← Book details Mijin Malama Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 90

Sashe 59

Mijin Malama Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Debeka data sakko hannunta riƙe da handbag da waya kamar sauri take zata fita, harta gilma sai kuma ta tsaya sbd jin sukur sukur da take ga ƙamshin Khalil daya cika parlon, ta jima tsaye tana kallon Majeederh ganin yadda ta ƙara zama ƙatuwa, gently ta ƙarasa da nufin taɓa Majeederh ta ɗan bubbuga bayan Khalil da zaton na Jee ta ce "Hi" Cak! Majeederh tayi zuciyarta ta ɗan daina aiki na wasu daƙiƙu numfashinta ya fara ɗaukewa, da ƙyar ta saita kanta ta ce "Uhm" Debeka tayi tsaye ganin Majeederh bata juyo ba sai kuma ta ce "Na kira number sweetheart, baya ɗauka ki ce masa na ɗan fita....," Wani emotional sounds Jee ta saki tana yarfe hannu, sbd wani abu da Khalil yayi mata da bata taɓa tunanin akwai shi ba, tana jin yadda yake haɗa zufa ta cikin hijab kaɗai ta fahimci yanayinsa tayi ƙasa da murya ta ce What is this plx?" Can ciki ya ce "Zunubi nake rage miki" Debeka ta ce "Are you okay?" Majeederh couldn't speak, saboda bata nutsuwarta da ƙyar ta ce "Uhm" Debeka ta ce "Ok, bye" Tayi gaba Khalil ya manta inda yake ya ce "Bye dear" Debeka ta tsaya jin muryarsa, Jee tayi saurin rufe ido saboda kunya itama, Khalil ya kame fuska tare da ɗaga hijab ɗin ya fito kamar ya yi wanka da ruwan zafi sbd zufa, Debeka ta dinga kallonsa ya ɗaga shoulder clamly yana nufar gunta ya ce "Where? Ina?" Idanun Debeka ya cicciko da hawaye, ya kama hannunta suka fita waje Jee wani tashin hankali taji bazata taɓa jure ganin Khalil da wata ba, zuciyarta zafi take mata, ta sunkuya tare da mayar da rigarta ta gyara zaman pant din, daidai nan ƙyakƙyawan matar ta fito daga wani ɗan corridor hannunta riƙe da waya tana ɗan shafawa kamar bata so, wata lafiyayyiyar lafaya ce a jikinta white colour daka gani ba irin ta ƙasar nan bace, hannunta zube da zoben gold, farar ƙafarta akwai necklace mai kyau siririya, ta nemi waje ta zauna, da ɗan sauri Majeederh ta zube a gabanta kanta a ƙasa ta ce "He's coming, Ummi" Gimbiya ta ɗan kalli Majeederh, komai na majeederh irin na ƴar uwarta ne, babu abinda ya bambanta da ita sannu a hankali son Majeederh ke sauka a zuciyarta, na rabuwa tare kasuwa zuwa ko wacce ƙofa ta zuciyar tata, amma babu ko alamun hakan a saman fuskarta idan kaga yadda take kallon Majeederh zaka ɗauka babu so sai zallar tsana, bakinta ke motsawa tana son yin magana amma gabaɗaya laɓɓanta sun yi mata nauyi sosai, da ƙyar tana jan numfashi ta furta "Is he sleeping?" Kafin Majeederh tayi magana Khalil ya shigo a nutse cike da kamala yana wata kalar tafiya ɗaiɗai suna haɗa idanu da Jee ya yi mata harara, bai tsaya wahalar zagayowa ba, duk abinda zai bashi wahala baya so, ta bayan gujerar ya kama Jee na girgiza mai kai domin gabaɗaya bai kula da matar dake zaune ba, ya kama gujerar ya dirgo saman gujerar, still idanunsa akan Majeederh ya ce "I love you baby" wata waƙa ce ta Justin Bieber, ganin taƙi kula shi ya saka baki tare hura mata iska, tayi saurin ƙasa da kanta a ranta tana cewa "Ohhh my dear Khalil" Khalil ya lumshe idanunsa yana mai da numfashi, haka kurum ya ji nutsuwa na saukar masa a jikinsa, ya miƙar da ƙafarsa a hankali ya ji ya zunguru mutum ya buɗe fitinannun idanunsa wanda suka jirkice, idanunsa ya sauka akanta, itama ɗin shi take kallo ai da sauri ya hantsila har yana buge goshi, bai kuma sake yarda sun haɗa idanu ba ya miƙe ganin part ɗinsa ya masa nisa kawai ya shige ƙofar garden, Majeederh ta fahimci bawai gudun haka kurum ya kewa Ummi ba, akwai wani irin abu dake ɗawainiyya da shi, bai saba da uwa mahaifiya ba, shi yasa yake gujewa haɗuwar tasu. Majeederh ta miƙe zata bisa Gimbiya tayi mata gyaran muryar akan ta barshi. A hankali ta ce "Tell me something about him" Majeederh ta yi murmushi ta ce "He's stubborn" Calmly Gimbiya ta ce "I know" Jee ta ce "Khalil love's food"...

