Sashe 57
Captain Sadiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A dai-dai affcent center motocin suka faka lokacin har wasu sun halara tun daga bakin hall din kana jiyo irin sautin dake tashi, wajen ya hadu ba karya, kallo daya zaka masa kasan naira tayi kuka wasu kujeru ne na alfarma a hall d'in wanda ko ba'a fada ba zaka gane hall din na d'an wane da wance ne, jerawa yan'matan amaran sukayi masu ashobe, haka suma abokan angwayan suka jera reras masha Allah shigar ta su yayi kyau, amaran suka shiga tsakiya da angwayan Sadiq sai bin fatuha yake da kallo bugun zuciyarsa na daduwa, ta masa wani irin kyau ita kanta fatuha ta qasan ido take kallon sadiq tana jin wani irin kishinsa dan ba qaramin kyau ya mata ba.
A natse suka shigo hall din, wajen ya gwarare da shewa da ihu, tuni aka canza salan kida da sauti majeed hannusa na maqale dana fatuha yadda ya shige mata kamar zai maida ta ciki, sadiq ya cika taf dan har ya fara jin kirjinsa na masa zafi duk sanyi AC dake ratsa hall baya ji sai zafi da yake ji zufa na karyo masa, kidin da aka saki sai ya qara dagula masa lusafi ya fara hanging jiri riqe hannu Basma yayi dan ba yadda zaiyi dan baya so ya bata ma qansa rai, ko bai so Basma so na aure ba yana sonta a matsayin ta na kanwar sa, sosai ya damke hannuta yana sauke numfashi a hankali dake neman kwace masa, ko da suka shiga gurin zama suka yi aka fara gudanar da shakali, can na hango su Aunty Rahenat anata kai kawo anzu shagali😜 ashe abin ba ita kadai ba ce har da yan Real Hausa fulani writers, can na hango Fulani da Aunty Rahama Nalele suna rabawa mutane kayan motsa baki, nima dai ba'a barni a baya ba dan na shiga a dama dani shoki kawai ake kwasowa.
A hankali majeed ya matso daf da kunan fatuha ya ce, "My love yanzu fa gobe kamar yanzu kin zama tawa ko? yana magana yana wasa da yan yatsunta Sadiq dake gefe yana kallon su bakin ciki na qara qumesa, dafe kirjinsa yayi domin yafara yi masa nauyi, zufa sai karyo masa take tamkar wanda ke bakin wuta a hankali ya miqe ya saci jiki ya bar guri tunda ya fito daga hall din jiri ke di barshi yana had'a hanya yana sauke wani irin numfashi mai baraza na da rayuwarsa, ko gabansa baya gani dakyar ya iya isa inda akayi parking motarsa ya daura hannusa kenan ya ji an riqe hannunsa, waigowa yayi su kayi 4 eye's da Dr yakub girgiza kai Dr yakub yayi ya ce, sa...!! bai furta abinda yayi niya ba ida sadiq ya fado jikisa sumame, rudewa Dr yakub yayi ya cewa, sadiq..! captain..! ka ga sadiq tashi ka ji kalle ni ka bud'e ido karka mana haka, ka gani ko abinda zurfin cikin ka zai ja mana karka barni aboki na ka ji captain.! kuka yakub yake sosai ya rude ya rasa abunyi daukar sadiq yayi cak yasa a mota ya bar harabar gurin da gudu..
Duk wannan bidirin da ake ba wanda yasan halin da sadiq ke ciki sai Dr yakub, MC ne ya fara cewa, "amarya da ango su fito su yanka cake ango ya ba amaryarsa itama ta basa" saukowa sukayi a hankali suka tsaya majeed ya yanka cake d'in yaba fatuha a baki itama ta basa hall din ya dau ihu, sadiq aka kira da Basma amma ba ango ba alama haka MC ya dinga kira ango ganin abin kunyar dake shirin faruwa yasa Khaleed hawa a matsayin ango yaba Basma cake a matsayin sadiq tuni hall ya dau tafi, Basma iyakar cika ta cika bata taba jin bacin rai ba irin na yau, yaune ta tabbatar da sadiq bai sonta kuma ba zai taba sonta ba tunda har ya iya wulaqantata gaban bainar jama'a, idanuwan ta taf da qwalla, tana tausayawa kantada irin rayuwar da zatayi a gidan Sadiq, haka akayi taro kusan duk abinda ango zaiyi ma amarya Khaleed ne yayi ma Basma.
