← Book details Captain Sadiq Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 42 OF 67

Sashe 42

Captain Sadiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

     Bedroom ta shige tare da yin wanka, kaya ta fido  ta rasa wanda zata sa duk wanda ta fido sai ta maida can ta hango wata red gown me stone's, aje ta tayi a gefe ta tsantsara kawalliya ba qaramin kyau tayi ba, sannan ta zura riga masha Allah indai maganar kyau ake fatuha ta kai, angel ce ta shigo da gudu itama sanye da gown pink ta ce "Aunty daddy ya dawo?" waigowa tayi tare da yin fari da ido cike  da  zakuwa suka fito a tare  shigowar sadiq parlour kenan su fatuha suka fito, kallo sadiq ya bisu da shi mai cike da so rugawa su kayi a tare suka rungume sadiq dariya ya saki kamar  yarda  suma suke  cike  da  farin  ciki  ya  ce, "zaku kadani.! Mom dake saukowa daga upstairs dariya ta saki ta ce "Sadiq kai da yaran ka kuna dirama wallahi" smile yayi tare da hug din Mom in taqaice maku duk wani girki da fatuha tayi sai da sadiq ya ci inda yake ta binta da kallo, ganin ta  kara  girma.

      Bayan ya hutu ya fido tsaraba yabama fatuha I phone 6 waya dadi da murna wajan fatuha ba'a magana jidda kuma Tap Apple mai shegyan kyau tare da new Teddy's haka suka dinga zuba murna baki har kunne.

         *2years letter*

     Wata kyakyawar matashiyar budurwace da baza ta wuce 16 years ba ta rugo da gudu daga upstairs gudu take amma komai na jikin ta amsawa yake sanye take da 3 quarter pink sai riga white mai gajeran hannu tana  sakin  murmushi  mai  qara  fito  da  zalla  kyanta bangaje mutun da tayi ne ya sata tsayawa chak, cikin cool voice din ta ta ce "Sorry ..! tare da ra6awa ta gefansa ta wuce mutuwar tsaye majeed yayi yana binta da kallo jin  wani  abu  ya  harbi  zuciyarsa  lokaci  daya kafadarsa ya d'age tare da sakin killing smile yabi stair's din da kallo, yana  ayana  yarda  ya  ganta wai gowa ya kuma yi ko zai ga yarinyar amma ba alamar mutum sauke  ajiyar  zuciya  yayi.
      sama ya haura direct part din sadiq ya wuce a hankali ya murda handle din kofar ya shigo, sadiq na zaune saman three sitar yana kallon news cikin sallama ya qaraso amsa masa sallamar yayi tare da aika masa harara wasa ya  ce, "sai yau zaka nemeni dan raini senses? dariya majeed ya saki tare da cewa "Sorry" ya zauna yana  cewa, "ni dai yanzu ba wannan zancan ba wacece na gani yanzu kamar daga part din nan ta fito? gaban sadiq ne ya yanke ya fadi qaqaro murmushi karfin hali yayi ya ce "Fatuha ce" *(Ohni salma🤦‍♀ yaushe fatuha ta waye haka🙄lol)* ok majeed yace tare da cije lips dinsa  yana ayana  wasu abubuwa a ransa......hmmmm

Muje zuwa fan's😘

Vote
      Comment

Written by
      Salma mas'ud nadabo

Edit by
     Raheenat

📘REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄
★We are the best ★

http/mobile.Facebook.com/Real-Hausa-fulani-writers-forum RHFWF-173984973194167/?refid=52&red=opera_speed_dial_&yn=H-R

*Email* [email protected]

*Facebook* www.Facebook.com/REALHAUSAFULANIWRITERSFORUM.COM

                 71_72

Ina matukar Godiya ga masoyan wannan novel, ina jin dad'in yadda kuke bani goyan baya wannan shafin naku ne duk masoyin CAPTAIN SADIQ*

