← Book details Captain Sadiq Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 67

Sashe 22

Captain Sadiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

     A hankali ta juyo ta shige gida, kwashe kayan breakfast din tayi Mom na zaune a parlour tana kallo fatuha ta zo ta wuce kitchen, washe da baki ta gaida baba jummai itama baba jummai washe da baki ta amsa, rabi'a na gefe tana gyara kayan miya tayata fatuha ta shiga yi suka gyara tare sosai ta taya su  baba jummai, saboda aikin kitchen na burge ta kusan tare da ita aka dafa lunch baba jummai ko dadi take ji har qosawa take suje kauye jauro yaga yadda fatuha ta koma kamar balarabiya, ta  wani  siko  ta  zama  yan  mata bayan sun gama aikin fatuha ta wanke duk wani kwano da akayi anfani da shi rabi'a ko sai hanata take amma taqi bari sai da suka gama komai sannan fatuha ta dawo parlour, ko da ta dawo Mom ta bar parlour  bedroom ta shige tare da rage kayan jikinta bathroom ta shige ta watsa ruwa d'aure da towel tafito bayan ta gama komai sannan ta tuna ashe bata gyara part din sangamin ba,  ko mai bata shafa ba ta zura kayan ta direct part din sadiq taje ta fara gyara sai da ta gyara shi tas, sannan ta zauna a parlour saman three sitar tana maida numfashi  lumshe idanunta tayi tare da ware su, fita tayi daga part din ta koma bedroom ta kuma watsa ruwa sannan ta shefe jikita da mai tare da fesa turare da maida uniform din ta.