Ko da fatuha ta juya bata ga sadiq ba tuni idanuwan ta suka kawo ruwa, dama shi take gani tana jin sanyi a ranta.
Ko da Dr yakub yaja mota basu zame ko ina ba sai asibitinsa, suna shiga aka turo gadon daukar marasa lafiya sadiq da yanzu idanuwansa sun fara budewa saboda oxygen d'in dake manne a hancinsa haka yake ganin asibitin na juya masa numfashinsa na sama-sama, Dr yakub kuwa kuka yake sosai, emergency aka wuce da shi doctorsa sun dade a kansa Dr yakub ma kasa shiga yayi sai zarya da yake a bakin kofar kusan 1 hour suka dauka sannan aka fito da sadiq manne da oxygen a hancinsa daki aka bashi tare da sa masa life sport machine sai qarin jini da ake masa, a hankali Dr yakub ya qaraso gaban gadon yayi kneeldown, hawaye ne ke masa zarya a hankali ya kai hannusa ya shafa sumar kan Sadiq ya ce, "Friend why me yasa kake bama kanka punishment haka? why sadiq.! ya ida zancan hawaye masu zafi na gangaro masa wayara ce dake ringing ciki aljihu ya curo tare da kallon suna dake maqale a screen din majeed, kashe wayar yayi gabaki daya tare da jawo wayar sadiq ya kashe sannan ya dau kayan sadiq da aka cire masa yaba daya daga cikin ma'aikatan asubitin su wanke.
Bayan ankamala dinner kowa ya dau hanyar zuwa masaukinsa majeed sai kiran layin sadiq yake, baya shiga dana Dr yakub, yana mamakin abun ya faru yau ya rasa mai ke damun sadiq hakura yayi da kiran tare da maida wayar aljihu.
Bangaran Basma ko kuka take sosai tare da taqaicin amincewa da auran sadiq, Khaleed sai bata hakuri yake tare da ganin rashin kyautawar sadiq ya rasa dalilin da zai mata irin wannan cin fuskar bayan tana qanwarsa kuma matar da zai aura, shi a ganinsa duk wanda ya samu Basma a matsayin mata ya mure, ya rasa me yasa sadiq ke nuna rashin ko in kulla a kanta, kuma majeed na gani ko ba komai yasan dole zai ji haushin sadiq da wannan tunanin suka qaraso gida ko Godiya bata masa ba ta shige gida da sauri tare da tsananta kukanta.
Motar su fatuha na fakawa majeed ya fara jero mata kalaman soyayya tare da jan ta jikinsa, ganin zai wuce gona da iri yasa fatuha sakin kuka, lallashin ta majeed ya shiga dan kukan fatu na d'aga masa hankali yayi mata peck, ko saurara shi ba tayi ba ta bale murfin motar ta fita da sauri.
