Sashe 5
Mijin Malama Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Germany, Schloss Bellevue. Schloss Bellevue shi ne sunan dake maƙale a jikin Hammerschmidt Villa in Bonn, babba gida wanda zai yi unguwa guda white house komai na gidan fari ne, fenti, gate glasses everything. Sai green grass da flowers da duk suka kasance green sai rufin gidan da yake cofie ga red ɗin ƙaramar ƙofa a tsakiya wacce data kai ka har ciki, iya gidan tsakiya abin kallo ne balle wanda suke gefe da gefe, ga wasu tarin windows da doors birjik hawan benen gidan ba zai irgu ba, ga totar ƙasar Jamani a maƙale, ga kwalta kwance tako'ina securities da Escorts kamar ana yaƙi. Cikin sauri sauri yake taka ƙafarsa idanunsa a lumshe hannunsa ɗaya a sumar kansa ɗayan kuma a aljihu a haka yake rasata Escorts ɗin dake bashi hanya suna ɗaga masa hannu babu wanda ya kula, dake yasan the process of entering the house har zuwa part ɗin President bai sha wahala ba, har ya ƙarasa haɗaɗɗan parlourn wanda ya ji Italian furniture's, komai fari ne the chairs are all white. Yana shigowa parlourn ya saka ƙafarsa ɗaya ya daki ƙofa glasses ɗin jiki ya tarwatse. Dad ya ɗago idanunsa ya sauke akan Abraham yana ɗan yin murmushi wato mai hali baya taɓa fasawa. "Wlcm back Son" A hargitse ya ce "Dad!" Ya faɗa yana lumshe idanunsa sai kuma ya ware su tas akan Dad ɗin ya nufe shi tare da zubewa a gabansa muryarsa na ɗan rawa ya ce "Dad!" Dad ya ce "Yes sweetheart, go on" Abraham ya sake haɗe fuska yaƙi kallon mutumin dake ta Kallonsa ya ce "Dad! She's my girlfriend, ita ina so, ni ne zan aureta" Ya yi shiru, ya ƙara haɗe fuska a dole baya son raini musamman ganin yadda Dad ɗin nasa yake ta Kallonsa yana murmushi ya ce "Plx Dad I'm begging u ban so na rasata, Dad I'm matured enough" Dad ya ce "You're too young dear, ba zan bari ba, babba dalili Musulma ce, kai yaro ne baka isa aure ba" A fusace Abraham ya kalli Dad ɗin idanunsa har ruwa yake ya ƙara tarwatsa wani Glasses ɗin ya ce "I'm matured enough" Dad ya ce "ABRAHAM u're not, kai yaro ne, baka ka kai ka riƙe mace ba, baka kai ka riƙe gida ba, ba kai ka zama mijin wata ba, watan ma wacce take older than you" Dad ya girgiza kai yana murmushi tare da ɗauke kai zafin zuciyar ɗan nasa na bashi mmki ya ce "And the worst part of it har yanzu u're dependant" Cikin zafin rai sosai kamar zai daki Dad ɗin nasa ya ce "Dad, I'm not dependant; Allow me to from convert from Islam, na auri ƴar madara" Dad ya ce "Ahh ƴar suger, baka isa riƙe mata ba" Abraham ya ce "Na isa, ka bani dama na aureta in 9mnts za kaga ta bani babies bama ɗaya ba, zan iya riƙe mata" Mutumin dai kallon Abraham kawai yake. Dad ya girgiza kai yana haɗa rai shi ma nasa zuciyar ya motsa ya ce "Ka tashi ka bani guri kafin na saka Escorts kulle mini kai, har yanzu kai yaro ne baka shige a raineka ba, u're still young" Wani irin kallon Dad ɗin Abraham yake yama kasa ce masa komai me ya sa Dad ɗinsa baya son farin cikinsa ne? A hankali ya ce "I'm not a kid anymore, ka yi mini aure