Sashe 96
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da hannu yayi mata nuni da ta tashi ta fice domin ya lura bacin rai kawai take son kara masa. Sululu a tashi ta juya ta fara tafiya tana yi tana waigensa shi kuma yana tsaye bakin kofar yana kallonta har sai ta sauka. Dinning ta dawo ta zauna tana kuka domin jin busar sarewar da ta ji Ameer yana yi tana son ta sake jin irinsa kuma tana son ta yi masa tambayoyi akai idan ma bata masa tambaya ba zata so rumgumarsa ta san komai. Tana tsaka da matsar kwalla mai goge mata uniform ya danna door bell din kofar, sai ta gwada yin karanbanin budewa domin bata taba mata gwada budewa wani kofa ba, ko da yi knocked din kofar sai dai ta yi ta kallo ko ta fadawa wani an taba kofa a zo a bude amman ita ba zata bude ba. Sai dai yau yadda ta ga Ummi na yi idan zata bude kofar haka ta yi har ta bude.
“Hajiya Waira yau ke ce da bude kofa?”
Cewar Haruna yana rike da uniform dinta da ya goge hannunsa. Kallonsa kawai take kamar wata marar wayo bata ce masa komai ba, sai yayi murmushi ya mike mata kayan.
“Gashi an goge, kuma malaminki ya iso tun dazun yana jiranki”
Da zumudi ta karbi kayan bata ko iya kaisu dakinta ba ta aje su akan kujera ta nufi dinning ta dauki jakarta da kayan karatunta ta fice da sauri. Kamin ta isa inda yake har da hadawa da gudu, sai dai yanayin yadda ta yi arba da fuskarsa ya katse duk wani hanzarinta. Zaunawa tai tana kallon yanayinsa da alama dai kam yau ransa a bace yake matuka.
“Good Evening”
Ta fada tana kallonsa sai ya amsa mata ba tare da ya kalleta ba, a ka'ida idan zai mata darasi na gaba sai ya yi mata tambayoyi akan darasin da aka yi na baya, sai dai be yi mata tambaya ko daya ba ya cigaba da dora mata daga inda ya tsaya a kwana ukun da suka wuce. Sakancewarta mai fahimta ta maida hankali sosai akan darasin har aka yi aka gama. Yana kokarin maida kayan da yayi mata karatu da su a jakarsa ta kalleshi.
“Wani ya bata maka rai yau ko Uncle”
Ba tare da ya kalleta ba ya amsa mata.
“Baki marmarin gidanku ne? Baki kewar garinki da mutanenki ne? Akwai abun da yake burgeki a nan?”
Ta sauke kai kasa tana taba littafin dake gabanta.
“Ina yi, amman....”
Ta kasa karasawa bata son ta fada masa cewar tsoron komawa take. Sai kawai ta saka hannu ta share hawayen da suka cika idonta.
“Abubuwa da yawa suna burge ni a nan”
Ta dago ta kalleshi.
“Kamar rayuwarsu, yadda suke mu'amala ababen hawansu, yadda uwa take kula da yayanta, yadda suke rayuwa a gidan nan, yarensu, da kuma yadda zuciyarsu take da son mutane da nuna kauna ga kowa, ni ba jininsu ba, ba yar garin ba amman Ummi ta nuna min kulawa da soyayya, kamar a garinmu idan ba jininmu basa son kowa basa barin kowa ya zauna, basa maraba da kowa, basa yarda su koyawa kowa yarensu”
Ya tsayar da abun da yake ya kalleta.
“Ashe kenan a garinku wani be isa ya auri jininku ba? Haka ne?”
Ta daga mishi kai.
“Toh sai ki kiyaye dokokinku, ina kara jaddada miki, karki kuskure watsarda al'adarki da addininki saboda na wasu, su ma suna nunawa mutum kauna ne kawai idan be shiga a cikin addininsu ba, da zarar kin jefar da addininki kin shiga na su, a nan za su canja miki har sai kin tsorata da lamarinsu”
“Kai ba addininsu kake yi ba?”
Ya kalli kansa domin shigar musulunci ce kuma shigar bahaushe a jikinsa kamar yadda fuskarsa take da gemu da tsaje.
