← Book details Mijin Malama Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 39 OF 90

Sashe 39

Mijin Malama Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

da yawa suna masa yawo aka silently ya ce "Come here" Ta miƙe ta ƙarasa kusa da shi saman kujera ya kama hannunta ya ce "Meke faruwa? Do you like him?" Ta kasa cewa komai ya saka hannunsa tare da ɗago fuskarta ya kalleta tayi saurin ɗauke nata idanun kamar wanda akai forcing nashi na yi mata magana ya ce "Ya akai?" Ya furta yana ɗan riƙe ƙansa da son daidaita nasa nutsuwar ta kasa cewa komai sai ta fashe da kuka tana ɗora kansa akan ƙafafuwansa, kuka take da dukkan ƙarfinta wanda yake tasuwa tun daga ƙasan zuciyarta, kuka ne wanda ta jima bata samu zarafin yinsa ba, Abbu ya runtse idanunsa a hankali cikin sanyi kukan nata yake shiga yana ratsa ko'ina na zuciyarsa, gabaɗaya ƙofofin gargasar jikinsa suka bubbuɗe yana amsar kukan nata cikin yanayin da ba zai iya fahimtar shi ko gane shi ba, muryarta na rawa ta ce "He is the one who destroyed my life, without my consent or approval, ba tare da yarda ko amincewata ba su Uncle suka ɗaura mini aure da shi, Abbu Khalil baya ji zuciya gare shi baya iya bakinsa da sarrafa kansa, na girme shi ba zan iya zama da shi ba, ba zan iya yi masa biyayya ba" Abbu was speechless, shi kansa zuciyarsa gudu take, ya saka hannu ya ɗagota bakiɗaya fuskarta cikin hannunsa ya ce "Ba wannan nake son ji ba" Ya lumshe idanunsa ya buɗe shortly ya ce "Do you love him?" Majeederh tayi shiru a hankali kuma ta girgiza kanta alamar “A'a” Abbu ya ɗora kanta a shoulder ɗinsa yana sauke wata ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya mai ƙarfi wacce take daga ƙasan zuciyarsa ta kuma jima shekara da shekaru. A hankali ya ce "I am sorry, I'm sorry Hawwa'u"...... Parlourn ya yi shiru bayan zuwan President Denial David, Dad ya kalli Majeederh dake gabansa ya ce "Ba zan raba muku aure ba, idan ya amince da auren ƴar uwar ta shi" Ya yi shiru can ya ce "Idan kuma yaƙi shi ma zai ɗan-ɗana zafin rashin masoyi, don sai raba auren" A hankali Majeederh ta ce "I am sorry Dad, na amince ya auri Debeka ni kuma ya sakeni" Chancellor dake zaune ya ce "For what reason?" Kanta a ƙasa ta ce "I don't love him anymore" Gabaɗaya Mutanen wajan suka kalli Majeederh da mamaki cikin sauri Yaya Bilkisu ta ce "You're Liar, ƙarya kike kina son mijinki" Majeederh ta girgiza kai ta ce "Tun farko kun san bana son shi" Zata sake magana Dad ya ɗaga mata hannu ya kalli Khalil da Majeederh kawai yake kallo without blinking his eyes ya ce "Yanzu zaka rubuta sakin ko ya?" Khalil ya miƙe tsaye ya ce "Burinka ya cika? Wannan shi ne Abin da kake so ko?" Dad ce "Her divorce paper, write it immediately" Khalil ya girgiza kai yana kallon Majeederh domin tafi bashi mamaki ya ce "To bari kiji na faɗa miki sai dai mu mutu haka nan, amma ba zan taɓa rubutu tsinanniyar abar da kike muradi ba" Dad ya miƙe tsaye ya zabgawa Khalil mari ya ce "Her divorce papers, ka rubuta do so immediately" Khalil ya kalli Dad ɗin nasa ya ce "I can't write it, Dad please tell me are you real father?" Abbu dai na zaune watching all of them tunaninsa ya bambanta da nasu, zuciyarsa ta kaɗai ta da wajan gabaɗaya, Uncle Isma'il ya ce "Mr President sir ina tunanin wannan ba hanya bace ta nemi mafita, Ibrahim zai auri Debeka, kuma zai zauna da matarsa Majeederh" Dad ya numfasa ya ce "Baka ji ba da bakinta bata son shi, daman yake kukewa yaranku Forced married?" Ya girgiza kai cike da takaicin zuciyar Khalil ya ce "Yarinyar ku mai kyau, hankali ilimi, sam ba tayi deserving auren yaro irinsa ba na faɗa muku" Uncle Isma'il ya ce "Karka damu da hakan, mun san halinsa mun zauna da shi kuma ko zaiwa kowa banda ita" Dad ya miƙe tsaye Chancellor ma haka kana ya kalli Majeederh ya ce "Daughter jeki waje wajan Zizi ki jirani" Majeederh ta miƙe tsaye ta juya ta kalli Abbu taga ita yake kallo ta nufi waje da sauri hannunta riƙe da waya da hand bag, Khalil ya bi bayanta hakan yasa Dad gyara zaman bluetooth na kunnen shi ya yi magana, ya kalli Uncle Isma'il ya ce "A bani a ron daughter in-law, gobe