kaga idan ban ma jee ƴar madara ciki ba... [05/08, 10:30 am] Sdy Auwal Gstc: _*Arewabooks@Nimcyluv*_ For more updates "Ka faɗa mini waye zai zama mijin Malama na gaske wacce tauraron ta da na shi yazo ɗaya, na sake faɗa maka ko da wasa kada Abuturab ya taɓa kusantar Majeederh, dan tsinannya ce yadda kasan ayo yanzu zaka ganta da ciki, ni kuma bana son hakan ya kasance, burina a rayuwa tai ta yin ƙasa ni kuma ina sama, ina baƙin ciki da duk wani samunta, kuma nayi al'ƙawarin yadda za a fini kyau ilimi ta fini arziƙi da nasaba, to ba zan taɓa yarda da a fini da gidan miji ba, ba zan yarda da a fini farin ciki da kwanciyar hankali ba, Turzum kayi duk yadda za ka yi kada His Excellency Abu-turab ya kusanci Majeederh ko da sau ɗaya ne" Wani irin kallon Turzum yake mata, yaga mugwayen mutane kala-kala daban daban, yaga wanda suka haukata kishiyoyin su, naga wanda suka sabauta uwar miji, wasu ma faccaloli sbd kawai abin duniya,amma ya jima bai yi aikin akan wacce ke son ganin bayan aminiyyarta ba, makashinka na gidanka ta shiga rigar annabi Musa bayan zuciyar Fir'auna ne da ita. Turzum ya kwashe da mahaukaciyar dariya yana yi yana ɗaga ƙafa tare da sakin tosa, girman bakinsa kaɗai ya isa bawa mutum tsoro, balle daƙwa-daƙwan idanunsa ya gyara zama ya ce "An gama, yadda kike so haka nan za a yi azzalumar mugwayen wacce bata da rabon rabauta, zamu kwantar da kayan aikinsa zamu cire masa sha'awa" Latifa Omar da har lokacin take durƙoshe yafe da wani jan yadi ta ce "Da kyau uban bokaye Turzum, ka faɗa mini miliyan nawa kake so?" Ya buga mata tsawa ya ce "Kin jima da sanin mana amsar ko sisinki ni bana amsar kuɗi a aiki, wannan cikin dake mararki da zarar ya yi wata huɗu kawai ki zubar da shi, jinin ɓarin shi Aljanu suke buƙata zasu sha, matan da kike bi kuma a duk sanda kuke masha'a Aljanu na gefe suna kwashe ƙazantarku" Latifa ta miƙa hannu ta shafa mararta ɗumin na ratsa hannunta, wani irin so da ƙaunar cikin ya wanzu a zuciyarta, nan da nan kuma shaiɗan ya ƙawata mata muguwar niyya cikin sauri ta ce "Da zarar ya yi wata huɗun zan zubar, ina fatan dai aikin yanzu zaka mini ko?" Turzum ya ɗaga ƙafa ya ƙara sakin tosa ya ce "Lashakka yanzu zamu kammala komai, Aljanu kawai za kiwa al'ƙawari, bayan wannan ne kike buƙata?" Ta gyara zama ta ce "To ai matsalar kace asiri ba zai tasirin a jikinta ba, banda haka da ita Majeederh kawai naso a sabauta ta shiga duniya ko kuma ta kwanta jinya har ajalinta ya yi, kuma ko anyi aikin baya tasiri sosai tunda gashi dana saka ta zama mujiya a idanun maza anyi hakan, to daman kace mini duk sanda ta haihu asirin zai karye, to ni dai ta shammace ni ban ma san yaushe ta samu cikin ba, daga haihuwarta zuwa yanzu samari sai magana suke suna sonta daga ciki kuma har mijina Aliyu, kuma wallahi manyan mutane fa? Shi yasa kawai naso ta auri wannan kafurin yaron ya zama mijin malama tunda kaga ana zaton ma bashi da Iyaye shi ma shege ne gantali kawai yake, gashi burina bai samu cika ba, kace mini wata tayi mini shigar