← Book details Nakasa Ba Kasawa Bace Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 100 OF 154

Sashe 100

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Cikin jin daÉ—i Samira tace.
"Alhamdulillah kinga wani hanin ga Allah baiwace,
yanzu dai ni bance kada ki liƙe mijinkiba amman ki dena kishin Zaleeha dan itafa matarsa ce ba karuwarsa bace kamar Dina da ya Amir so dan Allah ki sawa ranki salama, ki fauwalawa Allah lamarinki kamar forko, shi zai ɗaga daraja da kimarki a wurin mijinki wlh Abban Adeel yana sonki".
Dai-dai lokacin suka isa ƙofar gidan Samira, cikin sanyi Ameena tace.
"In sha Allah zan kula dan wlh ni kaina nasan Abban Adeel yana son farin cikina".
Kai Samira ta jinjina tare da cewa.
"Yauwa ƙawata ki kula gudun kada ki ɓarar da damarki sai gobe in mun haɗu zamu ƙara tattaunawar zan baki shawarwarin yadda zaki samu sauƙin kishin kuma ki yarda yana sonki."
Cikin jin daÉ—i Ameena tace.
"To Allah ya kaimu gashi yauma itace dashi gobema itace sai ran monday zan ƙarɓeshi kuma kinga ran monday ɗin munada off zan wuni a gida kusa da Mijina da ɗana, Allah dai ya bani ƙarfin hali irin naki, amman in sha Allah bazan sake tayar da hankali naba".
Amin Amin Samira tace lokacin data fita,
Kai tsaye cikin gidanta ta wuce, ita kuma Ameena taja motarta ta koma gida.

Koda Ameena ta dawo nono ta bawa Adeeli take kuwa yayi shiru kamar ba shine ya wuni koke-koke ba.
Anan sashin Ummin tayi magriba, tana idarwa kuwa ta tattara komanta ta wuce sashinta, dan yau ba itace da girki ba Zaleeha ce, shiyasa gaba ɗaya komai keneman dawo mata sabo donma tayi dace da shawarwari Samira aminiya ta gari mai imani ta nusar da ita ta koyi kauda ido kan miji da kishiyarta kada ta tsananta binciken cewar sai ta gano waya fi so a cikinsu ta kuma cire zargi, to Alhamdulillah kuma ta gamsu da shawarwarin Samira tasirin ƙawa ta gari kenan.

Zaleeha kuwa koda ta idar da sallan isha, wani haɗaɗɗen riga da wando me taushin gaske tasa, rigan irin mai hannun vest ɗinnan ne, tabi gaba ɗaya surar jikinta ta lafe, har takai ga ana iya hango shatin nipples ɗinta, dan batasa bra ba, wandon kuwa meɗan faɗi ne, amma duk da haka bai hana mayataccen hips ɗinta bayyana ba, dogon gashinta ta tubke sannan ta feshe gaba ɗaya jikinta da turare, wani irin kasala haɗi da bacci takeji, saboda hakane ma yasa batajin zata koma sashin Ummi, hayewa saman gadonta tayi, tare da jawo hand bag ɗinta, diary milk ta ɗauko, tare da ɓarewa, kwanciya tayi tana ɗan gutsuransa kaɗan kaɗan, wayarta ce ahannunta tana ɗan kallon hotuna a IG wanda duk hotunan Hamma Saif ne take gani wanda Hayatuddeen ke sakasu kamar ba gobe ta rasa me take ji a kanshi a haka ko mintuna 15 batayi ahaka ba, bacci ya ɗauketa, da diary milk riƙe ahannunta, takarasa akusa da bakinta, wayarta kuwa tabar data akunne saƙonni sai shigowa suke. Ɓangaren Saifuddeen kuwa saida akayi sallan isha kafun yake shigowa cikin gidan, sashin Umminsa yaje suka ɗan taɓa hira dasu Ahmad, sai wajen ƙarfe 9 ya nufo part ɗin nasu, kaitsaye ɗakinsa ya wuce, wanka yayi tare da shirya kansa cikin wasu kayan bacci masu taushi, sun kuwa yi masa kyau sosai, turarensa maidaɗin ƙamshi ya fesa, sannan ya nufi ɓangaren Ameena. Ahankali ya murɗa ƙofar ɗakin ya shiga, tana nan zaune akan gado, ko kayan bacci bata saba, ta zuba uban tagumi, ga kuma idanunta da suka cika da ƙwalla, gaba ɗaya komai bayayi mata daɗi, sam arayuwarta bata ƙaunar taga ranan girkin Zaleeha ya zagayo, saboda batason abun dazai nesanta ta da Saifuddeen ko kaɗan. Ganin yanda tayi tagumi ne yasashi ƙarasowa cikin ɗakin, hannun da tayi tagumin dashi ya sauƙe ƙasa tare da ɗan shafa gefen fuskarta, cikin body language ɗinsa ya dubeta, tare dayi mata alaman cewa. "Meke damunta?" Kallo ɗaya tayi masa ta kawar da kanta gefe, zuciyarta duk ba daɗi, sanin cewa idan ya matsa mata da tambaya, zata sake bayyana kishinta ƙarara, yasashi ɗan ƙarasawa ya sakarwa Adeel kiss agoshinsa, hannunta ya kamo, tare da ɗan lumshe idanunsa, alama yayi mata kan cewar saida safe, sannan ya juya akalan kekensa, tana kallonsa ya fice daga cikin ɗakin.

