Sashe 46
Captain Sadiq Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Direct part din Sadiq ta wuce a hankali ta murda handle din kofar tare da shigowa cikin sallama zaune sadiq yake saman two sitar da laptop gabansa kallo d'aya zaka masa kasan baya cikin dad'in rai zaka gane akwai abin da ke damunsa fuskar nan nasa babu annuri ya koma captain sadiq na da sak bakin fatu na rawa ta ce, "Uncle..! dogo kai yayi ya kalli fatuha tare da lumshe ido ya kauda kai ya ce, "Just leave me alone" sadiq ya fada a tsiwace tare da tatara takadunsa dake gabansa da laptop dinsa ya shige bedroom tare da buga kofar da karfi, har saida fatu ta razana da yarda ya buga kofar kafarta kasa daukar gangar jikinta yayi saboda tashin hankali na sauyawar sadiq lokaci daya kuka fatuha ta saki tare da fita daga part din da gudu jin ta fita yasa sadiq jingina da kofar bedroom ya lumshe ido har cikin ransa yake jin sautin kukanta, amma kishi ya hana sa saurara mata.
Da gudu ta wuce Mom a parlour ta shige daki saman bed ta fada tare da sakin kuka maicinrai har da shesheqa, kuka taci ta gaji.
Mom dake parlour bin fatuha tayi da kallo tana mamakin mai ya hada su da sadiq haka, koma dai menene ai sun saba zasu shirya ne amma abin mamaki basa kai haka, kauda zancan Mom tayi tare da cigaba da kallon ta.
Duk yinin yau babu wanda yaci abinci cikin su, ban da kuka ba abinda fatu take, shi ko sadiq sai bak'in rai dayake fama da shi.
Iskace mai sanyi da ke ta kad'awa da alama ruwa za'ayi saboda damuna data fara shigowa, qara cida ce kawai ke tashi bakin window sadiq ya tsaya a hankali ruwa ke saukowa kallon ruwan yake yanda yake saukowa da karfi, a wannan karan lumshe ido yayi tare da ware su, ya koma saman bed ya kwanta jikinsa ba dadi.
bangaran fatuha tunda aka fara ruwa ta lullu6e cikin blanket jikinta yayi rau da fever.
Gabaki daya yini yau ba wanda yayi ma wani magana, cikin fatuha da sadiq, horan d'aki sukayi wa kansu ba tare da sun nemi abin sama bakin sallatin su ba, ba wai kuma basu jin yunwar bane a'a abinci ne ba zai samu mahali ba, har bacci ya kwashe su.
Washe gari
Shiryawa yake cikin manyan kayansa kasancewar yau zasu je family meeting, fatuha ce ta fado masa a rai kawar da tunanin yayi dan har yanzu bai huce ba ko yana hucewa sai ya dawo daga meeting.
cikin Isa yake saukowa daga upstairs, lokacin har su Mom sun shirya suna parlour zaune suna jiran fitowar sadiq da fatuha ganin sadiq ya sako yasa Mom cewa, "angel kira Aunty mu wuce.! ko da angel ta shiga d'akin kwance ta samu fatuha qudindine cikin blanket, fitowa tayi da sauri daga bedroom din ta ce, "Grandma Aunty bacci take"
"toh fa! amma ai fatuha bata kai haka tana bacci" shiga d'akin Mom tayi tare da qarasawa wajan bed din fatuha ta ce a hankali, a hankali fatuha ware idanuwan ta da suka yi nauyi saboda tsabar kuka, kallonta Mom tayi ta ce "Mike damun kin fatuha? dafe kai tayi ta ce, "Mom kai nane ke ciwo"
"eyya sorry dama meeting zamu tunda baki jin dad'i ki zauna kawai a gida" to kawai tace tare da shigewa blanket, sannan Mom ta fita ko da ta fita sadiq ta aika ma harara tare da ayana ma ranta idan sun dawo zatayima tufkar hanci.
Katafarin parlour su da aka ware danyi meeting suke zaune, tunda sadiq ya shigo gabansa ke yankewa yana fad'uwa yarasa dalilin hakan addu'a da ke bakinsa ya furta dan samun nutsuwa, duk kuma ya damu da yanayin daya bar fatu yafi tunanin harda hakan ya hanasa nutsuwa, majeed ne ya shigo tare da zama gefen sadiq ya miqa masa hannu suka gaisa dakyar sadiq ke danne zuciyarsa kan majeed da bata hakuri.
