← Book details Mijin Malama Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 90

Sashe 26

Mijin Malama Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Juya peper ɗin kawai take a hannunta tana ƙara bin bedroom ɗin da kallo, a hankali ta buɗe saƙon ciki Alpha's mother is looking at the paper with a kind of nervousness and anxiety, zufa ta shiga yanko mata a dukkan jikinta ta ware idanunta sosai akan handwritten ɗin Khalil idanunta ya sauka akan short note ɗin tayi baya zata faɗi sai kuma ta zauna tana dafe kanta a fili ta shiga karantawa; _We didn't run away forever, one day we will come back to you with a blessed offspring, idan na faɗawa waye babana you couldn't believe me, ba zaku yarda ba, kun hanani matana, shi kuma yana son rabani da ita? What do you want me to do? Wanda kuke buƙatar gani zai zo, ba zamu dawo sai sanda kuka neme mu, my wife is with me zan kula da ita_ Ya yi sign da sunan shi, rubutun kuma wani Hausa wani turanci ba zai iya magana da complete na sentence ɗin Hausa ba, duk yana iya ƙoƙarin shi wajan ganin ya iya, shi ne dalilin daya sanya yake zama cikin jama'a a ɗan yi magana da shi yanzu. Maman Alpha kasa motsi tayi, tasan tana nemawa Khalil mafita but not this way, bata wannan hanyar ba, kallon paper ɗin kawai take with shock ta kasa tashi, a hankali ta miƙe ta nufi bathroom ta kashe shower ɗin dake zuba sosai, ta leƙa window taga ring ya faɗi ta dinga kallon ring ɗin babu ƙiftawar idanu, ina ta taɓa ganin irinsa? Sai ta juya ta nufi parlour, Tunda ta fita zuwa main parlour Uncle Bello ke kallonta ganin yanayinta duk a zabure take duk da dauriya irin ta Barrister. "Lafiya?" Mijin nata ya tambaya ta miƙa masa paper ɗin ya amsa yana gama karantawa ya ɗaga kai ya kalli Uncle Isma'il dake kallon su ya ce "Meye kuke ta zare ido? Ina shi Khalil ɗin?" A hankali Uncle Bello ya ce "He ran away with her, he was already gone, Ya gudu da ita" Da wani irin sabon tashin hankali Uncle Isma'il ya buɗe idanu ya ce "Waye? Dawa aka gudu meye kuma wani Ran away?" Uncle Bello ya ce "Kalmar turanci ce Yaya, Mijin Malama ya tafi da matarsa" Uncle Isma'il ya ce "Daman akwai wata Ran away kalman turanci" Ya faɗa fuskarsa cike da tashin hankali domin da gaske sam bai fahimta, Uncle Bello kallonsa kawai yake kafin ya ce "Eh, ai past tense na Run ne, we can check by yourself Yaya, amma dai Mijin Malama ya tafi da Malamar shi" Uncle Isma'il ya miƙe tsaye yana zaga parlourn ya kasa fahimtar komai sbd tashin hankali ya ce "To ya akai hakan ta kasance?" Maman Alpha ta ce "I didn't realize they weren't in the house until now, na shiga naji shower na ɗauka wanka take ina ƙoƙarin fita naga peper, ina da tabbacin ta window ya ɗauketa suka fice daga cikin gidan" muryarta a sanyaye domin ta girgiza da al'amarin Khalil, Uncle Isma'il ya ce "Bari na bisu" Yaya Bilkisu ta ce "Where? They're already left, kuma ina da tabbacin ba a Kano zai tsaya ba ƙasar zai bari" Uncle Isma'il ya ce "Ƙasar? Da wanne kuɗin zai tafi? Yaushe ya samu National ID card ɗinta? Ko ana barin country ba shi?" Yaya Bilkisu