Bangaran sadiq ko bashi ya tashi ba sai wajan 2:00am na dare a hankali yake ware sexy eye's ball's dinsa da wani irin ishin ruwa ya tashi, Dr yakub da ko rintsawa baiyi ba ya miqe da sauri ya qaraso wajan shi cikin cool voice sadiq ya ce, "Ruwa..! da sauri Dr yakub ya bude fridge ya dauko rubar ruwa ya bashi ko da ya sha ruwan miqewa yayi yana qoqarin cire jini da ake qara masa riqe hannusa Dr yakub yayi ya ce, "Captain me kake shirin aikatawa? ya fada bakin shi na rawa kallonsa Sadiq yayi ya ce, "so nake na tafi gida bana so majeed ya gane bani da lafiya, na san yanzu haka Basma name fushi dani, na ruguza mata farin cikinta saboda rashin hakuri na" ya ida zancan yana cire qarin jinin wasu hawaye ne masu zafi suka zubu ma Dr yakub ya ce, "Sadiq wai me yasa kake so ka raya rayuwar wani ka bata taka? why sadiq? Dr yakub ya fada yana jijiga sadiq kuka sadiq ya saki tare da cewa "ka dai kiran majeed da wani d'an uwa nane kuma na jini, bazan ta6a bari majeed ya mutu saboda bakin ciki na ba, nafi son farin cikin majeed a kan na kowa a duniya, bani da d'an uwa sama da majeed, kasan ko ya majeed ya ke waje na yana so na yana son farin cikina, tunda da nake da majeed bai ta6a nuna min abinda yake so ba kamar fatu ba, ina iya ce ma kan fatu majeed ya san me so saboda haka ban taba bari saboda ni ya rasa rayuwarsa..! sadiq ya ida zancan yana kuka mai tsuma zuciyar mai saurare a hankali ya ida cire kayan asibiti dake jikinsa yasa kayansa wayarsa ya dauka tare da kunna ta Dr yakub mutuwar tsaye yayi yana bin sadiq da kallo cikin bacin rai ya ce, "kai taka rayuwar yaya za'ayi da ita, kai taka zuciyar ayi yaya da ita? Sadiq ka fahimce ni kafi majeed buqatar fatu, kafi majeed son ta, ka duba halin da kake jefa kanka, ka falasa abinda ke ranka tun kafin gobe fatu ta zama malakin majeed..! tabbas yanzu yasan me sadiq yake nufi so yake ya rasa rayuwarsa ya zamar masa dole ya kawo karshan abunan ko saurarashi sadiq bai yi ba saima car key daya dauka tare da fita yana ingisawa.....
Vote
Comment
Written by
Salma mas'ud nadabo
Edit by
Raheenat
📘 REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄
★We are the best★
http/mobile.Facebook.com/Real-Hausa-fulani-writers-forum RHFWF-173984973194167/?refid=52red=opera_speed_dial_&yn=H-R
*Email* [email protected]
*Facebook* www.Facebook.com/REALHAUSAFULANIWRITERSFORUM.COM
91_92
A natse suka shigo hall din, wajen ya gwarare da shewa da ihu, tuni aka canza salan kida da sauti majeed hannusa na maqale dana fatuha yadda ya shige mata kamar zai maida ta ciki, sadiq ya cika taf dan har ya fara jin kirjinsa na masa zafi duk sanyi AC dake ratsa hall baya ji sai zafi da yake ji zufa na karyo masa, kidin da aka saki sai ya qara dagula masa lusafi ya fara hanging jiri riqe hannu Basma yayi dan ba yadda zaiyi dan baya so ya bata ma qansa rai, ko bai so Basma so na aure ba yana sonta a matsayin ta na kanwar sa, sosai ya damke hannuta yana sauke numfashi a hankali dake neman kwace masa, ko da suka shiga gurin zama suka yi aka fara gudanar da shakali, can na hango su Aunty Rahenat anata kai kawo anzu shagali😜 ashe abin ba ita kadai ba ce har da yan Real Hausa fulani writers, can na hango Fulani da Aunty Rahama Nalele suna rabawa mutane kayan motsa baki, nima dai ba'a barni a baya ba dan na shiga a dama dani shoki kawai ake kwasowa.