“Addini mu daya da su, shiyasa nake baki labarin abun da baki sani ba, saboda ina tausayinki, mu muna boye hallayarmu ne har sai idan mutum ya bar addininsa ya shiga da mu. Ke wai baki tunanin komawa garinku ne?”
Ta girgiza kai alamar aa bata so.
“Wata kila zuwa yanzu, sun shiryar karbarki sun shirya yafe abun da kika yi”
Ta mike tsaye tana kallonsa.
“Ya aka yi kasan sun shirya karbata? Waya fada maka guduwa na yi?”
Yayi yar siririyar dariyar da zata batar da tunaninta.
“Waira, ni fa ba yaro ba ne ina fahimtar komai, ko da baki fada min ba na fahimci hakan ne ta yanayin maganarki da kuma fuskarki kana da mu'alamarki, ni mai matukar kaunar farincikinki ne ƴata”
Ta kasa natsuwa da kalamansa, ta san gaskiya ya fada yayi yata da bakwai da ita, amman yadda ya fadi wasu abubuwan akanta a yanzu ya saka ta tunani.
“Me yasa baka zo jiya ba”
“An yi mutuwa ai”
“Waya fada maka?”
“Na zo na tararda gidan a cike da mutane, na tambaya sai aka fada min mutuwa aka yi”
Ta saka littafanta a muhalinsu ta dauki jakarta ta juya ba tare da tace komai ba. Sai ya kirata
“Waira”
Ta juyo ta kalleshi.
“Karki da al'ummarki, karki yada al'adarki, karki manta da mutanen da suke ta fafuka akanki, memory ki na kurciya ya zauna a kanki, rayuwar da kike a garinku tana da dadi fiye da nan”
Kasa ce masa komai ta yi ban da ido data sakar masa har ya dauki jakarsa ta karatun ya nufi gate yana dingishi kamar gurgu.
9:23pm
Ummi ta aje kofin shayi biyu a gaban Abiey, ma farkon ta fara dauka ta mikawa Abiey sannan ta dauki dayan ta mikawa Dr Zainab dake zaune a falonsa.
“Aa ku sha tea ai sai ku, ni idan kin ga na sha tea safiya ce zan yi breakfast”
Ummi ta zauna rike da kofin tana kallon Abiey da ke bata umarni babu wasa a maganarsa haka ma a fuskarsa.
“Wannan ya zama na karshe da zaki sake dafa min wani abu, na san aiki zai yi ma Hanne yawa dan haka na yanke shawarar zan karo wasu masu aiki”
“Ciwona ba zai hana ni yin komai ba ranka ya dade, dan abun da nake dafa maka ai ba wani abun wahalar ba ne”
“Ba shawararki nake nema ba, hukunci ne da na riga na yanke, kuma idan abubuwa sun dan laba zamu fita waje a duba ki a can hankali zai fi kwanciya kuma zan fi samun gamsuwa idan a can ne, saboda suna da kayan aiki masu kyau”
Dr Zainab ta tari numfashinsa.
“Yanzu ma yake min maganar rage wasu ayukan ma office, saboda ya samu time din zama a gida kuma na yaba da hakan, daman ina tunanin lokaci yayi da ya kamata ace ya sauwake kansa wasu abubuwa ya huta”
“Duk saboda ni? Haba dan Allah karku sauya rayuwarku saboda wannan, ba abun mamaki ba ne Allah ya bani lafiya mai daurewa, wata kila ma sai duk kun rigani mutuwa”
Dr ta yi murmushi tana zolayar Ummi.
“Ban ji bakinki gashi ina son na tafi Kano jibi idan Allah ya kai mu”
“Jibi kuma?”
“Eh tun da na zo ina nan Abuja, ai ya kamata na leka gida na ga yan'uwa da iyaye, jibi idan Allah ya kai mu zan tafi Kano, Jabir ma na ji yana zancen tafiyar gobe ban sani ba ko ya fasa”
“Zaku kara mana kewa Auntie”
“Toh ya za'ayi abun da ya zama dole ai dole ayi shi, daman bayan taro sai raguwa, amman dai ina bada shawarar ku sake bincika yan'uwan yarinyar Waira take ko Wara? Saboda akwai rai akwai mutuwa”
Abiey ya kurba tea ya aje ya dauko wani zancen domin baya son maganar da Dr Zainab ta yi ta Waira.