Samun kanta tayi da danne kishinta, kan gado ta faÉ—a tare da jawo pillow ta rungume tana fidda zazzafan numfashi.

Shikuwa Saifuddeen yayi hakanne dan shine abun da yafi dacewa, saboda yasan tsayuwarsa awajen nata, tamkar ƙara mata wutar kishi ne acikin ranta.
Ta cikin falonsa yabi, inda ya shiga sashin Zaleehan, dama baiyi tunanin ganinta acikin falo ba, hakan yasashi wucewa ɗakinta, ahankali ya tura ƙofar ɗakin ya shiga, sassanyan ƙamshin turare da kuma sanyin AC ne ke tashi acikin ɗakin, ɗan lumshe idanunsa yayi, tare da buɗewa, hangota da yayi akan gado ne yasashi ɗan ƙarasawa. Idanunsa ya zuba mata, tundaga kan ƴar yatsar ƙafarta yake kallonta, har ya gangaro zuwa ƙirjinta, wanda rabin breast ɗinta suka fito ta saman rigar, ga kuma shatin nipples ɗinta da suka bayyana kansu, ta cikin rigar, wani irin zubawa yaji tsikar jikinsa nayi, take yaji jijiyar jikinsa na neman miƙewa tsaye, saboda sexy dress ɗin dake jikin Zaleehan ya isa hautsuna tunanin duk wani ɗa namiji me lafiya, ahankali yaɗan lashi lips ɗinsa, tare da kai dubansa ga fuskarta, baccinta take cikin nutsuwa, ga kuma diary milk ɗin dake riƙe ahannunta, wani kyakkyawan murmushine ya suɓuce masa, saboda ya lura bata shiryawa baccin ba ya ɗauketa, gab da ita ya ƙaraso, tare da kai hannunsa yaɗan zare diary milk ɗin dake hannunta, ganin cewa chocolate ɗin yaɗan ɓata mata baki ne yasashi, kai hannunsa saman tausassun ƙaɓɓanta, yaɗan goge mata, wayarta ya ɗauka, tare da kashe mata datan, ya ɗaura mata wayar akan bedside, hannu yakai yaɗan shafi lallausan gashinta da ya watse akan pillow, anutse ya ɗan haɗe mata gashin nata waje ɗaya, idanu ya tsurawa kyakkyawar fuskarta, ji yake kaman ya buɗe cikin jikinsa ya sata aciki, kayan sunyi mata matuƙar kyau, ga kuma kyawawan breast ɗinta dake mugun ɗauke hankalinsa, saman breast ɗin nata yaɗan shafa, wani irin zut zut haka yaji mararsa nayi masa, take duk wani kuzarinsa ya kau, ahankali yaɗan ranƙwafo da kansa, kiss ya manna mata agoshinta, tare da ɗan shafa gefen fuskarta, jikinsa amatuƙar mace ya jawo blanket ya rufa mata, rage mata hasken wutan ɗakin yayi, sannan ya juya ya fice, gaba ɗaya jikinsa amace yake, wani irin fitinannen sha'awarta ne ke taso masa badan yasa a ranshi sai yaga ta nuna begenta gareshi zai kusancetaba tabbas da yau zai rabata da budurcinta, kaitsaye ɗakinsa ya koma ya kwanta, duk yanda kuwa yaso bacci ya ɗaukesa abun ya gagara, dan wani irin feeling ɗin Zaleehan yakeji, haka ya dinga juyi akan gado yana lumshe fitinannun idanunsa, sai wajen ƙarfe ɗaya kafun bacci ɓarawo ya sace shi.
Ameena kuwa, yaƙi tasha da zuciyarta harta godewa Allah, babu abun dake ɗaga mata hankali kamar yanda zuciyarta, ke raya mata cewar. "Yanzu haka Saifuddeen ɗin nacan jikin Zaleeha, sai take tuno yadda ta samu Ya Amir da Dina sai tanaga yanzu shima Saifuddeen da Zaleeha suna can manne da juna."
wannan tunanin shike ƙara dagula mata lissafi. Haka nan ta tsinci kanta da cewa.
"To sai meye ba matarsa bace, in sha Allah daga yau bazan sake sawa raina damuwar kishin baiwar Allah nan da take son É—anaba".
a haka tayi bacci cikin sanyin rai. Washe gari da safe kuwa, Zaleeha ita kaÉ—ai ta shiga kitchine tayi musu break fast, simple foods kawai tayi musu, sai kuma chicken egg rolls.
Ko awajen breakfast ɗin gaba ɗaya fuskar Ameena babu wata alamar damuwa, haka takejin zuciyarta a sauƙaƙe, cin abincin kawai take hankalin na kan wayarta.
Saifuddeen kuwa duk yana lure da ita, har acikin ransa yana fatan Allah ya ragewa Ameenan kishinta, dan yaga alama da kishin na sawa tana takura kanta da yawa, gashi kuma wacce take kishin dan ita, batasan ma tanayi ba, wannan shine sakai a wahala sai dai ya lura da nitsuwar zuciyarta.
Tun kafun sugama break fast ɗin ta miƙe dan tafiya wajen aiki.
Ya lura kamar bata fiyo son zaman gidanba yanzu tafi jin daÉ—in tafiya aikinta in ba ran girkinta bane.
Chapter 100 · 0% Book details