sauri ko?" Turzum dai kallonta kawai yake babu ƙiftawa ta ce "Wallahi wulaƙantacce miji naso Majeederh ta aura wanda zai dunga cin Ubanta yana gallazawa rayuwarta, amma idan babu damuwa shi kansa His Excellency Abu-turab ɗin kawai a saka masa hannu a arziƙin shi, komai ya saka hannu ya lalace yadda E.F.C C zasu garƙame shi a gidan yari" Turzum ya ce "Zan yi tunani sai na kammala wannan aikin, ki je sai ki dawo kuma kada ki matsanta akan sanin waye MIJIN MALAMA na har abada, kada ki matsanta kada ki matsanta kinji na faɗa miki baƙar muguwa" Latifa ta jinjina kanta ta ce "Shi kenan Turzum bari na je" Ta miƙe tana ajjiye masa ƙyallen wanda yake ta zuba wari ta shiga fita daga ƴar bukkar tana kaɗa masa mazaunai, Turzum ya bita da idanu yana dry. After Issha prayer, around eight and forty minutes, Majeederh ce durƙoshe gaban matan wan mahaifinta da Uncle's ɗin sai Innati da Yaya Bilkisu, faɗa suke mata sosai Uncle Isma'il ya ce "Duk abin da zan faɗa alrdy an faɗa miki, Majeederh idan aka ce aure to ana nufin haƙuri, haƙurin gidan miji yafi daɗin yawa, kina da hankali shekaru 35 ya isa ki fahimci rayuwa, ki kwantar da hankalinki kima mijinki biyayya da ƴan uwansa da uwar mijinki, Majeederh yadda Ubangiji ya rufa mana asiri kika samu miji kamar Abuturab kada ki bamu kunya plx, kiyi zamanki lafiya, ki yi haƙuri, ki yi haƙuri, ki yi haƙuri aure haƙuri ne, ka auri mai kuɗi ka yi haƙuri, ka auri talaka ka yi haƙuri shi ne" ɗaya bayan ɗaya suka shiga yi mata faɗa kusan kowa zai ce mata ta yi haƙuri, aure ɗan haƙuri ne. Ita dai kanta na ƙasa ta saka wani tsadadden lace black colour da feshin dutsun jaa ya zauna daram a fatar jikinta ya ƙara fidda haskenta ainun a fili. Sai wani vail babba white colour data ɗora akanta wanda Sona ta ɗaura mata ta fito a babbar mace idanunta ne kawai ya faɗa amma haihuwar da tayi ya sanya jikinta buɗewa irin na masu ɗanyen jego. Suna zaune Jawaad ya shigo yana ɗan murmushi ya ce "Finally he's here" Gaban Majeederh ya faɗi ta ƙara sunkuyar da kanta ƙasa, Uncle Bello ya ce "To ya kai ɗaya?" Ya ce "Oh! Ya ce ba zai shigo ba, maybe kunyar surukan shi yake" Maman Alpha ta yi murmushi tana kallon Jawaad matsayin Alpha har yanayinsu ɗaya da ɗaga shoulder's da suke. "To ai babu damuwa, ku bata ɗanta sai su shige" Da sauri Yaya Bilkisu ta ce "Wani ɗan ni ƴar nan? Kawai sai ta tafi gidan miji da ɗan mutane kuma jariri? Ai nan zamu riƙe shi in sha Allah taje kawai Allah ya bata sa a" Da sauri Majeederh ta ce "Plx zan je da shi" Yaya Bilkisu ta riƙe haɓa ta ce "Naga abinda ya Isheni ni Bilkisu, gidanku Hawwa'u ashe baki da kara? Ai kamata ya yi ki tsani ɗan kamar yadda kika tsani ubansa" Ita dai ta yi shiru, anyi ba ai ba, taya zatai farin ciki babu baby Khalil wajanta? Idanun yaron kawai idan ta kalla nutsuwa take samu. "Gaskiya ban goyi bayan ta tafi da shi ba ni ma, ni zan riƙe shi In sha Allah daman ba nono yake sha ba madara ce idan ya yi kamar shekara ɗaya sai a kawo miki shi, kafin nan za a dinga kawo shi kina gani"