← Book details Captain Sadiq Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 67

Sashe 21

Captain Sadiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

      dauke da jidda fatuha ta fito, lokacin  yayi  dai-dai  da shigowar  sadiq  parlour ballama fatuha harara tare da kauda kai, itako tayi kamar bata gani ba, yana gaba suna bayan shi jidda na zuba surutu suna shiga part din a parlour fatuha ta aje jidda tana qoqari fita, kamar  daga  sama  ta ji  zazakar  muryarsa ta doki dodan kunna  ta "keee.. Yace da ita birki ta ja ta tsaya zuciyar ta na dukan uku-uku dan bata manta rashin kunyar da ta masa ba da safe  maganar sa  ce ta  kara  dawowa  da  ita  daga  duniyar  tunani "ba dake nake magana? ya fada cikin daka tsawa, juyowa tayi tana zare ido  ya ce, "kije kitchen ki hada min coffee ki kawo min" zaro ido fatuha tayi waje take ce, "uhm kwarankwatsi ban san me hakan ba" tsoki yaja mtss "yar kauyan banza toh  bunu nake nufi tea mara madara zaki had'a ki kawo min  karki sa sugar a ciki" ya ida zancan tare da balla mata harara abin ma dariya ya so ya ba fatuha wani lokacin sadiq idan yana harara kamar qaramin yaro a zuciyar ta ta ce, "bai ma san idan yana fada wani qara kyau yake ba..! ta dan ja tsaki ta fita, saida ta gama hada masa ta kai masa yana zaune parlour yadda ta barshi jidda na saman cinyar shi da alama bacci ya dauke ta hannu ya miqa zai amshi coffee tana bashi ya saki cup din ya fadi gaba daya ruwan tea din ya zube mata a kafa wani irin ihu fatuha ta bude baki zatayi wata  irin  fisgowa  sadiq  yama  fatu  ta  fado jikinsa tare da toshe mata baki yana kallon ta damn sanyayin  idanusa ido cikin ido, idanuwan fatu t cicikowa sukayi da kwalla hawaye daya nabin daya saboda  azabar  ruwan  tea  din  daya  konata.
   murmushi mugunta  yayi na  gefan baki komin banza ya sata kuka, gashi matsar da yayi ma bakin bana wasa bane dan bakin sai radadi yake mata, sai da tayi kuka san ranta sannan ya sake ta tare da hankada ta ta fadi kasa sannan ya tashi ya kashe kayan kallo ya matso gaf da ita har tana jin saukar numfashinsa tana  sauke  ajiyar  zuciya  sama-sama tuni  idanu  ta  sun  rine  zuwa  ja  sadiq ya ce cikin cool voice nasa "wannan kad'an na maki akwai saura nan tafe..! ya ja saki tare da daukar jidda sai da ya kai bakin kofar bedroom ya juyo tare da yin killing smile din shi ya cigaba da cewa, "kuma ki tabata kin gyara gurin kafin ki bar wajan? Yana fad'in hakan ya shige bedroom ya barta tana matsar kwalla tare da jera masa Allah ya isa ta  ce, kuma indai gyara gurine wallahi banyi mugu kawai sannan taja kafar ta wadda ta kone wajan har yayi ja bakin tama haka saboda ya ji matsar manya.

      Direct bedroom dinta ta wuce  tare da rage kayan jikinta, bathroom ta shige tayi wanka ta fito daure da towel tana shafa mai tana mai cigaba da jera masa Allah ya isan, a haka har ta gama shirin tafada saman bed se bacci...

Written by
        Salma mas'ud nadabo

Edit by
      Raheenat

📘REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄
★we are the best★

http//mobile.Facebook.com/Real-Hausa-fulani-writers-forum RHFWF-173984973194167/?refid=52&red=opare_speed_dial_&_yn_=H-R

*Email*:[email protected]

*Facebook*:www.Facebook.com/REALHAUSAFULANI WRITERSFORUM.com

                         41_42

Kiran sallah asuba ne ya tada fatuha, alwala ta d'auro tare da yin wanka bayan ta idar da sallah ta shafe jikin ta da mai kamar kullun tare da fesa turare  uniform ta zure sannan ta d'aure gashin kanta wanda dakyar ta kama sa, ganin bai kamuwa yasa ta sake shi haka kawai ta fita direct part din sadiq ta shiga tana karema parlour  kallo, har yanzu glass din jiya nan zube a parlour baki ta ta6e ta shige bedroom sadiq na kwance jidda na maqale a jkinsa da alama daga masallaci ya dawo bacci ya kwashe shi dan jalabiya ce a jikin sa ba night dress ba sajan nan nashi yayi luf-luf kwance, qare masa kallo fatuha tayi sannan ta bala masa harara  ta  ce, "kamar idanuwan shi biyu..!  a hankali ta sa hannu ta fara janye jidda daga jikinsa jawo jidda ya qara yi ya maqale ta, abin ma dariya ya ba fatuha qara jan jidda tayi shima ya qara jan jidda haka suka riqa ja inja  qara leqa fuskar sa tayi taga dai bacci yake a hankali ta qara miqa hannu zata janye jidda cikin dubara  ta janye jidda direct bathroom ta dire ta, kamar kullun ta shirya jidda murmushi tayi  washe da baki  ta ce, "Anuty I like you" murmushi fatuha tayi tare da langwabe kai ta shafa kan jidda tare da cewa, "jidda kisan ban iya wannan yaran ba" murmushi jidda tayi take ce, "ina nufi kina birge ni Anuty" murmushi fatuha tayi wadda ya baya kyawawan hakoran ta ta ce, "nima haka Jidda" peck jidda tayi mata itama fatuha peck tama jidda.