A hankali majeed ya matso daf da kunan fatuha ya ce, "My love yanzu fa gobe kamar yanzu kin zama tawa ko? yana magana yana wasa da yan yatsunta Sadiq dake gefe yana kallon su bakin ciki na qara qumesa, dafe kirjinsa yayi domin yafara yi masa nauyi, zufa sai karyo masa take tamkar wanda ke bakin wuta a hankali ya miqe ya saci jiki ya bar guri tunda ya fito daga hall din jiri ke di barshi yana had'a hanya yana sauke wani irin numfashi mai baraza na da rayuwarsa, ko gabansa baya gani dakyar ya iya isa inda akayi parking motarsa ya daura hannusa kenan ya ji an riqe hannunsa, waigowa yayi su kayi 4 eye's da Dr yakub girgiza kai Dr yakub yayi ya ce, sa...!! bai furta abinda yayi niya ba ida sadiq ya fado jikisa sumame, rudewa Dr yakub yayi ya cewa, sadiq..! captain..! ka ga sadiq tashi ka ji kalle ni ka bud'e ido karka mana haka, ka gani ko abinda zurfin cikin ka zai ja mana karka barni aboki na ka ji captain.! kuka yakub yake sosai ya rude ya rasa abunyi daukar sadiq yayi cak yasa a mota ya bar harabar gurin da gudu..
Duk wannan bidirin da ake ba wanda yasan halin da sadiq ke ciki sai Dr yakub, MC ne ya fara cewa, "amarya da ango su fito su yanka cake ango ya ba amaryarsa itama ta basa" saukowa sukayi a hankali suka tsaya majeed ya yanka cake d'in yaba fatuha a baki itama ta basa hall din ya dau ihu, sadiq aka kira da Basma amma ba ango ba alama haka MC ya dinga kira ango ganin abin kunyar dake shirin faruwa yasa Khaleed hawa a matsayin ango yaba Basma cake a matsayin sadiq tuni hall ya dau tafi, Basma iyakar cika ta cika bata taba jin bacin rai ba irin na yau, yaune ta tabbatar da sadiq bai sonta kuma ba zai taba sonta ba tunda har ya iya wulaqantata gaban bainar jama'a, idanuwan ta taf da qwalla, tana tausayawa kantada irin rayuwar da zatayi a gidan Sadiq, haka akayi taro kusan duk abinda ango zaiyi ma amarya Khaleed ne yayi ma Basma.
Ko da fatuha ta juya bata ga sadiq ba tuni idanuwan ta suka kawo ruwa, dama shi take gani tana jin sanyi a ranta.
Ko da Dr yakub yaja mota basu zame ko ina ba sai asibitinsa, suna shiga aka turo gadon daukar marasa lafiya sadiq da yanzu idanuwansa sun fara budewa saboda oxygen d'in dake manne a hancinsa haka yake ganin asibitin na juya masa numfashinsa na sama-sama, Dr yakub kuwa kuka yake sosai, emergency aka wuce da shi doctorsa sun dade a kansa Dr yakub ma kasa shiga yayi sai zarya da yake a bakin kofar kusan 1 hour suka dauka sannan aka fito da sadiq manne da oxygen a hancinsa daki aka bashi tare da sa masa life sport machine sai qarin jini da ake masa, a hankali Dr yakub ya qaraso gaban gadon yayi kneeldown, hawaye ne ke masa zarya a hankali ya kai hannusa ya shafa sumar kan Sadiq ya ce, "Friend why me yasa kake bama kanka punishment haka? why sadiq.! ya ida zancan hawaye masu zafi na gangaro masa wayara ce dake ringing ciki aljihu ya curo tare da kallon suna dake maqale a screen din majeed, kashe wayar yayi gabaki daya tare da jawo wayar sadiq ya kashe sannan ya dau kayan sadiq da aka cire masa yaba daya daga cikin ma'aikatan asubitin su wanke.
Bayan ankamala dinner kowa ya dau hanyar zuwa masaukinsa majeed sai kiran layin sadiq yake, baya shiga dana Dr yakub, yana mamakin abun ya faru yau ya rasa mai ke damun sadiq hakura yayi da kiran tare da maida wayar aljihu.