“Sauban ma yace min gobe zai koma, amman kamin ya tafi zai sake dawowa”
“Yayi kokari ai sosai Allah dai ya bar zumunci, kun zama yan'uwan kai da shi”
Cewar Dr Zainab kamin ta kalli Ummi dake fadin.
“Waira tana son zama da mu Auntie, kuma ta fada mana matsalarta, ko ba komai tana rage min kewar Nimra, idan aka dauketa zan yi kewa sosai kuma ita ma ba asan halin da zata fada ba”
“Zamu yi wannan maganar daga baya, for now yarinyar tana tare da ke, karki saka damuwa a ranki”
Yadda Abiey ya mika hannu ya dafa kafadar Ummi yana bata magana ya matukar burge Dr Zainab, hakan ha tabbatar mata har yanzu kanenta yana bawa matarsa kulawa. Ummi ta mike tsaye rike da tea
“Bari na baku guri”
“Okay”
Abiey ya amsa yana binta da kallo ransa na ƙuna,a yanzu ta fi zame masa tashi hankali fiye da mutuwar Nimra domin ita dai ya san ta tafi kenan, tsabanin Ummi da ciwo ke tare da ita. Waira na ganin Ummi ta mike tsaye ta nufi Ummi tana fadin.
“Ummi zaki kira min Sulem ko Ameer please?”
“Ba ni da number Shuraim, Namra ce mai number sa, Ameer kuma idan na kira na san ba zai daga ba”
“Zai daga Ummi please ki kirashi”
“Toh kai wannan Kitchen sai ki dawo na kira shi”
Ta karbi tea ta nufi hanyar kitchen, tana shiga ta samu Maleek tsaye yana sakawa kansa kankara. Kallo daya ta yi masa ta dauke kai ta nufi kusa da inda hake ta aje ta dauki abu ya rufe sannan ta juyo. Samun kansa yayi da binta da kallo, ya sani da a da ne sai ta fada masa abun da ya kawo ta kitchen din sannan ta yi dakon jiran umarnisa kamin ta aje. Sai dai a yanzu bata yi ko ďaya ba, hakan kuma sai ya ji kamar dan dame shi, fushi take da shi? Or ranta ne a bace? Be raba ďayan biyu ba aje kankarar ya fito daga kitchen din, yana daf da ficewa falon ya ji Ummi na fadin.
“Shiga ďakina ki dauko wayar sai a kira shi”
[7/8, 5:19 PM] My S Line: 50
Yana rike da wani littafi na turanci yana dubawa kanwarsa Fiyya ta turo kofar dakin a hankali ta shigo.
“Ya Ameer”
“Favorite”
Ta fada ba tareda ya dago ya kalleta ba. Sai ta zauna kusa da shi tana leka abun da yake dubawa, a lokacin ya kalleta.
“Wani abu kike so?”
“Ya Ameer duk ka canja, kusan three days kullum kana daki”
“Hajiya Waira yau ke ce da bude kofa?”
Cewar Haruna yana rike da uniform dinta da ya goge hannunsa. Kallonsa kawai take kamar wata marar wayo bata ce masa komai ba, sai yayi murmushi ya mike mata kayan.
“Gashi an goge, kuma malaminki ya iso tun dazun yana jiranki”
Da zumudi ta karbi kayan bata ko iya kaisu dakinta ba ta aje su akan kujera ta nufi dinning ta dauki jakarta da kayan karatunta ta fice da sauri. Kamin ta isa inda yake har da hadawa da gudu, sai dai yanayin yadda ta yi arba da fuskarsa ya katse duk wani hanzarinta. Zaunawa tai tana kallon yanayinsa da alama dai kam yau ransa a bace yake matuka.
“Good Evening”
Ta fada tana kallonsa sai ya amsa mata ba tare da ya kalleta ba, a ka'ida idan zai mata darasi na gaba sai ya yi mata tambayoyi akan darasin da aka yi na baya, sai dai be yi mata tambaya ko daya ba ya cigaba da dora mata daga inda ya tsaya a kwana ukun da suka wuce. Sakancewarta mai fahimta ta maida hankali sosai akan darasin har aka yi aka gama. Yana kokarin maida kayan da yayi mata karatu da su a jakarsa ta kalleshi.
