← Book details Mijin Malama Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 90

Sashe 29

Mijin Malama Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

President Denial David na zaune saman wata ƙatuwar kujera sanye da wata tsadaddiyyar suit expensive one,Macron's suit. Hannunsa ɗaya riƙe da wani small pen yana jujjuyawa baya cewa komai sai idanunsa da sukai jajur a hankali kuma yake sauraran reporters ɗin nasa da yake cewa "Mrs President sir, mun samu ya zare millions daga cikin bank ɗin shi kafin akai ga blocked bank ɗin, bayan mun yi bincike da manager na bank ɗin mun samu nasarar gano daga inda akai transfer ɗin" Dad ya ware idanunsa bai ce komai ba, Chancellor da zuwan shi ƙasar kenan ya sauka a nan Bristol Palace Hotel ɗin ya ce "Yana ina?" Ya ce "Qatar" Dad da kuma first lady Kiristi suka kalli juna for some seconds, shi kam rabonsa da Qatar ai ya ɗauki shekaru haka ko matsala ne shugaban ƙasar Qatar ɗin ke zuwa har Germany sai da wani dalili mai ƙarfi yasa ya ɗauki Kiristi suka tafi Qatar ɗin tare da yin 2weeks. Calmly kamar bai tsoron magana ya ce "Kuma ina ya samu kuɗin zuwa Qatar with his wife?" Ya ɗan yi jim sai ya ce "US$1,010 fa each person?" Ɗaya daga cikin reporters ɗin ya ce "I am very sorry for that Sir, but duk inda kake tunanin kuɗin Abraham ya shige nan, idan bai fika ba to ba lallai ka fisa ba" A hankali Dad ya miƙe tsaye yana ɗan kai wa da kawowa a nutse ya duba agogon wrist ɗin hannunsa can ya nisa ya ce "Can you speak English in Qatar??" Tunda da ya je da mutum ɗaya kawai ya gana kuma yaga Arabic shi ne abin da ya fi ƙarfi a nahiyar Chancellor ya ce "English is widely spoken" Dad bai ce komai ba ya nufi cikin bedroom Kiristi tabi bayansa da wani guntun wandon jikinta tana zuwa ta same shi tsaye yana danna wayar sirrin shi yana ganinta ya tsaya ba tare da ya ce komai ba, za tayi magana ya nuna mata ƙofa da sauri ta fice, duk wasu Digits ɗin Khalil na ko wacce ƙasa yana da su luckly kiran ya shiga wajan kira uku ba a ɗagawa can aka ɗaga maimakon ya ji hello ko hi sai ya ji kwantacciyar muryar ɗan nashi wacce ta rage hayaniya an yi sallama da alamun bacci a cikinta. "You, duk ina kake ka dawo nan da 12hrs or else i should come and brake your legs, kazo ka mini explanation ina ka samu kuɗi har kke shirin zama millionaire ka shiga jerin masu kuɗi na Africa, kuɗina kke sata ko? You're a criminal Mr young man" Yadda yake huci zaka san Khalil amsa yake bashi daidai da maganar shi Dad ya ce "Hold on! Nafa san inda kake kawai I'm not interested na zuwa inda kake understood? Kana Qatar a Doha, ko ban zo ba zan saka a kawo mini matarka ta dole kaga ya zama dole ka dawo" Ta cikin wayar ƙarfin sautin muryar Khalil ke fitowa yana cewa "What? My wife at that time zaka san a zafin zuciyarka dana ɗauka baka taɓa ganin ko kaɗan ba, Qatar ta sha bamban da ƙasar ka Mrs President, zan ce ban saka ba kuma daman ban haɗa komai da kai ba, duk duniya ba wanda ya san kana da ɗa sai Zizi da Badi kaje kayi rayuwa da su