Bangaran Basma ko kuka take sosai tare da taqaicin amincewa da auran sadiq, Khaleed sai bata hakuri yake tare da ganin rashin kyautawar sadiq ya rasa dalilin da zai mata irin wannan cin fuskar bayan tana qanwarsa kuma matar da zai aura, shi a ganinsa duk wanda ya samu Basma a matsayin mata ya mure, ya rasa me yasa sadiq ke nuna rashin ko in kulla a kanta, kuma majeed na gani ko ba komai yasan dole zai ji haushin sadiq da wannan tunanin suka qaraso gida ko Godiya bata masa ba ta shige gida da sauri tare da tsananta kukanta.
Motar su fatuha na fakawa majeed ya fara jero mata kalaman soyayya tare da jan ta jikinsa, ganin zai wuce gona da iri yasa fatuha sakin kuka, lallashin ta majeed ya shiga dan kukan fatu na d'aga masa hankali yayi mata peck, ko saurara shi ba tayi ba ta bale murfin motar ta fita da sauri.
Bangaran sadiq ko bashi ya tashi ba sai wajan 2:00am na dare a hankali yake ware sexy eye's ball's dinsa da wani irin ishin ruwa ya tashi, Dr yakub da ko rintsawa baiyi ba ya miqe da sauri ya qaraso wajan shi cikin cool voice sadiq ya ce, "Ruwa..! da sauri Dr yakub ya bude fridge ya dauko rubar ruwa ya bashi ko da ya sha ruwan miqewa yayi yana qoqarin cire jini da ake qara masa riqe hannusa Dr yakub yayi ya ce, "Captain me kake shirin aikatawa? ya fada bakin shi na rawa kallonsa Sadiq yayi ya ce, "so nake na tafi gida bana so majeed ya gane bani da lafiya, na san yanzu haka Basma name fushi dani, na ruguza mata farin cikinta saboda rashin hakuri na" ya ida zancan yana cire qarin jinin wasu hawaye ne masu zafi suka zubu ma Dr yakub ya ce, "Sadiq wai me yasa kake so ka raya rayuwar wani ka bata taka? why sadiq? Dr yakub ya fada yana jijiga sadiq kuka sadiq ya saki tare da cewa "ka dai kiran majeed da wani d'an uwa nane kuma na jini, bazan ta6a bari majeed ya mutu saboda bakin ciki na ba, nafi son farin cikin majeed a kan na kowa a duniya, bani da d'an uwa sama da majeed, kasan ko ya majeed ya ke waje na yana so na yana son farin cikina, tunda da nake da majeed bai ta6a nuna min abinda yake so ba kamar fatu ba, ina iya ce ma kan fatu majeed ya san me so saboda haka ban taba bari saboda ni ya rasa rayuwarsa..! sadiq ya ida zancan yana kuka mai tsuma zuciyar mai saurare a hankali ya ida cire kayan asibiti dake jikinsa yasa kayansa wayarsa ya dauka tare da kunna ta Dr yakub mutuwar tsaye yayi yana bin sadiq da kallo cikin bacin rai ya ce, "kai taka rayuwar yaya za'ayi da ita, kai taka zuciyar ayi yaya da ita? Sadiq ka fahimce ni kafi majeed buqatar fatu, kafi majeed son ta, ka duba halin da kake jefa kanka, ka falasa abinda ke ranka tun kafin gobe fatu ta zama malakin majeed..! tabbas yanzu yasan me sadiq yake nufi so yake ya rasa rayuwarsa ya zamar masa dole ya kawo karshan abunan ko saurarashi sadiq bai yi ba saima car key daya dauka tare da fita yana ingisawa.....
Vote
Comment
Written by
Salma mas'ud nadabo
Edit by
Raheenat
📘 REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄
★We are the best★
http/mobile.Facebook.com/Real-Hausa-fulani-writers-forum RHFWF-173984973194167/?refid=52red=opera_speed_dial_&yn=H-R
*Email* [email protected]
*Facebook* www.Facebook.com/REALHAUSAFULANIWRITERSFORUM.COM
91_92