ta ce "To bana ce ba, batun ka tambaya da wanne kuɗin bai tashi ba ko kaɗan, kasan kakansa pasto ne kuma baka san kalar arziƙin shi ba" Cikin ɓacin rai ya ce "Nabi pasto da gudu ba wando" Yaya Bilkisu ta ce "A'a gwara kasa dai Isma'ila" Ya yi ƙwafa yana kallon Uncle Bello da matarsa ta ce "Daman nasan za a rina an saci zanin mahaukaciya, barewa tayi gudu ɗanta ya kasa rarrafe? Ai tunda Majeederh ta dawo gidan nan nasan zai biyota ai taurin kai ne dashi baya da zuciya akanta, kuna can kun saki baki da ƙyar idan bai hakke mata ba" Nan ma Yaya Bilkisu ta ce "Da sauƙi ai tunda kafi kowa sanin matarsa ce" Uncle B kowa gyara zama ya yi sosai ya ce "Ni dai ba zan ga abin kunyar nan a gidana ba" Uncle Isma'il ya juya ya kalli Maman Alpha ya ce "You're the reason behind all this Barrister, ni ban yarda dake ba kece kika bashi opportunity na ɗauketa shi yasa kika shirya dawowarta gidanki, kin muna furuci mijinki dani kai na kuma kinci amanar yarda da kuma zumuncin Allah" Za tayi magana Uncle Bello ya girgiza mata kai, Yaya Bilkisu ta ce "Sai ihu kake da kumfar baki kamar mijin bazawara, ai tunani zakai ina za'a same su, domin daya tafi da ita gwara an tarkata an bashi matarsa wlh" Bai ƙara magana ba ya ɗauki key ɗin motar ya yi waje hankali tashe. Yaya Bilkisu ta juya kan Maman Alpha ta ce "Kuma da gaske baki san inda suke ba?" Maman Alpha da idanunta sukai jajur damuwa ta mata yawa, tana jin zafi da raɗaɗi a zuciyarta ta ja wani numfashi mai wahala ta ce "Haba Yaya Bilkisu, taya kike tunani zan bashi damar tafiya da ita? Wlh i knw nothing akan wannan abin, Majeederh is like a daughter to me ba zan su abinda zai sanyata cikin wahala ba, idan na cutar da ita ɗana da ya yi shekara da shekaru baya nan ban san ina yake ba ban san kuma zai cutar dashi ba" Sai kuma ta fashe da matsanancin kuka ta ce "Yana raye baya raye babu wanda ya sani,kamar an danni bakin jama'a babu wanda ya damu daya tofa tashi akai even his family haka wajan aikinsa" Kuka take sosai wanda daman ya jima yana cin ranta, tsakanin Yaya Bilkisu da Uncle Bello aka rasa me yin magana. Suna zaune Jawaad ya shigo da Baby Khalil dake ta kuka Maman Alpha ta miƙe ta amshe shi tana jin temperature ɗinsa na sake high. "Ga result ɗin da akai masa, sun ce bayan wata uku a koma but suna zargin ko Sikila ce dashi babu tabbaci dai" Da wani Expression take Kallonsa ta ce "Sikila wacce iri ni ƴar nan? Genotype na Majeederh AA ne, haka kuma Khalil AA ne, ina tunanin ba zasu taɓa samun sikila a zuri'ar su ba" Jawaad ya ce "Haka dai Dr ya ce" Ta kalli Baby Khalil yaron gwanin sha'awa amma 2days duk ya rame kasa magana tayi ta nufi bedroom tana goya shi a bayanta. A hankali yake kai komo cikin katafaren ɗakin, babu wanda zai iya fahimtar yanayin da zuciyarsa ke ciki da yadda al'amarin ya riske shi, gently ya juya idanunsa ya sauka akan Joshua daya sha wani mahaukacin duka kamar bugun lugudan shekararriyyar dawa duk an saɓa masa kamanni "Oh tunda ba zaka faɗa ba, kuje ku harbe shi" Jikin Joshua na rawa ya ce "I am sorry sir, zan faɗa" Yana hakki ya ce "Yes