Alhaji Babba ne ya shigo sanye da babba riga tasha aiki sai sheqi kayan suke, da sallama ya shigo tare da zama a kujerarsa ta musanman wato kakan su sadiq, Ammi na gefansa na dama sauran jikoki da iyaye na gefe da yan uwa.
Taro ya fara budewa da addu'a sannan ya fara jawabin cikin nutsuwa ya ce, " ina maku barka da zuwa Allah yasa yarda ku ka zo taron nan lafiya mu koma gida lafiya, kuma na ji dadin yarda kuke zuwa wannan taro na qara dankon zuminci kamar yarda kuka sani ko wani lokaci muna samun alherai da yawa bangaran kasuwancin mu ina ma albishir da abubuwa da yawa na farin cikin a wannan shekara mun samu kimanin billioths of naire cikin ribar kasuwancin mu, mun talafawa gidan marayu da asibitoci mun biyawa mutun 30 kujerun maka..! kabara wajan ya dauka tare da hamdallah.
Gyaran murya Alhaji yayi ya ce, "Kuma ga muhimiyar sanawar Majeed ya samu matar da zai aura..! sadiq dake zaune saman kujera gabansa ya qara yankewa ya fadi ras-ras muryar Alhaji babba ce ta dawo masa dodan kunne, "Alhamdulillah mun nema an bamu saboda karamci, ba kowa bace sai yar gidan ibrahim wanda yake ruqo fatuha..! har gidan iyayan ta muje munyi bincike ashe ma akwai sanaya a tsakanin mu kuma sun aminci sun bada haka ya mana dadi matuqa..! wani irin gumi ne ya karyo ma sadiq maitsananin zafi take nan ya fara ji wutarsa na d'aukewa jikinsa rawa ya d'auka jin kalaman Alhaji yake tamkar saukar aradu, wani irin amo kalaman suke masa cikin brain, ba sadiq ba hata Mom sai da ta girgiza da wannan furucin, ita dake qoqarin furta abinda ke ranta sai gashi an masu shigar sauri da karfi kirjinta ke bugawa tana tunanin halin da d'an autanta dilo zai shiga, wata kalmar ya qara jefowa a karo na biyu "sadiq kuma mun yanke shawarar bashi kanwarsa Basma amma da sharadi idan har ya kawo wadda yake so nan da sati daya kamin asa biki to za'a basa dama ya auri wadda yake so, Basma ma kuma ta hakura wannan shine hukuncin dana yanke.! sannan ya kalli baban Basma ya ce, "Alhaji khabiru cika mana taro da addu'a..!
Gabaki d'aya parlour juyawa sadiq yake dakyar ya samu ya miqe, jiri na neman kadasa majeed ban da murna ba abin da yake finally yanzu zai samu fatu shawo kanta kawai ya rage masa, ko ta kan sadiq bai bi ba haka Basma baki har kunne tana ganin shawo kan sadiq ya so ta abu ne mai sauki kamar yarda Umma ta sheda mata.
sadiq ne kadai da Mom basu farin ciki, sai Hanan da tashin hankali ya hanata motsi sanin matsayin da fatu ta aje sadiq.
yana fitowa daga parlour parking space ya nufa cikin sauri ya bale murfin mota ya shiga, da gudu ya fisgi motar ya harba kan titi gudu yake tsulawa kamar zai tashi sama, ko ganin gabansa ba yayi saboda tsanin tashin hankali mara musaltuwa, fatu da majeed abun kamar a mafarki, yana isowa gida ya danna horn da karfi dan sam bai san mai yake ba, bala mai gadi na bude masa geta ya ce "Subhanilillah..! Saboda yadda sadiq ya shigo da motar da mugun gudu kamar zai tashi da bala mai gadi.