idan an ɗaura auren su a church ina nufin shi da Debeka ita kuma zata dawo ku shiryata zuwa Germany" Yana faɗin hakan ya fice daga ciki, tun a entrance ya hango yadda ake zuba dambe da Khalil sun riƙe shi da ƙarfi, shi kuma yana ƙoƙarin kwancewa ya ƙarasa wajan Majeederh, Gabaɗaya ya yi wa Escorts ɗin duka ya karya hannun wasu wani ya fasa masa baki, Dad ya ce Majeederh ta shiga mota akan idanunsa suka fice daga gidan kana Escorts ɗin suka sake shi ya bi motar da kallo, zuciyarsa a sunkushe bai taɓa jin zafin Majeederh ba irin na yau, tana son dawo masa da halin daya manta da dainawa, idanunsa har wani ruwa ke kwanciya a cikin su, burinsa a yanzu ya yi Idanu biyu da barasa.... Har dare ya yi Majeederh ta kasa samun sukuni a ranta, haka kurum ta tsani harafin D ta dinga juyi akan gado, ita kanta a wannan lokacin burinta ta samu maganin da His Excellency Abu-turab yake mata take yin bacci, ta kuma kasa gano wani magani ne, ta kasa rabuwa da shi yana nan zaune a ranta, a hankali ta jawo jakarta da nufin kiran Latifa sai ga Envelope ya faɗo, gabaɗaya ta mance da ita cikin sauri ta ɗauka tare da buɗewa abinda ta fara gani shi ne.... _“No words to explain, no words to describe; no words to ask your forgiveness, Wait for me I'll be back sooner or later! Please Jee”_ Sune rubutun da idanunta ya fara cin karo da shi, ta juya bayan paper ɗin taga an saka BAD MAN, _THE STUBBORN BOY, CRIMINAL, GANG BOY, THE LEADER_ Cikin sauri ta shiga karantawa, kafin ta ƙarasa kuka take kamar ranta hadda majina jikinta rawa yake da ɓari yana wata iriyar ƙyarma,wani irin zazzafan zazzaɓi ya nemi rufeta bata iya ƙarasawa ba ta ɗauki hijabi ta saka, a hankali ta fita daga cikin bedroom ɗin gidan da suke tana fita waje wani soja ya sara mata cikin dauriya ta ce "Key car Plx?" Ya ce "Madam zaki fita ne?" Ta zuba masa Idanu ya ce "I'll drive you" ta ce "No Thank you" Ya bata key ta amsa tana shiga motar ta jata da wani irin sauri tana tafe tana kiran number Khalil but a kashe, kuka take cikin damuwa ta ce "I am sorry, i know nothing about that" Har gidansa taje amma ba alamar mutane, wannan gidan kawai ta sani, tana da tabbacin ba zai je gidan Uncle's ba, sbd ya yi zuciya daman bai damu da zama gidan Abbu ba “Lebanon Club” Shi ne ya faɗo mata a rai, tabbas ta taɓa jin Taj ya faɗa, daga inda take a yanzu 22ms 10km ne zai kaita Fagge due to the traffic conditions duk da dare ne, magana ake ta wajan 12 na dare, gudu kawai take akan titi without knowing yama take driving ɗin a haka ta shige Bampai Rd, ta shige Zaria Ave ta zo Miller Rd daidai by pass na firstmonie agent on the left ta samu traffic, ji take kamar ta tashi sama deep down na zuciyarta kuma addu'a take Allah yasa yana wajan, don tasan baƙar zuciyarsa yanzu sai ya bar ƙasar idan har ya samu jirgi, motar ta ƙarawa gudu har ta iso fagge dake daga Miller Rd zuwa nan tafiyar 600m, ta dinga kallon Lebanon Club ɗin ganin kamar rana manyan motoci birjik a hankali tayi parking ta fito, har lokacin hannunta riƙe da envelope ɗin, ta shiga ciki wani ta gani sukai ɗan magana ya ce "I am sorry Maa, he's not around" jikinta ya yi sanyi ta juya zata bar wajan ta hango shi tsaye ya juyawa ruwan da yake gudana a wajan baya, hannunsa ɗaya riƙe da rigarsa ɗaya kuma ya riƙe wata ƙatuwar kwalba wacce ya kasa buɗeta, ya fashe gabaɗaya Glasses cup ɗin da aka kawo masa, gabanta ya faɗi badai giya ya sha ba? Jin tsaiwa a bayansa ya sanya ya juya a hankali sukai idanu biyu, taga idanuna kamar gauta don jaa yadda yake Kallonta a makake yana lumshe idanunsa ta ɗauka a cikin maye yake ta ɗaga masa envelope ɗin ta ce "Why?" Ya kalleta ya kalli envelope ɗin sai kawai ya sake juya baya, cikin sauri Majeederh ta ƙarasa inda yake tare da tsayawa a bayansa, a hankali ta zura hannayenta ta ƙasan nasa hannunsa ta ɗora tafin hannunta a ƙirjinsa dake a buɗe babu riga hannun ya sauka a kwantaccen sumar wajan, ta ɗora kanta a wuyansa cikin wani irin yanayi dake fisgarta yana shigarta ta bashi da ƙyakƙyawar runguma ta baya ta fashe da wani irin raunataccen kuka ta ce “I... I... Love You
Chapter 39 · 0% Book details