Abraham called me, kan nazo na ɗauke shi so daman ina hanyar gidan da yake ina zuwa ya fito tare da matarsa wacce hankalinta yake a tashe domin kamar ma dole ya yi mata, bata da wani option kuma, daga nan nace ina zashi bayan nayi dropped nasa a airport ya ce Saudiyya" Kallon bakinsa kawai Dad keyi yana fahimtar maganganunsa ya fahimci gaskiya yake faɗa wani daga cikin mutanen wajan ya ce "Kana ganin jirgin su zai iya tashi yanzu?" Ya girgiza kai ya ce "I don't think so sbd whether akwai damina ga hadari, amma naji ance ba zai shige 30 minutes ba" Calmly Dad ya ce "Daga matar har shi ku kawo mini su nan do so immediately" Gabaɗaya suka fice wasu manyan motoci suka shiga daga dakarun Jamani har na Nigeria kuma Kano suka nufi airport da wani irin azababben gudu. Basu ɗauki lokaci ba suka ƙarasa airport ɗin sbd hanya motoci suka dinga basu musamman anga jami'an da ba'a taɓa gani ba, kamar wanda ake shirin data ɗan ƙaramin yaƙi, da gudu wani soja ya ce "Hi wanne jirgi zai tashi in few minutes?" Jami'in wajen ya ce "who are you?" Ya zaro masa id card jiki na rawa ya ce "Jirage biyu muke dasu, akwai na Saudiyya akwai na Qatar wanda zai fara sauka a Lagos kafin ya shige, kuma duk a shirye suke da tashi yanzu" Baki na rawa ya ƙarasar maganar ya ce "Ka sanarwa da pilto ɗin Saudiyya ya fasa tashi yanzu we're coming muna neman wani dake shirin guduwa" Yana faɗin hakan ya juya gabaɗaya suka nufi cikin inda jirage suke, da ga kuma can inda ake ajjiye passengers zuwa wajan inda ake control na jirage jami'an airport ɗin ne birjik cikin bada umarnin gaggawa suke cewa "033 Pilto Khabir an fasa ka sauke niyya an fasa ka sauke niyya" Kai tsaye maganar tashi har cikin jirgin take zuwa. Daga can wajan dakarun kai tsaye motocin suka shige cikin airport nan suka hango jirage biyu na yawo ɗaya ma har har ya fara ƙoƙarin tashi ɗayan kuma yana ta juya, suka ƙarawa motocinsu gudu. Majeederh dake zaune kusa da Khalil ta ware idanunta hankali tashe take hango motoci kamar me ta cikin jirgin ta juya ta kalli Khalil wanda shi kuma idanunsa a rufe suke ya riƙe hannunta cikin nashi, tana jin yadda hannunsa ke kakkarwa bai taɓa tunani halin Dad ɗin nasa har ya kai haka ba, cikin nutsuwa kuma jirginsu ya lula sama ta yi saurin rufe Idanu jikinta na rawa bawai tsoran jirgin take ba, shi just scared of everything ya jawota ya rungumeta sosai a ƙirjinsa take masifaffen harabawa. Da sauri wani soja ya fito daga cikin jirgin da zai tashi zuwa Saudiya wanda aka hana tashi ya girgiza kai ya ce "Ya raina mana hankali, baya ciki" Ya juya ya kalli jirgin Qatar wanda ya tashi sama kuma babu yadda za'ayi ya sakko tunda har ya fara nisa ya ce "Even his friend Khalil bai yarda da su ba, yama abokinsa ƙarya kuma daman ya yi tunanin za'a biyo shi ashe Qatar za shi ba Saudiyya ba" Suna nan tsaye sun rasa abin yi har jirgin ya shige cikin gajimare. Wata ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya Khalil ya sauke lokacin da jirgin ya gama daidaituwa a sama ya ƙara ƙanƙame Majeederh a jikinsa fuskarsa a
Chapter 26 · 0% Book details