“Wani ya bata maka rai yau ko Uncle”
Ba tare da ya kalleta ba ya amsa mata.
“Baki marmarin gidanku ne? Baki kewar garinki da mutanenki ne? Akwai abun da yake burgeki a nan?”
Ta sauke kai kasa tana taba littafin dake gabanta.
“Ina yi, amman....”
Ta kasa karasawa bata son ta fada masa cewar tsoron komawa take. Sai kawai ta saka hannu ta share hawayen da suka cika idonta.
“Abubuwa da yawa suna burge ni a nan”
Ta dago ta kalleshi.
“Kamar rayuwarsu, yadda suke mu'amala ababen hawansu, yadda uwa take kula da yayanta, yadda suke rayuwa a gidan nan, yarensu, da kuma yadda zuciyarsu take da son mutane da nuna kauna ga kowa, ni ba jininsu ba, ba yar garin ba amman Ummi ta nuna min kulawa da soyayya, kamar a garinmu idan ba jininmu basa son kowa basa barin kowa ya zauna, basa maraba da kowa, basa yarda su koyawa kowa yarensu”
Ya tsayar da abun da yake ya kalleta.
“Ashe kenan a garinku wani be isa ya auri jininku ba? Haka ne?”
Ta daga mishi kai.
“Toh sai ki kiyaye dokokinku, ina kara jaddada miki, karki kuskure watsarda al'adarki da addininki saboda na wasu, su ma suna nunawa mutum kauna ne kawai idan be shiga a cikin addininsu ba, da zarar kin jefar da addininki kin shiga na su, a nan za su canja miki har sai kin tsorata da lamarinsu”
“Kai ba addininsu kake yi ba?”
Ya kalli kansa domin shigar musulunci ce kuma shigar bahaushe a jikinsa kamar yadda fuskarsa take da gemu da tsaje.
“Addini mu daya da su, shiyasa nake baki labarin abun da baki sani ba, saboda ina tausayinki, mu muna boye hallayarmu ne har sai idan mutum ya bar addininsa ya shiga da mu. Ke wai baki tunanin komawa garinku ne?”
Ta girgiza kai alamar aa bata so.
“Wata kila zuwa yanzu, sun shiryar karbarki sun shirya yafe abun da kika yi”
Ta mike tsaye tana kallonsa.
“Ya aka yi kasan sun shirya karbata? Waya fada maka guduwa na yi?”
Yayi yar siririyar dariyar da zata batar da tunaninta.
“Waira, ni fa ba yaro ba ne ina fahimtar komai, ko da baki fada min ba na fahimci hakan ne ta yanayin maganarki da kuma fuskarki kana da mu'alamarki, ni mai matukar kaunar farincikinki ne ƴata”
Ta kasa natsuwa da kalamansa, ta san gaskiya ya fada yayi yata da bakwai da ita, amman yadda ya fadi wasu abubuwan akanta a yanzu ya saka ta tunani.
“Me yasa baka zo jiya ba”
“An yi mutuwa ai”
“Waya fada maka?”
“Na zo na tararda gidan a cike da mutane, na tambaya sai aka fada min mutuwa aka yi”
Ta saka littafanta a muhalinsu ta dauki jakarta ta juya ba tare da tace komai ba. Sai ya kirata
“Waira”
Ta juyo ta kalleshi.
“Karki da al'ummarki, karki yada al'adarki, karki manta da mutanen da suke ta fafuka akanki, memory ki na kurciya ya zauna a kanki, rayuwar da kike a garinku tana da dadi fiye da nan”
Kasa ce masa komai ta yi ban da ido data sakar masa har ya dauki jakarsa ta karatun ya nufi gate yana dingishi kamar gurgu.
9:23pm
Ummi ta aje kofin shayi biyu a gaban Abiey, ma farkon ta fara dauka ta mikawa Abiey sannan ta dauki dayan ta mikawa Dr Zainab dake zaune a falonsa.
