Ahmad karki cuci kanki, ki zaɓi wanda kike so ki aura, dan aure ba abun wasa ba ne." Neehal ta ce "Hmm, Allah yasa ya fahimta ɗin. No, ni da Ya Sadik da Uncle Ahmad duk ɗaya ne a gurina, duk wanda na zab'a dai-dai ne, saboda duk sun cancanta." Ta yi shiru tare da ɓata fuska, sannan cikin damuwa ta ce. "Ni duk ba wannan ba ma, ina tsoron abun da ya faru a baya ya kuma faruwa." Sai ta fara hawaye sannan ta cigaba da magana. "Ina tsoron a kuma kashe mun wanda zan aura yanzu ma." Haneefah ta ɓata fuska ta ce "Oh my God, Neehal har yanzu baki daina wannan banzan tunanin ba, kin manta Allah ne me rayawa da kashewa." Neehal ta girgiza kai kawai ba ta ce komai ba, hawaye na cigaba da shatata a fuskarta. Haneefah ta matso ta rungume ta, cikin lallami ta ce. "Insha Allahu, Besty babu abun da zai faru sai Alkhairi, Allah yana sane da ke, ki miƙa masa k'ok'on bararki, shi kuma da yardarsa na san zai kawo miki ɗauki. Kuma duk wanda yake kisan nan matuƙar dan ke ake yi bisa zalunci da son zuciya Ubangiji zai saka miki cikin gaggawa, dan Allah yana karɓar addu'ar wanda aka zalunta. Kuma rayuwar mumuni bata tafiya sai da jarrabawa, ke kuma wannan ita ce taki jarabawar, amma in kika yi haquri sai ki ga komai ya wuce tamkar bai taɓa faruwa ba, be a good Muslim please Dear." Haka dai Haneefah tay ta nusar da Neehal da nasihohi da kalamai masu daɗi gami da ƙara mata k'warin gwiwa akan Sadik, daga baya kuma ta koma tsokanarta da matar Barrister, an kusa shiga daga ciki. Har ta ji zuciyarta ta mata sanyi, kaso mafi yawa na damuwar da take ciki ya tafi. Shi yasa take son Haneefah, because mutum ce har da ƙari, kuma ta san baza ta taɓa bata shawarar da zata cutar da ita ba. Amma wani b'arin na zuciyarta sai tambayar ta yake akan anya ta yiwa Ahmad adalci kuwa? Sai bayan Magriba sannan ta bar gidan, shi ma sai da Mama ta kira ta a waya, dan sosai ta ji daɗin kasancewa da Besty'n tata.........✍️
[8/7, 9:21 AM] Zee data: *âš¡ NEEHALâš¡*

_By_
_Zeey Kumurya_

*5️⃣8️⃣*

Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*

*I selling MTN data with this cheap price*

*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500

Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*

*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp OR*
*Call 08066268951*131*4#*
Chapter 108 · 0% Book details