   Misalin karfe 2:00pm su jidda suka dawo, kasancewar yau sadiq bai da wani aiki tare suka dawo, part dinsa ya nufa masha Allah gyaran part din ya masa yana jin dad'in ganin part din shi a gyare, duk rashin jin fatuha tasan aikin ta shiyasa wata rana yake d'aga mata kafa, bathroom ya shige ya watsa ruwa ya fito cikin wando da riga ya shirya, kayan sun masa kyau sosai, bangaran su fatuha kuwa jidda na dawowa yadda ta saba yi mata haka ta mata sannan tace taje parlour ko da ta fito parlour  daddyn ta gani jikinsa ta fad'a tana zuba masa surutu shikuma yana sauraranta yana jin dad'i, Mom da Abba ne ke saukowa daga upstairs Abba sanye da shada malin-malin  brown Mom na sanye da atamfa pink mai ratsin green n bleu sanye da mayafinta ba qaramin kyau sukayi ba, parlour suka qaraso washe da baki jidda ta sauka daga jikin sadiq ta riqe hannun grandpa murmushi Abba yayi ya ce "Sadiq yau da wuri ka dawo daga wajen aiki  kenan?" smile yayi tare da cewa, "eh..!
      "to mu zamu wuce gidan Ammi mu masu sallama"
           "to Allah ya tsare"
"ameen.! jidda ce ta ce, "grandpa zan biku"
    "toh shikenan yima fatuha magana" cewar Mom, "sai muje tare ko" rugawa tayi bedroom fatuha kuwa tunda jidda ta fita wani irin bacci ne ya sure ta ko da jidda ta shigo ta samu fatuha na bacci veil din ta ta d'auka tare da fita tana  cewa, "grandma Anuty na bacci"
     "toh shikenan tunda bacci take mu tafi kawai ta samu hutu ne" washe da baki jidda ta bi su Abba, sadiq ya rako su har parking space sannan ya koma gida ko da ya koma wani irin killing smile yayi upstairs ya haura sannan ya fito kitchen ya shiga ya dako ruwa a fridge mai sanyi wanda har qanqara ya fara saboda tsabar sanyi a hankali ya murda handle din kofar dak'in fatuha ya shiga.
        hangota yayi saman bed kwance tana sharar bacci gashin ta ya baje saman gadon,  da  alama  tana  jin  dadin  baccin cije lips yayi sannan ya qaraso sai da yazo dai-dai face nata ya bud'e murfin rubar ruwan ya juye mata shi, fatuha da ke bacci wani irin razana tayi ta tashi cikin  gigicewa ta yunkura zata fita saboda tsoro, sadiq ya jawo gashin kanta tare da dauke ta da lafiyayan mari,wani irin kuka fatuha ta saki tare da zama saman bed jajayan eye's din ta ta dago tana kallon sadiq wani irin murmushi yayi ya ce "Fatuha yau zan koya maki hankali, bani kika so ki nakasa ba? toni yau kona maki gashi zanyi" ya ida zancan tare ya matse mata fuskarta, idanuwan fatuha sunyi jawur sai kuka take tana bama sadiq hakuri ganin  ya  koma  mata  bakin  kumurci  dama  ya  lafiyar  giwa  bare  tayi  hauka sosai  tsoron  sadiq  ya  d'arsu a zuciyarta  ganin  abinda  yake  kokarin  yi  ta  zaro  manya-manya  idanuta  waje, ashana ya ciro a aljihun shi ya kunna tare da fusgo gashin ta wani irin kuka fatuha tasa tana  cewa, "dan Allah mai kyau kayi hakuri wallahi bazan sake ba" ta ida zancan tana qara rushewa da sabon kuka "shhhh.! yimin shiru fitsarariyar banza..! nufo gashin ta yayi da wutar dake  hannusa take fatuha ta fashe da wani sabon kukan tare da tafiya luuuu ta sume, murmushi sadiq yayi ganin suma tayi ya ce, "marar kunyar qarya" kitchen ya koma ya d'ako wani sabon ruwan sanyi ya dawo bedroom ya qara juye mata shi wata irin ajiyar zuciya ta saki tare da fashewa da kuka tana bama sadiq hakuri sam  ta  kasa  kwatar  kanta  saboda  yarda  sadiq  ya  matse  ta  can  karshan  bed  har  suna  jin  saukar  numfashin  juna  su, da  sauri-sauri  numfashin su  ke  harbawa  harda  sadiq  din  daya  matse  ta, cije lips yayi yana qare mata kallo yarinya ce sosai amma sai rashin kunya duk a zuci yake wannan zancan, bindiga ya ciro ya daura mata akai tuni fatuha ta saki fitsari ta sauke numfashi agwagwame cikin sarkewar murya ta ce, "dan Allah mai kyau kayi hakuri bazan sake ba" tsaki yaja tare da cewa, "fitsari ma kikayi ko? ya  fada  cikin  daka  tsawa  bakin  fatu  na  rawa  ta  ce, "a'a wallahi ruwa ne haka wallahi" murmushi gefan  baki  yayi ya  kara  hada  rai dan yasan qarya take yana  kallon  gashin  kanta  daya  hargitse sannan ya ce, "daga yau sai yau kika qara min rashin kunya sai na 6ula maki kai da wannan abar kina  jina ? girgiza kai tayi alamar baza ta sake ba, sannan ya  hankada ta kanta ya bigi gado ta qara sakin wani sabon kukan sannan sadiq ya sa kai ya fita.

Written by
         Salma mas'ud nadabo

Edit by
      Raheenat

📘REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄
★we are the best★

http//mobile.Facebook.com/Real-Hausa-fulani-writers-forum RHFWF-173984973194167/?refid=52&red=opare_speed_dial_dial_&_yn=H-R

*Email*:[email protected]

