← Book details Nakasa Ba Kasawa Bace Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 154

Sashe 12

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 2 Complete Hausa Novel · about 1 min read

By
*GARKUWAR FULANI*
10/4/20, 7:04 PM - Mmn Khalid: _Shafinga ƙyauta ne gareke babana, Ali Wambai, inai maka fatan al'khairi a rayuwarka, yaro mai sunan manya Allah yasa ka samu nagarta irin na masu sunan naka_

A hankali ya lumshe Kyawawan idanunshi, tare da furta.
"Masha Allah!." a cikin zuciyarshi sosai tayi masa kyau acikin shigar wedding gown ɗin nata, har wani ƙyallin kyau take kamar wata tauraruwa, komai nata yazama wani na musamman,  cikin nutsuwa haɗi dajan aji irin na amare suka ƙaraso wajen motar Saifuddeen ɗin, da sauri Sule driver ya ƙaraso inda ya buɗe murfin motar da kansa, idanunta dake cikin wani ɗan siririn mayafi ta rumtse sakamakon ƙamshinsa da yadaki hancinta, sakamakon buɗe marfin motar da akayi, da taimakon Balkeesu tashiga cikin motar, ƙasa-ƙasa Balkeesu ke kallon Saifuddeen, sosai yayi bala'in yin kyau, saikace wani balarabe, komai nasa is perfect, sosai Saifuddeen ya haɗu, haƙiƙa musamman a irin wannan rana ko maƙiyinsa bai isa kushesa ba.
Zaleeha na gama shiga cikin motar Sule driver ya maida murfin motar ya rufe.
wata muguwar hararan Balkeesu ta abkawa Sule driver, cikin takaici tabi Rasheeda suka shiga wata mota ta daban.
Chapter 12 · 0% Book details