      Ko da fatuha ta shiga bedroom wayar tace ta hau ruri dake bedside drawer, cikin fara'a ta d'auka saboda sunan dake maqale a screen din wato Hanan, daukar wayar tayi tare da kallon screen din kasancewar video call ne saman bed ta haye ta  ce, "Hey yan'mata ya kike?
      "lafiya lau, wai yaushe zaki zo gida ne? ina so muje gidan Ammi birthday din Basma ya kusa?
          "a ina za'ayi birthday din? inji fatuha
    "kema kin san ba'a gida za'ayi ba"
    "Chab aikin san halin uncle wallahi ba zai barni naje ba"
     "nifa matsala ta dake kenan wallahi, ke komai uncle komai shi.! shi..!
    "Eh naji din.!
"yanzu dai ki masa dubara sai muje"
       "gaskiya ina tsoran fushinsa kin manta randa muka je birthday din haulat kenan?
       "wallahi ban manta ba ina sane ras,"
     "toh yayi kyau, amma fa zan shigo insha Allah"
     "to shikenan ki gaishe min da angel"
  "tam.! ta katse wayar tare da kwaciyarta tana  tuna kyakyawar  captain sadiq wadda  bata  gajiya  da  tozali  da  ita har  rana  mai  kamar  ta  yau  kankame pillow tare  da  lumshe  ido.

    Kamar yarda suka saba idan suka had'u haka suka dinga zuba hira tare da yin musu, dama sun saba baza su taba rabuwa ba, ba tare da sunyi musu ba, amma duk wannan hirar da suke majeed tunanin fatuha na maqale a ransa cike  da  begen  sake  tozali  da  ita  karo  na  biyu, kiran sallah magrib ne ya tashe su, d'auro alwala sukayi suka wuce masallaci.
        Basu dawo gida ba sai bayan sallah isha, ko da suka dawo majeed bai shiga gidan ba daga waje ya tsaya tare da jan motarsa yana tunanin ta inda zai 6ulo domin  ya  kara  tozali  da  fatu  tattausan murmushi  ya  saki  yana  tuna  kyawuta mai  gusar  da  nutsuwar  wucin  gani, wannan  lokacin  sam  ba  zaiyi  wasa  da  damarsa  ba dan a gaskiya a shirye yake da ya aure ta kota halin kaka.......hmmm tofa..!

    Ko da sadiq ya shigo gidan Mom na zaune a parlour ita da angel suna kallo, kallon parlour sadiq yayi tare da cewa "Angel ina Aunty?
     "tana bedroom Dady" ok yace sannan ya haura sama ko minutes 5 bai yi ba ya dawo parlour tare da wuce wa bedroom din fatuha, zaune take saman bed tana assignment da laptop tana sanye  da rigar bacci dai-dai gwiwa sai gashin kanta data nanad'e sa kamar ganmo.