mana eh?? Who stopped you from doing what you want to do? Who? Eh" Dad duk ya gama kaiwa ƙarshe ya ce "No one's, ba wanda yake da ƙarfin ikon haka, domin kai na je Nigeria zan kuma je har gidan surukan naka na shaida musu su gaggauta karɓe ƴar su domin baka da cikakken hankali tunda har kana iya sa'insa da mahaifinka" Ƙitt ya ji Khalil ya kashe wayar ya fahimci komai na Majeederh shi ne raunin Khalil ɗin. Majeederh na kwance tana bacci sbd daɗin jikinta da taji da kuma tausar da Khalil ya yi mata, sama sama take jiyo ƙarar fashewar abu daga parlour ta buɗe idanu da ƙyar ta duba taga bedroom ɗin duhu ta gane shi ne baya son haske gabaɗaya a bedroom ɗin nasa, ta miƙe da ƙyar ƙafarta babu ko takalmi sbd gabaɗaya na gidan wasu irin grace carpet ne masu kyau walking slowly daga jikin bango har zuwa parlour wanda yake ɗauke da haske daidai idanun kowa tayi tsaye tana kallon ikon Allah ganin ya fashe komai na parlourn duk ya farfasa jikinsa kuma sai rawa da ƙyarma yake hakan da yake ta gane wani ya ɓata masa rai, wanin da ba zai iya ɗaukan matakin komai akansa ba, Majeederh ta jingina da jikin bango Khalil a jikinsa ya ji tana kallonsa da sauri ya bar wajan ya shige wani gun not too long ya dawo tunda ya shigo yake binta da kallo ganin hakan yasa ta kalli jikinta ta runtse Idanunta ta mance wani ɗan wando ne daya saka mata iya laps ɗinta cinyoyinta sai ƴar riga kamar Half-vest ta dinga mmkin inda ya samu shegun kayan wanda ya siyo su duk rabi haka, da taga bills sai data tsorata, kayan baby peach ne dugun gashinta duk a baje har bayanta wani gefe sai ta koma kamar ba ƴar asalin Nigeria ba kuma haihuwar Kano, tayi zaton ta cikin Glasses ɗin zai biyo sai taga tsalle ɗaya ya diro ta gefen kujerar yana binta da wani ɗan banzan kallo wanda kai tsaye ta gane ma'anar shi, jikinta ya ɗauki rawa ta juya zata bar wajan ƙafarta ya riƙe daman ciwo yake mata a nutse ta ji ya ce "Uhm" wato ɓacin ransa har ya kai ya kasa cewa komai ta tsaya sbd ita a yanzu komai nasa tsoro yake bata gashi yanzu yana abu kamar wanda ya samu matsala ita kam yaushe zai daina wannan baƙar zuciyar? Ya tsaya gabanta sai kuma ya leƙa fuskarta suka haɗa idanu ta marairaice ta ce "Kayi haƙuri karka taɓa ni plx" Ya ware idanu bai ce komai ba jin shiru ta ɗaga kai ta kalle shi suna haɗa idanu ya marairaice mata fuska yana langwaɓar da kai har lokacin bai ce komai ba Silently ta ji ya ce "Damn it" Yana hargitsa sumarsa sai kuma ya zauna saman kujera ya ce "Come" sai kuma ya miƙe kamar zai shige ya sunkuceta zuwa bayan Glasses ɗin gidan wanda ruwa ke kwance ga laimar iska, ta riƙe wuyansa tana rufe ido tafiya yake Magesticaly a wani waje kamar bench dake balcony na gidan ya zauna saman kujera yana danna wani abu ta kwanta amma nrml a zaune suke tana kan cinyoyinsa ta kwantar da kai a ƙirjinsa wacce ta cire armless ɗin sai gargasar ƙirjinsa dake ta ƙamshi hannuna ɗaya a saman chest ɗin nashi ya yi shiru hannunsa guda na shafa kwantaccen cikin nata zuwa cinyoyinta da suke saman