ko daidaita parking ya kasa ya bale murfin motar ya fito, cikin sauri ya wuce part dinsa yana shiga ya zame bakin kofa tare da dafe kansa, jijiyar kansa duk ta taso saboda tsabar tashin hankali maganar Alhaji babba na dawo masa, cikin dodan kunne miqewa yayi ya shige bedroom saboda har yanzu bai dai na ganin jiri ba, gani yake kamar kunnasa bai ji dai-dai ba wani irin kuka sadiq ya saki mai tsuma zuciyar mai saurare kneeldown yayi a wurin bakinsa na rawa yana furta, no..! No..! I cant believe abinda kunne na ya ji noo..! fatali da kayan d'akin sadiq yake kamar sabon kamu, duk abinda ya dauka ya wurga sai ya watse ya dawo kasa sai da yayima d'akin fata-fata ya shiga toilet da kayan jikinsa sakar ma kansa shower yayi, maganganun Alhaji babba har yanzu ke masa yawo a brain wata zuciyar ta ce "Wato jiya fatuha tabama majeed izinin turawa gidan su? Dama fatu ba so na take ba? Jikin sadiq na rawa ya furta Kalaman bakinsa hadeye kukan da yake yayi ba shiri ya fito sharkaf ya zauna kasan carpet bai damu da kayan dake jikinsa ba ya takure waje daya.
Bangaran fatuhu ko tunda su Mom suka fita gabanta ke faduwa, ta rasa dalilin haka ta rasa sukunin ta jin an bude kofar d'akin ya sata waigowa Mom ce tsaye bakin kofa murmushi fatuha ta saki wanda iya karshi la66anta ta ce, "Mom har kun dawo da wuri haka? eh tace tana qoqarin danne damuwarta, ta qarasa shigowa zama tayi kusa da fatuha cikin sanyi murya ta ce "Fatuha gobe da safe ki shirya zaki je wudil Baffa nasan ganin ki?" sannan ta tashi ta fita kallo fatuha tabi Mom da shi take nan jikinta ya haubari da tsoro-tsoro ko dai uncle ya kai qarata kauda zancan tayi tasan ma ba zanyi haka ba, amma zuciyarta na cike da tanbayoyi, ganin bata da amsa ta hakura.
Ola sadiq ya kira a waya bugu d'aya zuwa biyu ya dauka, "ina san ganin ka" sadiq ya fada a taqaice.
ko da ola ya zo ganin watsin da akayima dakin sadiq ya tsorata kallon sadiq yayi da magana a bakinsa, ganin fuskar sadiq ba annuri yaja baki ya tsuke, nuni ya masa daya gyara d'akin shi kuma ya shingida saman sofa, yana jin wani quna da suya da zuciyarsa ke masa hawaye daya na bin daya saman fuskarsa kamar ba soja ba,
Gabaki d'aya gidan Alhaji Ibrahim ba wanda ya rintsa, daga angel sai Abba ne kawai suka samu bacci,
bangaran sadiq ban da kukan zuci ba abinda yake, fatuha kuwa tunanin me yasa Baffa ke neman take? ko dai inna ce ta rasu? ba'a son fada mata girgiza kai kawai tayi.
Da gudu ta wuce Mom a parlour ta shige daki saman bed ta fada tare da sakin kuka maicinrai har da shesheqa, kuka taci ta gaji.
Mom dake parlour bin fatuha tayi da kallo tana mamakin mai ya hada su da sadiq haka, koma dai menene ai sun saba zasu shirya ne amma abin mamaki basa kai haka, kauda zancan Mom tayi tare da cigaba da kallon ta.
Duk yinin yau babu wanda yaci abinci cikin su, ban da kuka ba abinda fatu take, shi ko sadiq sai bak'in rai dayake fama da shi.
Iskace mai sanyi da ke ta kad'awa da alama ruwa za'ayi saboda damuna data fara shigowa, qara cida ce kawai ke tashi bakin window sadiq ya tsaya a hankali ruwa ke saukowa kallon ruwan yake yanda yake saukowa da karfi, a wannan karan lumshe ido yayi tare da ware su, ya koma saman bed ya kwanta jikinsa ba dadi.
bangaran fatuha tunda aka fara ruwa ta lullu6e cikin blanket jikinta yayi rau da fever.
Gabaki daya yini yau ba wanda yayi ma wani magana, cikin fatuha da sadiq, horan d'aki sukayi wa kansu ba tare da sun nemi abin sama bakin sallatin su ba, ba wai kuma basu jin yunwar bane a'a abinci ne ba zai samu mahali ba, har bacci ya kwashe su.