        Bud'e kofar da akayi ne yasa ta d'aga eye's ball's din ta  saki  tattausan  murmushi ta ture laptop din dake  gabanta  tana qoqarin tashi, harara sadiq ya aika mata, tare da cewa, "Ina car Key's dina?" zuburo baki tayi gaba sadiq  ya  cigaba  da  cewa, "wato kin rai nani ko? shine zan fita kika d'auke min car key's kika boye"
      "sorry uncle, bana so ka fita ne ka sha rana, kuma da ka fita ai da bakon ka bai same ka ba, am sorry.! tasa hannuwata biyu a kunne ta langwabe  kai  ta  ce, "Allah yaba ka  hakuri" matsowa sadiq yayi kusa da ita har tana jin saukar numfashinsa ja mata baki yayi har sai da ta saki yar qara, ta6e baki tayi tana shirin yin kuka cikin  wata  irin  murya can  kasan  makoshi  sadiq  ya  ce, "kul kika min kuka wallahi yau sai kin kwana kina kneeldown, kuma kin san zan iya, bani key's dina," bedside drawer ta bude tare da zaro key's din ta miqa masa tana qoqarin komawa saman bed  jawo hannuta sadiq yayi yana qare mata kallo ba qaramin kyau ta masa ba, lumshe ido yayi tare da ware su a kanta murmushi fatuha ta saki mai cike da sakonni iri-iri wani langwabe kai  sadiq  yayi  yana  binta  da  kallon  qasan  ido  ya  ce, "rufe idanuwan ki kiga wani abu" cikin sauri da zakuwa fatu ta lumshe idanuwanta wani d'an kit ya fido tare da bude kit din ya  ce, "oya bud'e.! wata hadadiyar sarkar gold ce sai  sheki  take da  walwali kallo  daya  zaka  mata  kasan  ba  qaramar  sarqa  ba  ce  bude  baki  fatu  tayi  tana  kallon  sarqar wani irin ihu fatuha tasaki  tare da rungume sadiq, shima rungume ta yayi tare da kai hannu saman gashin kanta ya warware daurin data masa ya  kwanto  gadon  bayanta, cikin cool voice sadiq  ya ce can  kasan  maqoshi yarda  sai  fatu  zata iya  jinsa  cikin  rad'a ya  ce, "Gashin ki yafi kyau a haka..! smile tayi tare da dagowa daga fafad'an qirjinsa da murmushinta  mai  qara  mata  kyau ta juya masa baya tana facing din dressing mirror tare da matsar da gashin kanta gefe tana  kallon  sadiq  ta  cikin  mirror a  hankalin ya  kwance  sarqar lumshe  ido  fatu  tayi  tana  jin  yarda  hannu  sadiq  ke  yawo  a  dokin  wuyanta, samata sarkar yayi ya  tsare  ta  da  ido  ya  jin  farin  ciki jin  shuru  yasa fatu  ware  ido  ta  sauke  su  kan  sadiq  daya  daura  kansa  saman  kafadarta,  suna  kallon  juna  ta  cikin  mirror ba qaramin kyau sarkar ta mata ba da  murmushi ta juyo  tare da cewa, "Uncle na gode" murmushi sadiq yayi ya  ce, "nike da godiya fatuha yau kusan shekarana uku bana tunani, bana zuwa asibiti kin  zamar min  wani  bangare  na  rayuwata" murmushi ta saki tare da fita daga d'akin da  sauri.
       tana Isowa parlour ta fad'a jikin Mom tana  cewa, "Mom kin ga sarkar da uncle ya siya min? murmushi moym tayi irin nasu na manya ta  ce, "amma dai gaskiya mun gode wannan kyau ta haka" lokacin yayi dai-dai da fitowar sadiq daga bedroom din fatuha, angel ce ta turo baki ta ce, "Daddy ni fa☹?" ja mata kumatu yayi tare da fido mata zube na gold ya sa mata murmushi ta saki ta  fada  jikin  sadiq  ta  ce, "love you daddy" tare da yimasa peck Mom  ta  ce, "lallai abin ma yar haka ce kenan? yaran ka kawai ka sani ni kuma ko oho" Mom ta fada, bayan Mom sadiq yaje tare da zuro kansa a wuyanta ya  ce, "sorry Mom next time siyayarki  ce  ke  kad'ai kin ji"  d'an smile Mom  tayi tare  da  shafa  sumar  kan  sadiq shima zagayowa yayi ya zauna sun dad'e suna hira sannan kowa ya wuce bedroom dinsa.

      Bangaran majeed ko cikin farin ciki ya koma gida, ko da umyma ta tanbayesa sai ce mata yayi ya kusa cika mata burin ta, murna ko har ba'a magana ko da ya koma d'akinsa da ya rintse ido fatuha yake gani tana  sakin  murmushinta  mai  tafiya  dashi haka ya dinga juyi saman bed har bacci barawo ya sace shi.

       *Asuba ta gari*
Chapter 42 · 0% Book details