nashi a hankali ya ce "Hawwa'u" Gabanta ya faɗi jin sunanta raɗau a bakinsa bama Majeederh ba, ya ɗan matse mararta ta runtse idanu ta ce "Na'am" ya ɗauke hannunsa tare da miƙewa sosai ya ɗauketa ya juyo da ita gabansa yana tallafo fuskarta clamly ya ce "Da gaske baki son auren?" Tayi shiru ya leƙa fuskarta yaga ta kifata a ƙirjinsa ta riƙe hannunsa sosai cikin nasa ya ce "Sorry, akwai snow" Ya jawo plate ɗin abinci dake ɗauke da Majboos ya saka spoon ya ɗora a cinyarta yana ɗauka yakai bakinsa to cfrm ko babu zafi yaji daidai ya cinye ya ƙara ɗauka ya kai bakinta a hankali ta buɗe ta amsa sbd yunwa take ji sosai ba wanda ya sake magana daga ita har shi kowa tunani yake a ransa ita tana tunanin yadda zata iya yi masa biyya da Kallonsa matsayin miji shi kuma yana tunanin zai koma Naija ya auri Debeka ko hakan zai dawo da Majeederh cikin hayyacinta. Bayan sun kammala taji ya fara zagaye lip's ɗinta da hannunsa a duk sanda yaso yin kiss ɗinta daman haka yake farawa ya ce "Zamu ko ma Naija kiyi tunani, a tunaninki kina iya zaɓar rabuwa amma ni Mijin Malama bani zan bada divorce paper ba, idan kina so na ki faɗa mini tun wuri muyi fighting tare" a karo na farko ta ɗaga kai ta kalli idanunsa shi ma ya kalleta without blinking they're eyes irin kallo na so da ƙauna ko wanne yake ma juna har wani hawaye yake kwanciya cikin idanunta na irin idan ta kai maƙura a son abu ɗin nan Khalil ya ƙanƙameta a ƙirjinsa ya ce "Thanks Wife" Ya faɗa yana kissing goshinta da wuyanta ya ƙara cewa "No one can separate us, actually no one... U most be mine forever wife" jin yana taɓa ƙafarta tayi saurin riƙe hannunsa cikin sabuwar muryarta ta ce "ban warke ba" ya saka hannu ya dungure mata kai ya ce "bari na duba" Majeederh ta rufe Idanunta tasan bata isa ta hana shi ba tunda har ya yi niyya a zuciyarta kuma tana jin Khalil yafi ƙarfinta ko dan haka dole ta lallaɓa shi suna komawa Naija su rabu. Ta riƙe shoulder's ɗin shi ta ce "Plz Yaa K...." Kafin ta ƙarasa maganar taji saukar bakinsa a wajan...

_After spending four to three days in the hospital, I was discharged today.Allhamdulillah! Masu kiran waya, Dm, masu zuwa asibiti. I am very grateful Sarauta na yabawa da so da ƙauna🤓👐🏼Masu jiran MIJIN MALAMA da M.M B1💋da M.M B2 da Arewabooks, da Ƴan Bati siddan duk Sannunku ya zaman jira da damuna Allah ya bamu mai albarka🫣In sha Allah zamu dawo update ba kama hannun yaro muna can dai Qatar a nan Allah ya nufa Khalil ya angon ce da Maminsa don Allah duk wanda sukai new payment su yi mini magana immediately ba zance nafi kowa yawan messages ba, amma ni kaɗai nasan un-read messages d nke da su_

Masu Arewabooks su daure suyi following Acct ɗina😎👐🏼
MIJIN MALAMA na kuɗi a daure a biya a sauke hakƙin ko dan wahalar typing da nake cikin jinya Plz, kuga babu daraja sam ka dinga yekuwa dan ana karanta littafinka as free an san soyayya ne, littafai nawa ake na kuɗi amma sai naka ake bi? Ake fitarwa? Wasu ma ba a san da su ba? 08119237616
Chapter 29 · 0% Book details