*Facebook*:www.Facebook.com/REALHAUSAFULANIWRITERSFORUM.com

                       43_44

Sai da fatuha ta ci kuka sosai tare da jerawa sadiq Allah ya isa, sannan ta tashi jiki ba qwari ta nad'e zanin bed din  Allah ya taimake ta katifar akwai leda dan haka ruwan da fitsarin bai shige cikin katifar ba, iya karshi saman bedsheet tatare shi tayi ta aje ta shiga toilet ta watsa ruwa, tana gamawa ta fito ta d'auki bedsheet din ta wanke shi tas sannan ta fito da bokitin ta aje agefe sai da ta shirya tsaf sannan ta dau bokitin ta fita ko da tafi dasu ola taci karo da Sunday yaran sadiq suna ta shawagi a tsakar farfajiyar gidan, kai tsaye wajan shanya ta nufa ta shanya bedsheet din sannan ta dawo ta zauna saman wata resting chair da ke a farfajiyar gidan, lumshe ido tayi tana jin wani tsoro sadiq na ratsa ta, wasu hawaye masu zafi na zubo mata, dan yau ba qaramar wahala tasha a hannun shi ba take nan wani zazza6i mai zafi ya lullu6e ta sakamakon ruwan sanyin da sadiq ya sheqa mata, ganin masasarar taci qarfin ta yasa ta ja jiki ta koma parlour saman three sitar ta zauna ta qudindine waje daya  tana kyarma abin gwanin ban tausayi😰.

    Bangaran sadiq ko zuciyar shi fes bathroom ma ya shige ya sheqa wanka bai jima sosai ba ya fito daure da towel da dan karami yana tsane gashin kansa,  gaban dress mirror ya tsaya yana gyara kanshi da ya tuno da yanda fatuha tayi sai ya saki murmushi jin dadi bayan ya gama shiryawa cikin 3quarte  da armless t-shirt din shi cikin shirin shi na zuwa gym, sannan ya feshe jikinsa da turare masu sanyi kamshi a hankali ya bude handle din kofar tare da barin part din cikin isa yake sakowa daga upstairs, fatuha ya hango saman three sitar qudindine kauda kansa yayi yana qoqarin fita har yayi gaba sai kuma ya dawo saboda rawar  sanyi  da yaga jikinta nayi har ana  jiyo  had'ewar  hakoranta yasa yaji tausayinta kadan azuciyarsa, a hankali ya qaraso gaban three sitar  ya leqa fuskar ta wadda tayi jawur ga shatin hannu shi kwace a fuskar ta lumshe ido yayi tare da waresu a kanta, a hankali ya kai hannu ya ta6a goshin ta ji yayi goshi da zafi rau  kamar wuta, a hankali fatuha ta ware idanuwan ta ta fara rera masa kuka a tunanin ta wani muguntar ya zo ya mata, daurewa yayi tare da cewa, "yima muta ne shuru kafi na kife ki da wani sabon marin..! tsuru-tsuru tayi tana kallonsa cike  da  tsoro  da  fargaba ga wani irin zazza6i da take ji, lumshe ido tayi ta juya masa baya wayar shi ya ciro dake aljihunshi ya  kira  doctor bugu daya biyu Dr yakub ya dauka sannan ya sheda masa yana buqatar ganin shi, OK ya ce masa tare katse wayar sannan ya kalli inda fatuha take kwance hata gashin kanta jiqe yake, haka  nan  ya  tsinci  kansa  da  tausayinta miqewa  yayi  tsaye  hannuwansa na  zube  cikin  aljihu  yana  karewa  fatu  kallo a hankali ya kai hannu ya d'auki fatuha ita ko sai matsar kwalla take tana  mutsu-mutsu  a jikinsa  cike  da  tsoro tana bashi hakuri banza yayi da ita bai dire ta ko ina ba sai bedroom dinta, saman bed ya direta sannan ya dau ko hand dryer daya ke anfani da ita  fatu  nata  binsa  da  idanuta har  ya jona  hand dryer  jikin soket ya  tako  gabanta gashin  kanta  ya  kama ya busar mata da kanta fatuha ko sai bin shi take da ido AC dakin ya rage ma gudu tare da rufe ta da blanket har  lokacin  fatu  da  ido  take  binsa  tamkar  mutum-mutumi ya koma gefe ya zauna fatuha ko lumshe ido tayi kamar mai bacci.
Chapter 22 · 0% Book details