← Book details Captain Sadiq Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 67

Sashe 49

Captain Sadiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

      Jingine yake saman kujera office ya rasa sukuninsa, idanuwan shi na lumshe saboda nauyin da suka masa har wata masasara ke rufe shi ga wani  irin  zafi da qirjinsa ke masa, tamkar  an  daura  masa dutse  mai  nauyi a hankali ya ware sexy eye's ball's dinsa da suka rine sukayi jaa wayarsa dak'e ruri cikin aljinhunsa ya curo sabuwar number ce baro-baro a screen din, da kamar ba zai dauka ba sai ya daure ya dauka tare da karawa a kunne, daga  dayan  bangaran cikin zazakar muryata cikin yauki Basma ta masa sallama, amsawa yayi a taqaice tare da tanbayar, "wake magana? gyara kwanciyar tayi daga inda take tare da kankame wayar dan wani irin sanyi ke ratsata, dan gyaran murya tayi cike da shagwaba ta ce, "Yaya sadiq ni ce fa Basma..! ko number ta ashe baka da ita? ta ida zancan cikin shagwaba Sadiq dake kishingide saman kujera, ranshine ya qara suya dan shi duduniya ba macan dake birge shi ko bashi sha'awa kamar fatuha, ko wannan magana ma da take yi jiyake kamar tana watsa masa ruwan zafi,  tsuke fuska sadiq yayi kamar tana ganinsa ya ce, "Yanzu ina wani aiki ne letter mayi magana idan na dawo gida" bai jira cewarta ba ya katse wayar tare da yin wurgi da ita ta daki bango ta dawo watse ko ta kanta bai bi ba ya sa kai ya fice daga office din, domin idan ya cigaba da zama tabbas kwakwalwar shi da zuciyarsa suna iya bugawa.
            bin wayar tayi da kallo tare da dan bata fuska, ta aje wayar ta kwanta.

    Ko da aka tashi su fatuha majeed ne ya zo daukar su, ganin shine yasa ta had'a gira sama data kasa dan ba abinda ta tsana kamar ganinsa, ba yadda ta so haka ta bale murfin motar ta shiga tare da gaishe shi, kallon ta yake mai cike da so da kauna, sannan ya ce "My love daga gani yau kin sha wuya da yawa? ina fata dai kina kulla min da kanki?" dan guntun tsaki fatuha ta ja ciki-ciki sannan ta ce a cikin zuciyar ta "Har wani kira kake na kulla ma da kaina mtww dan iska kawai" muryar  majeed ce ta doki dodan kunnan ta a karo na biyu ya ce, "My love! ko duk gajiyar ce tasa ko magana ba'a san yimin?" dan smile fatuha tayi wanda iyakar shi la66an ta ta ce "A'a" murmushi majeed yayi tare da cigaba da driven, haka ya dinga janta da surutu tana amsa masa sama-sama sannan ya wuce da su shoprite yayi masu siyaya ice cream da cake, jidda ko sai dadi take ji dan har yanzu bata san inda aka dosaba.

        Suna kunna hancin motar su, suka ci karo da sadiq wanda shima dawowarsa kenan wani irin dogon numfashi sadiq yaja a duk lokacin da yaga majeed da fatuha, numfashinsa sai ya nemi ya dauke ko qirjinsa ya dinga masa zafi, dakyar ya iya d'aga kafarsa dan baya so ko fuskar su ya gani sun fito a tare, amma sai dai kash majeed ya riga ya kira sunan sa. lumshe ido yayi ya tsaya chak! sai da ya kwashe yan mintina sannan ya waigo tare da sakin smile din karfin hali, ta gabansa fatuha ta raba ta wuce jidda nata zuba masa surutu sannan itama ta shige, miqa mashi hannu majeed yayi suka gaisa ya  ce, "big man duk yau ban ganka a office ba"
       "oh ina cikin office ina wani aiki ne gobe ma nake so na wuce Lagos"
          "Lagos kuma? me zaka je yi lagos? cewar majeed
          "zan je nayi 2week ne cikin ruwa na dawo"
        "Eyya to Allah ya taimaka"
  "Amin..! yana qoqarin shigewa majeed ya ce, "Baby..!
      "yes..! ya ce a taqaice
"dama ina so muyi wata magana"
       "ok mu shiga ciki" ok majeed yace tare da bin bayan sadiq suka shiga part din sadiq briefcase dinsa sadiq ya aje tare da rage kayan jikinsa ya shiga toilet, ya dade a toilet din baiyi wankan ba yana kukan bakin ciki sannan ya tashi yayi wanka, sanye da bathrobe ya fito da qaramin towel a hannusa yana goge jikinsa, majeed na zaune saman sofa shima tashi yayi ya shige toilet ya sheqa wanka ya fito ko da ya fito lokacin sadiq ya shirya cikin black 3 quarter  da white shirt mai gajeran hannu, yana zaune saman sofa idanuwansa lumshe, shiryawa majeed yayi a tsanake sannan ya bude wardrobe din sadiq ya ciro riga da wando riga blue sai dark blue jeans sannan ya bude fridge ya curo fresh milk ya tsiyaya a cups ya miqama sadiq ya amsa.
           zama yayi kusa da sadiq ya ce, "Please ina so kamin taimako guda daya please?
      "ok inajin ka indai baifi karfina..! murmushi majeed ya saki ya ce "Bai fi karfin ka ba"  gyara zama sadiq yayi yana sauraran majeed riqe hannusa majeed yayi cikin lagwabe kai ya  ce, "please baby kamin hanya fatuha ta so ni..! tsura masa ido sadiq yayi da idanuwansa da suka ciciko da kwala hadiye su yayi yana saurara majeed ya  cigaba  da  cewa, "baby ina  son  fatu wallahi ina sonta i  love  her  more than how  you  think, ban ta6a jin son wata  d'iya  mace ba kamarta ba, baby karkayi tunanin irin son da nake ma sauran yan'mata nake mata a'a son ta nake da gaske ba  da  wasa ba, idan har  na rasata zan iya rasa rai na ina  jin  sonta mai  yawa  sadiq  na  kamu  da  sonta  mara  musaltuwa  ina  manta  kai a  gabanta  ita  ce  bugun  zuciyata sadiq...!  majeed ya fada, da  sauri-sauri  numfashin  sadiq ke  gudu  zaune  yake tamkar  an  dasa  akwai yana bin majeed da ido kamar sakarai gabaki daya  jikin shi ya mutu sai zuciyarsa dake tsinkewa kamar zata fito waje dan  tashin  hankali, dan matse hannusa da majeed yayi ya sasa dawowa daga duniyar tunanin, smile ya saki yana  kallon majeed  ya  ce, "my man karka damu kaji d'an jama aji take amma nasan zata so ka kaji, kasan yadda mata suke amma nasan zata so ka  har ku dai-daita  babu  macan  da zata  same  ka  ta fasa kai  kasan  da haka, kana  da  abinda  kowace  'ya  mace  zata  so ka" murmushi majeed ya saki tare da kaima sadiq hug ya ce, da  gaske  Bros..!
      "Eh mana.!
"Ka  tabbata  fatu  zata  so  ni?
    "Sosai  ma..! hawaye dake  maqale  idon  sadiq  ne suka cigaba da anbaliya dan ko yasan ya rasa fatuha, dan baya fatan abinda zai samu majeed dan uwan shi abokinsa mai  son  farin  cikinsa bashi da aboki dan uwa saman da majeed, mai  yasa  ma  tun  farko  yake  kishin  d'an  uwan  nasa, lokaci yayi da ya kamata ya ba zuciyarsa hakuri jin majeed zai zame jikinsa yasa sadiq saurin share hawayansa tare da sai ta kansa murmushi suka sakar ma junan su, fira suka fara sama-sama kiran sallah magrib ne ya tashe su.