Washe gari
Shiryawa yake cikin manyan kayansa kasancewar yau zasu je family meeting, fatuha ce ta fado masa a rai kawar da tunanin yayi dan har yanzu bai huce ba ko yana hucewa sai ya dawo daga meeting.
cikin Isa yake saukowa daga upstairs, lokacin har su Mom sun shirya suna parlour zaune suna jiran fitowar sadiq da fatuha ganin sadiq ya sako yasa Mom cewa, "angel kira Aunty mu wuce.! ko da angel ta shiga d'akin kwance ta samu fatuha qudindine cikin blanket, fitowa tayi da sauri daga bedroom din ta ce, "Grandma Aunty bacci take"
"toh fa! amma ai fatuha bata kai haka tana bacci" shiga d'akin Mom tayi tare da qarasawa wajan bed din fatuha ta ce a hankali, a hankali fatuha ware idanuwan ta da suka yi nauyi saboda tsabar kuka, kallonta Mom tayi ta ce "Mike damun kin fatuha? dafe kai tayi ta ce, "Mom kai nane ke ciwo"
"eyya sorry dama meeting zamu tunda baki jin dad'i ki zauna kawai a gida" to kawai tace tare da shigewa blanket, sannan Mom ta fita ko da ta fita sadiq ta aika ma harara tare da ayana ma ranta idan sun dawo zatayima tufkar hanci.
Katafarin parlour su da aka ware danyi meeting suke zaune, tunda sadiq ya shigo gabansa ke yankewa yana fad'uwa yarasa dalilin hakan addu'a da ke bakinsa ya furta dan samun nutsuwa, duk kuma ya damu da yanayin daya bar fatu yafi tunanin harda hakan ya hanasa nutsuwa, majeed ne ya shigo tare da zama gefen sadiq ya miqa masa hannu suka gaisa dakyar sadiq ke danne zuciyarsa kan majeed da bata hakuri.
Alhaji Babba ne ya shigo sanye da babba riga tasha aiki sai sheqi kayan suke, da sallama ya shigo tare da zama a kujerarsa ta musanman wato kakan su sadiq, Ammi na gefansa na dama sauran jikoki da iyaye na gefe da yan uwa.
Taro ya fara budewa da addu'a sannan ya fara jawabin cikin nutsuwa ya ce, " ina maku barka da zuwa Allah yasa yarda ku ka zo taron nan lafiya mu koma gida lafiya, kuma na ji dadin yarda kuke zuwa wannan taro na qara dankon zuminci kamar yarda kuka sani ko wani lokaci muna samun alherai da yawa bangaran kasuwancin mu ina ma albishir da abubuwa da yawa na farin cikin a wannan shekara mun samu kimanin billioths of naire cikin ribar kasuwancin mu, mun talafawa gidan marayu da asibitoci mun biyawa mutun 30 kujerun maka..! kabara wajan ya dauka tare da hamdallah.
Gyaran murya Alhaji yayi ya ce, "Kuma ga muhimiyar sanawar Majeed ya samu matar da zai aura..! sadiq dake zaune saman kujera gabansa ya qara yankewa ya fadi ras-ras muryar Alhaji babba ce ta dawo masa dodan kunne, "Alhamdulillah mun nema an bamu saboda karamci, ba kowa bace sai yar gidan ibrahim wanda yake ruqo fatuha..! har gidan iyayan ta muje munyi bincike ashe ma akwai sanaya a tsakanin mu kuma sun aminci sun bada haka ya mana dadi matuqa..! wani irin gumi ne ya karyo ma sadiq maitsananin zafi take nan ya fara ji wutarsa na d'aukewa jikinsa rawa ya d'auka jin kalaman Alhaji yake tamkar saukar aradu, wani irin amo kalaman suke masa cikin brain, ba sadiq ba hata Mom sai da ta girgiza da wannan furucin, ita dake qoqarin furta abinda ke ranta sai gashi an masu shigar sauri da karfi kirjinta ke bugawa tana tunanin halin da d'an autanta dilo zai shiga, wata kalmar ya qara jefowa a karo na biyu "sadiq kuma mun yanke shawarar bashi kanwarsa Basma amma da sharadi idan har ya kawo wadda yake so nan da sati daya kamin asa biki to za'a basa dama ya auri wadda yake so, Basma ma kuma ta hakura wannan shine hukuncin dana yanke.! sannan ya kalli baban Basma ya ce, "Alhaji khabiru cika mana taro da addu'a..!
