← Book details Captain Sadiq Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 67

Sashe 30

Captain Sadiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

    Cikin jin dadi suka gabarta da darasin su inda malam yayi masu qari tare da yi masu yan tanbayoyi suka bashi amsa sai da ya tabatar sun gane misalin karfe hudu ya sallame su, ya wuce akan cewa gobe karfe hudu zai zo insha Allah littafan su suka kwashe suka shiga gid, dama daure da alwala  fatuha take  sallah ta gabatar sannan ta cire zanin ta shiga wanka tana fitowa daure da towel ta tsane jikin ta tare da shafa jikin ta da lotion har ta dauko uniform din ta zata maida ta tabe baki, tunda na gama aiki ai sai na sa na gida dan ni na fara gajiya da su.! ta fadi tana turo baki wardrobe ta bude ta curo wata pink gwon mai dogwan hannu rigar  simple ce mai kyau tayi shape sosai tayi mata kyau rigar ita kanta sai da ta yaba rigar parlour ta dawo ta zauna, jidda na zaune tana kallon carton itama ta zauna tana kallon.

    Ring din wayar shi dake bedside drawer ne ya tasheshi dan guntun tsaki yaja tare da kai hannu ya dau wayar, ba tare da ya duba suna ba ya  ce, "hello.!  cikin alamar gajia ta daya bangaran a kayi dariya, sadiq tashi yayi zaune tare da saki guntun murmushi, ta  daya  bangaran  aka ce, "wallahi sadiq baka da kirki Allah yasa ma ka gane mai magana? yar dariya yayi tare da shafa sajan sa ya  ce, "ba Khaleed bane? dariya Khaleed yayi ya ce, "ashe dai kana gane mutane" dan guntun tsaki sadiq ya ja ya  ce, "ya za'ai na kasa gane muryar childhood friend dina,"
     "ai ka kyauta ina majid ai ya fika zuminci,"
    "haka dai kace"
     "toh yau na leko Kano insha Allah zan shigo"
     "toh shikenan sai ka zo idan ka zo ka kira ni" toh yace tare da yanke wayar agogwan dake manne a bangwan daki ya kalla ware sexy eye's ball's din shi yayi "ohno na kwanta ina ta bacci har 4 ya gota.! tashi yayi tare da yaye blanket din jikin shi toilet ya shige ya sheqa wanka yafito daure da qaramin towel a qugunsa, hannun shi riqe da qaramin towel yana tsane sumar kan shi yana cikin shafa lotion wayar shi ta fara ruri hannu ya sa ya dauka tare da karawa a kunne ta  daya  bangaran  aka  ce, "hello big man ganin a filin gidan ku" smile sadiq yayi ya ce, "are u serious,?
   "yeah angayama kowa irin kane mara zuminci" dariya sadiq yayi  ya  ce, "kai friend nine fa"
  "koma yane.!
"toh shikenan ganin zuwa" katse wayar yayi tare da zura jallabiya white ya fito daga part din shi ya wuce su fatuha a parlour suna ta karatun dan fatuha ta dake sai jidda ta koya mata karatun boko yanzu haka har ta iya ABCD.

      Yana fita farfajiyar gida ya hango Khaleed jingine jikin motarsa mai tsada kallo daya zaka masa kasan shima dan hutu ne, kuma gaye ne sanye yake da shada  tasha diki mai kyau Khaleed chocolate colour ne yana da saje daya kara bayanar da kyawunsa, yana da manyan ido murmushi ya saki ganin sadiq ya qara so fararan haqoran shi suka bayana cikin jin dadi sadiq ya qaraso tare da miqa masa hannu suka gaisa ya  ce,  "Ashe dama zan kara  ganinka a duniyar nan? murmushi  Sadiq yayi  ya  ce, "bagashi ba ai kai ma baka zama shiyasa"
     "haka kuma dan last week ma na dawo daga London har muka hade da yaya jawad wajan shopping shi da matar shi har ya ke ce min sun kusa zuwa gida, jira kawai yake Aunty shukara da haihu su zo" murmushi Sadiq yayi ya ce, "haka ya fada min"  suna tattaunawa har suka qaraso kofar parlour cikin parlour suka shigo har yanzu su fatuha na nan inda ya bar su ,Sadiq ya ce  "Fatuha.! dagowa tayi ita da jidda tare da gaishe da Khaleed murmushi Khaleed yayi tare da amsawa yana bin fatuha da kallo Sadiq ya katse masa tunani da cewa "Fatuha ki kawo mana glass cup" ta ce masa toh tare da shigewa kitchen sadiq ya  ce, "jidda ga uncle.! Khaleed smile jidda tayi Khaleed murmushi yayi ya ce, "karka ce min angel ce ta girma haka"
      "ita ce mana" zaro ido waje Khaleed yayi ya ce, "kai.! amma gaskiya mun yadda zuminci, come here angel" kusa da shi jidda ta matso kallon ta yayi tare da daukar ta suka haura upstairs sai tanbayar ta ya ke tana zuba masa surutu suna shi ga part din Sadiq saman two sitar Khaleed ya zauna tare da daura jidda a cinyar shi, sadiq kuma fridge din bedroom ya bude ya curo lemu ka masu sanyi ya kawo ma Khaleed lokacin yayi dai-dai da shigowar fatuha dauke da tray da cup's amsa tray din Sadiq yayi tare da yi mata nuni da ta dau jidda, Khaleed sai bin fatuha da kallo ya ke kiran jidda tayi suka fita a tare tana fita Khaleed ya sauke ajiyar zuciya, yana kallon  Sadiq, Sadiq din ma kallon shi yake ya  ce, "big man ina kuka samo beautifully girl,"
     "wake nan ya? fadi a taqaice
"wadda ta dau angel yanzu" murmushi Sadiq yayi ya ce "Fatuha she is my sister baka ga muna kama ba" ya fadi zancan yana cigaba da zuba ma Khaleed juice khaleed ya  ce, "amma ai nasan kai ne dan auta baka da wata sister" bashi glass cup yayi na lemo yana qara saki wani murmushin wanda iya karshi lips din shi ya  ce, "she is my consin sister yanzu ka gane ko" murmushi Khaleed yayi ya ce, "amma fa tana da kyau karka ce min Basma ce ta zama mai kyau haka" tanbayar Khaleed ta kusa fara kai Sadiq wuya amma sai ya maze ya ce, "ba ita ba ce wannan diyar sister mom ce"
     "eyya.! shi kansa Sadiq yana mamaki karyar da ya zauna yana shunfuda ma Khaleed me  ke  damun  sa  haka toh me idan ya ce masa yar aiki ce, dan guntun saki ya ja a zuciyar shi  khaleed ya  katse  sa  da  cewa, "Sadiq mom fa?
      "Mom ba ta nan sun tafi uk da Abba" OK hira suke sha sosai suna kallo.

Written by
       Salma mas'ud nadabo

Edit by
   Raheenat

📘REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄

http/mobile.Facebook.com/Real-Hausa-fulani-writers-forum RHFWF-173984973194167/?refid=52&red=opare_speed_dial_&yn=H-R

*Email*:[email protected]

*Facebook*www.Facebook.com/REALHAUSAFULANI WRITERS FORUM.com

                    55_56
Chapter 30 · 0% Book details