     Jawo hannun jidda  tayi cikin nishadi suka qaraso dining area tea ta shiga hada ma jidda mai kauri, wanda yaji ovaltine da madara  tare da bread n egg a hankali ta shiga feeding din jidda tana amsa itama idan taji dadi sai ta gutsuro bread din taba fatuha, Mom da Abba ne suka qaraso cikin fara'a dining area cikin ladabi fatuha ta gaishe su, cikin  fara'a suka  amsa hada masu breakfast fatu ta shigayi, jidda ce ta washe baki tare da cewa, "morning grandma n grandpa"
      "morning too angel" suka amsa a tare  bayan fatu  ta gama hada masu ta aje masu cikin nishadi suke breakfast.

    Tsaye yake gaban dress mirror sanye da bathrobe hannu shi riqe da qaramin towel yana goge sumar kanshi da alama daga wanka ya fito, cikin nutsuwa yake shirinsa lotion ya shafa tare da saka uniform din sa sannan ya feshe jikinsa da turaruka masu kamshi, booth din shi ya curo ya saka black sai sheqi yake tsaf ya fito sojan shi hula shi ya dauko ya sa sai agogo silver na azurfa wanda  ya  dace  da  tsintsiyar  hannusa wani irin kyau yayi ba d'an kad'an ba  sai dai fuskar nan d'aure ba  wani  walwala  kamar  kullun briefcase nasa ya dauko tare da d'aukar wayarsa da ke bedside drawer a hankali ya bud'e kofar bedroom kallo daya yayi ma parlour tare da jan dogwan tsaki ya  furta, "fatuha kin rainani wallahi..! sannan yasa qafa ya fito daga part din a hankali yake saukowa daga upstairs tuni kamshi turaran shi ya mamaye parlour fatuha da ke feeding din jidda ta dago idanuwa tana qaremasa kallo sosai  take  ganin  kyan  sadiq har ta  manta  kanta  wajan  kallonsa, cikin isa ya qaraso wayar shi ya cure ya kara a kunne cikin nutsuwa yake wayar.
      "holle ole.! daga daya bangaran ola ya ce, "hello boss"
        "ka zo ka amshi briefcase dina" to ya ce masa tare da kashe wayar ya qaraso dinning area smile yayi wanda  iyakar  le66ansa tare da gaishe da su Mom jidda washe da baki ta gaishesa haka fatuha banza yayi da ita kamar bai ji ba tare da qare mata kallo  ganin  yarda  gashin  ta  ya  kwata  har  gadon  baya,  tsintar  kansa  yayi da  maganar zuci, "yau kuma wani sabon iskancin yima mutane yawo a gida ba dankwali  ya  kamata yana yin maganar ne  duk cikin zuciyarsa.
           a hankali ta jawo cup da niyar hada masa breakfast hannu ta ya rike ya wurga mata wani irin kallo ya aje hannu tare janye cup din Mom ce ta aika masa harara sai yayi kamar bai gani ba ya cigaba da aikin da ya ke ole ne ya shigo cikin sallama suka amsa sannan ya amshe briefcase din sadiq ya fice da ita Abba ne ya katse shurun da cewa,  "Alhamdulillah ka ce min qafa ta warke? murmushi sadiq yayi tare da cewa, "eh Abba.!
           "toh masha Allah"
   "Abba ya maganar kwangilar ku kunko samu?
         "a'a munan dai muna fama amma insha Allah this time around zamu samu abinda muke so insha Allah" murmushi sadiq yayi tare da cewa, "Allah yasa" Mom ta amsa da ameen tashi yayi tsaye tare da cewa, "oya angel mu tafi" Mom  ta  katse  sadiq  da  cewa "baby karka ce min ruwan tea din har ya isheka ba bread ba komai"
         "eh Mom na koshi"
      "toh shikenan, ka  dai  kula  da  kanka" hannu jidda ya kama har sun kai baki ko Abba ya ce, "yauwa baby ina san fadama ranar Sunday tare da Mom din ku zamu tafi uk"
        OK sadiq ya ce tare da sa kai ya fita fatuha na biye da su da lunch box din jidda har gaban mota sannan ta miqa wa jidda lunch box din tare yi mata peck sadiq kallon su yayi tare da ta6e baki har  mamakin  shakuwar  jidda  da  fatu  yake  bai  ta6a ganin  mai  aikin  da  angel ta  shaku  da  ita  ba  kamar  fatu  ba  kawar da  tunanin  yayi sannan ya shige mota.
Chapter 21 · 0% Book details