Khalil na zaune a office ɗin NAPTIP sanye da wata Brown suit ya ɗan jujjuyawa akan gujerar da yake kai kafin ya ce "Ohh" Mutumin ya ce "Shi wannan DDMASTER BOM ɗin babu wanda zai taɓa ce maka koda wasa ya taɓa ganin fuskar shi, har yanzu kuma jami'anmu na sirri basu samu information ɗin komai akan shi ba, abu ɗaya suka samu nasara shi ne yana yawan shiga Pakistan da Singapore, akwai wani sansanin su dako tsuntsune ya shiga baya fitowa da rai balle mutum" Gently Khalil ya jinjina kai, kafin ya ce "I'll like to know, me DDMASTER BOM yake?" Musbah ya juya ya zaro wani record ya ce "Mutum ne mara imani da tausayi, yana Creating muggan makamai wa Pakistan, yana Fataucin mutane wasu a cire musu ƙoda a siyar wasu Idanu, ga safarar mata manya da yara, yana forcing nasu to sex ga manyan masu muƙamai na ƙasa ƙasa, ana masu kuɗi su suna mayar da matan jarinsu ne, ga siyar da miyagun ƙwayoyi" Khalil was speechless the same time shocked and confused ya ce "Taya suke samun matan?" Musbah ya ce "Taya ake ruɗar matan da zummar aikatau a ƙasashen waje? Kuma ko tsufa kikai basa barin mace dawowa gida harbeta sukeyi, ko kina jinin al'ada sai sun yi tarayya dake" Khalil ya miƙe tsaye yana zagaye office ɗin a fili ya ce “DDMASTER BOM” Da sauri ya ce "Ni zan kawo ƙarshen shi" Musbah yayi dariya sosai ya ce "Mr President zai iya baka kariya, amma kana ganin zaka iya kare iyalanka? A yau zaka iya ganin an shigo gidanka an yanka matarka akan Idanunka, duka haka aka dinga yi wa ma'aikatanmu, mu rayuwarmu cikin kasada take da hatsari mai tarin yawa, matanmu kullum cikin zullumi suke"
"Zan iya, zan kashe shi da hannu na, zan sauke girman kansa zan kawo ƙarshen zaluncin shi" Musbah ya danna abu ya ce "Ka shiga jerin ma'aikatan NAPTIP, hukumar dake yaƙi da fataucin mutane ta Najeriya" Khalil ya sauke numfashi Musbah ya ce "Akwai Card, wanne suna za a saka maka wanda ba za a gane kai bane, domin komai hukumar mu a sirrince take" Khalil ya dinga tunani a fili kuma ya ce "MIJIN MALAMA" Musba ya yi murmushi ya ce "Done, ur card is done already, ka fara shirye-shiryen tunkarar DDMASTER, ka kuma fara tunanin yadda zaka kula da ilayanka all the best" Khalil ya amshi Card ɗin sannan ya fice, yana fita Musbaj ya miƙe ya rufe ƙofar.
A hankali yake zagaye office ɗin, sai kuma ya zaro waya ya kira wata number ana ɗagawa ya ce "Ur son is here" Ya yi shiru sai kuma ya ce "Da alama ɗanka na cikinka ya shirya kawo ƙarshen ka, Family issues kenan" Ya ƙara yin shiru yana saurare sai kuma ya ce "Ok Sir, babu mamaki ɗan ka ya zama silar kawo ƙarshen girman kai da jinkimar ka, ya kuma kawo ƙarshen wutar gabar dake tsakaninka da mahaifiyar shi" Musbah ya ce "An yi masa I.d card da suna MIJIN MALAMA, kamar yadda na saba fidda sirrin hukumar NAPTIP a wannan karan ma na turo maka kuɗi kawai nake jira" Yana gama faɗin hakan ya kashe wayar. Musbah ya saki wata dariya sosai ya ce.
"Let's watch and see, waye zai winning waye zai zama loser, DDMASTER BOM KO MIJIN MALAMA, Mr President or Dr Ibrahim-Khalil? Waye za a kashe President Denial David or Abraham Denial David?
[12/09, 11:29 pm] Sdy Auwal Gstc: *MIJIN MALAMA*

*BOOK 2 PAGE 82*
Chapter 59 · 0% Book details