Gabaki d'aya parlour juyawa sadiq yake dakyar ya samu ya miqe, jiri na neman kadasa majeed ban da murna ba abin da yake finally yanzu zai samu fatu shawo kanta kawai ya rage masa, ko ta kan sadiq bai bi ba haka Basma baki har kunne tana ganin shawo kan sadiq ya so ta abu ne mai sauki kamar yarda Umma ta sheda mata.
sadiq ne kadai da Mom basu farin ciki, sai Hanan da tashin hankali ya hanata motsi sanin matsayin da fatu ta aje sadiq.
yana fitowa daga parlour parking space ya nufa cikin sauri ya bale murfin mota ya shiga, da gudu ya fisgi motar ya harba kan titi gudu yake tsulawa kamar zai tashi sama, ko ganin gabansa ba yayi saboda tsanin tashin hankali mara musaltuwa, fatu da majeed abun kamar a mafarki, yana isowa gida ya danna horn da karfi dan sam bai san mai yake ba, bala mai gadi na bude masa geta ya ce "Subhanilillah..! Saboda yadda sadiq ya shigo da motar da mugun gudu kamar zai tashi da bala mai gadi.
ko daidaita parking ya kasa ya bale murfin motar ya fito, cikin sauri ya wuce part dinsa yana shiga ya zame bakin kofa tare da dafe kansa, jijiyar kansa duk ta taso saboda tsabar tashin hankali maganar Alhaji babba na dawo masa, cikin dodan kunne miqewa yayi ya shige bedroom saboda har yanzu bai dai na ganin jiri ba, gani yake kamar kunnasa bai ji dai-dai ba wani irin kuka sadiq ya saki mai tsuma zuciyar mai saurare kneeldown yayi a wurin bakinsa na rawa yana furta, no..! No..! I cant believe abinda kunne na ya ji noo..! fatali da kayan d'akin sadiq yake kamar sabon kamu, duk abinda ya dauka ya wurga sai ya watse ya dawo kasa sai da yayima d'akin fata-fata ya shiga toilet da kayan jikinsa sakar ma kansa shower yayi, maganganun Alhaji babba har yanzu ke masa yawo a brain wata zuciyar ta ce "Wato jiya fatuha tabama majeed izinin turawa gidan su? Dama fatu ba so na take ba? Jikin sadiq na rawa ya furta Kalaman bakinsa hadeye kukan da yake yayi ba shiri ya fito sharkaf ya zauna kasan carpet bai damu da kayan dake jikinsa ba ya takure waje daya.
Bangaran fatuhu ko tunda su Mom suka fita gabanta ke faduwa, ta rasa dalilin haka ta rasa sukunin ta jin an bude kofar d'akin ya sata waigowa Mom ce tsaye bakin kofa murmushi fatuha ta saki wanda iya karshi la66anta ta ce, "Mom har kun dawo da wuri haka? eh tace tana qoqarin danne damuwarta, ta qarasa shigowa zama tayi kusa da fatuha cikin sanyi murya ta ce "Fatuha gobe da safe ki shirya zaki je wudil Baffa nasan ganin ki?" sannan ta tashi ta fita kallo fatuha tabi Mom da shi take nan jikinta ya haubari da tsoro-tsoro ko dai uncle ya kai qarata kauda zancan tayi tasan ma ba zanyi haka ba, amma zuciyarta na cike da tanbayoyi, ganin bata da amsa ta hakura.
Ola sadiq ya kira a waya bugu d'aya zuwa biyu ya dauka, "ina san ganin ka" sadiq ya fada a taqaice.
ko da ola ya zo ganin watsin da akayima dakin sadiq ya tsorata kallon sadiq yayi da magana a bakinsa, ganin fuskar sadiq ba annuri yaja baki ya tsuke, nuni ya masa daya gyara d'akin shi kuma ya shingida saman sofa, yana jin wani quna da suya da zuciyarsa ke masa hawaye daya na bin daya saman fuskarsa kamar ba soja ba,
Gabaki d'aya gidan Alhaji Ibrahim ba wanda ya rintsa, daga angel sai Abba ne kawai suka samu bacci,
bangaran sadiq ban da kukan zuci ba abinda yake, fatuha kuwa tunanin me yasa Baffa ke neman take? ko dai inna ce ta rasu? ba'a son fada mata girgiza kai kawai tayi.