← Book details Neehal Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 118

Sashe 11

Neehal Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Misalin ƙarfe goma da rabi na dare Mama ta na ɗakinta a zaune a kan darduma ta na lazimi, domin babu d'igon bacci ko kaɗan a idonta, bayan tafiyar su Aunty Sadiya gidajensu Dad ya koma part ɗinsa, ita kam Mama yau ko part d'in nasa ba za ta iya zuwa ba, saboda damuwar da take ciki, don sosai ta damu da wannan al'amari, domin ba ta k'aunar abin da zai taɓa Neehal ko kaɗan a rayuwar nan, balle abin da zai taɓa farin cikinta, amma tasan ba ta isa ta goge rubutacciyar ƙaddarar da Ubangiji ya zana mata ba a rayuwarta. A hankali ta ji an buɗe ƙofar ɗakinta an shigo, a tunaninta Dad ne, amma jin k'amshin turaren Ameen ya sa ta d'ago kanta da sauri ta kalle shi, kansa a ƙasa ya yi sallama tare da nufo inda take, Mama ta ɗauke kanta daga Kallonsa tare da amsa masa sallamar da ya yi a zuciyarta. Kusa da ita ya zauna kansa na ƙasa still ya ce "Mum!" Mama ta ɗan kallesa ta watsar amma ba ta ce komai ba, ya ƙara faɗin "Ya haƙurinmu?" Mama ba ta amsa masa ba sai cewa ta yi "Me ya samu phones ɗinka?" Ba tare da ya yarda sun haɗa ido ba ya ce "Kashe su na yi" Mama ta ce "Akan wanne dalili" ya ɗan yi shiru na wasu sakanni ita kuma Mama ta tsura masa ido. Cikin dakiyarsa ya ce "Aikin da ya kaini Lagos ne ba ƙarami ba ne, kuma ina so in gama shi a yau gobe kawai sai dai a rabawa masu yi, that is why na katse wayar kar a kira ni a tsayar da ni." Mama ta yi shiru dan ita ta damuwarta take a halin yanzu, shima shirun ya yi, amma ba ka isa ka gane ko wani abu ya na damunsa ko akasin haka ba a halin yanzu.

Washegari Neehal ta tashi jikin nata da ɗan dama, dan Mama a gurinta ta kwana, tun dare jinin ya ɗauke mata, hakan ya sa da asuba ta yi wanka ta yi sallar ta, ta daɗe ta na wa Anwar addu'ar samun dacewa, da waɗanda kullum da koyaushe cikin yi musu take, da Jameel da ma dukkan Musulman da suka rigamu gidan gaskiya baki ɗaya. Zuwa yanzu zuciyarta ta gama tsinkewa ta haƙura ta fawwalawa Allah komai, Amma kallo ɗaya Mutum zai mata ya hango ramar da ta yi lokaci ɗaya, bayan ta gama addu'o'inta ta janyo wayarta wadda rabonta da ita tun jiya, missed calls d'in da akai mata take dubawa, Numbobin da ta sani da wanda ba ta sani ba gasunan rututu har ta rasa kiranwa ma za ta bi. Aranta ta ce "Da waninta ne ya mutu ba Anwar ba, da har da missed calls d'inshi za ta gani, kuma shi kaɗai za ta iya bin kiranshi, wani abu ta ji ya tokare mata a k'irji, a hankali ta shiga App din free kur'an ta buɗe ta fara karanta Suratul Baƙara, domin ta san shi kaɗai zai mata maganin abun da yake damunta. Ta yi nisa a karatun Ameen ya shigo ɗakin, ba ta ma san ya shigo ba har ya yi sallama, saboda hankalinta gabad'aya ya na kan karatun da take, a ƙoƙarin ta na ganin ba ta ba wa damuwa damar zama a cikin zuciyarta ba, sai dai k'amshin turarensa da baya b'uya ya sanar mata da zuwan nashi, ta d'ago da kanta da sauri cikin mamaki dan ba ta san ya kwana a gidan ba, gabanta ya faɗi haɗa idon da suka yi da shi, ta ɗauke idonta da sauri daga kallon shi bugun zuciyarta na ƙaruwa ba tare da tasan dalili ba, nufar inda take ya yi cikin takunsa na ƙasaita da burgewa..........✍️
[7/21, 9:00 AM] Zee data: *âš¡ NEEHALâš¡*

_By_
_Zeey Kumurya_

0️⃣8️⃣
Chapter 11 · 0% Book details