  1week letter

      Shirye-shiryan aketayi a family house, kasancewa yau za'a sa rana biki duk wanda ka kalla cikin farin ciki yake musanman Basma da majeed.
       zaune suke cikin d'akin yan'mata sunata zuba hira muryar Basma kadai ke tashi fatuha na gefe tana matsar kwalla dan har yanzu gani take kamar wasa, kamar kuma  a mafarki tashi tayi ta fita daga d'akin ganin kayan da ake ta wucewa da sune yasa jikin fatuha qara sanyi.
       fitowa tayi daga parlour hango qanan Baffa tayi su baba Barau  kasancewa  komai Abban sadiq  ya  ce zaiyi  tunda  fatu  hannusa  take, wasu hawaye ne masu zafi suka sulalo mata yanzu ta tabbatar za'a samata rana da wanda bata so a matsayin miji kuka ne ya ci karfin ta, fita tayi daga gidan gabaki daya dan ko sanin inda zata ba tayi ba jefa  kafar  kawai  take  kan  titi, can baba jummai ta fado mata a rai keke napep ta tara ta shige  ta ce, a kaita gadan qaya" kasanwcewar gidan baba jummai kan titi yake bata wani sha wahala kwatantawa mai napep  gidan ba kukan da take yasa mai keke napap din bar mata kudin saboda ya tausaya mata.
          ko sallama bata cika ba ta shige gidan, baba jummai dake qoqari fita, fatuha ce ta fada jikinta tare da sakin kuka kamar ranta zai fita, rud'ewa baba jummai tayi tana kallon ta baki sake tana  cewa, "ke  lafiyar  ki  'yan nan  wani  abune ya  faru? zaunar da ita saman kujera Baba  jummai  tayi tana qara tanbayar ta lafiya kuka take sosai, cikin shasheqar kuka ta ce, "Wallahi baba bana son majeed bana jin zan iya zaman aure da shi..! ta ida zancan tana rushewa da kuka, sallati baba jummai ta hauyi tare da tafi tana  cewa, "na shiga uku ni jummai , me nake ji haka fatuha sokike ki ja mana abin fade? kowa  yana  mana addu'a Allah  ya  rufa  mana  asirri ya  kai  ki  gidan  sutura, yanzu  kuma  ki  ce  ba  haka  ba, toh idan ba majeed ba wakike so? kuka ta kuma saki cikin shasheqar kuka bakin ta na rawa ta ce, "CAPTAIN SADIQ nake so Baba..! Baba idan na rasa sadiq mutuwa zanyi, ni  shi  nake  so" ta ida zancan tana kuka mai tsuma zuciya, zaro ido waje baba jummai tayi  ta  ce, "na shiga uku ni jummai..! rungume fatuha tayi tana lallashi dan ita kanta ta tausayama fatuha ita kanta taso ace da sadiq din za'ayi, amma ya zasuyi tunda shi bai ce yana so ba? d'ago da fatuha tayi tana share mata hawayan ta ta  ce, "kiyi hakuri fatuha kinji ki cigaba da addu'a Allah yana tare dake Allah zai dubi zuciyar ki ya baki mafi alheri fatuha, ki sama zuciyar ki sallama kinji" ajiyar zuciya kawai take saki tayi lamo a jikin baba jummai.
Chapter 49 · 0% Book details