“Aa ku sha tea ai sai ku, ni idan kin ga na sha tea safiya ce zan yi breakfast”
Ummi ta zauna rike da kofin tana kallon Abiey da ke bata umarni babu wasa a maganarsa haka ma a fuskarsa.
“Wannan ya zama na karshe da zaki sake dafa min wani abu, na san aiki zai yi ma Hanne yawa dan haka na yanke shawarar zan karo wasu masu aiki”
“Ciwona ba zai hana ni yin komai ba ranka ya dade, dan abun da nake dafa maka ai ba wani abun wahalar ba ne”
“Ba shawararki nake nema ba, hukunci ne da na riga na yanke, kuma idan abubuwa sun dan laba zamu fita waje a duba ki a can hankali zai fi kwanciya kuma zan fi samun gamsuwa idan a can ne, saboda suna da kayan aiki masu kyau”
Dr Zainab ta tari numfashinsa.
“Yanzu ma yake min maganar rage wasu ayukan ma office, saboda ya samu time din zama a gida kuma na yaba da hakan, daman ina tunanin lokaci yayi da ya kamata ace ya sauwake kansa wasu abubuwa ya huta”
“Duk saboda ni? Haba dan Allah karku sauya rayuwarku saboda wannan, ba abun mamaki ba ne Allah ya bani lafiya mai daurewa, wata kila ma sai duk kun rigani mutuwa”
Dr ta yi murmushi tana zolayar Ummi.
“Ban ji bakinki gashi ina son na tafi Kano jibi idan Allah ya kai mu”
“Jibi kuma?”
“Eh tun da na zo ina nan Abuja, ai ya kamata na leka gida na ga yan'uwa da iyaye, jibi idan Allah ya kai mu zan tafi Kano, Jabir ma na ji yana zancen tafiyar gobe ban sani ba ko ya fasa”
“Zaku kara mana kewa Auntie”
“Toh ya za'ayi abun da ya zama dole ai dole ayi shi, daman bayan taro sai raguwa, amman dai ina bada shawarar ku sake bincika yan'uwan yarinyar Waira take ko Wara? Saboda akwai rai akwai mutuwa”
Abiey ya kurba tea ya aje ya dauko wani zancen domin baya son maganar da Dr Zainab ta yi ta Waira.
“Sauban ma yace min gobe zai koma, amman kamin ya tafi zai sake dawowa”
“Yayi kokari ai sosai Allah dai ya bar zumunci, kun zama yan'uwan kai da shi”
Cewar Dr Zainab kamin ta kalli Ummi dake fadin.
“Waira tana son zama da mu Auntie, kuma ta fada mana matsalarta, ko ba komai tana rage min kewar Nimra, idan aka dauketa zan yi kewa sosai kuma ita ma ba asan halin da zata fada ba”
“Zamu yi wannan maganar daga baya, for now yarinyar tana tare da ke, karki saka damuwa a ranki”
Yadda Abiey ya mika hannu ya dafa kafadar Ummi yana bata magana ya matukar burge Dr Zainab, hakan ha tabbatar mata har yanzu kanenta yana bawa matarsa kulawa. Ummi ta mike tsaye rike da tea
“Bari na baku guri”
“Okay”
Abiey ya amsa yana binta da kallo ransa na ƙuna,a yanzu ta fi zame masa tashi hankali fiye da mutuwar Nimra domin ita dai ya san ta tafi kenan, tsabanin Ummi da ciwo ke tare da ita. Waira na ganin Ummi ta mike tsaye ta nufi Ummi tana fadin.
“Ummi zaki kira min Sulem ko Ameer please?”
“Ba ni da number Shuraim, Namra ce mai number sa, Ameer kuma idan na kira na san ba zai daga ba”
“Zai daga Ummi please ki kirashi”
“Toh kai wannan Kitchen sai ki dawo na kira shi”
Ta karbi tea ta nufi hanyar kitchen, tana shiga ta samu Maleek tsaye yana sakawa kansa kankara. Kallo daya ta yi masa ta dauke kai ta nufi kusa da inda hake ta aje ta dauki abu ya rufe sannan ta juyo. Samun kansa yayi da binta da kallo, ya sani da a da ne sai ta fada masa abun da ya kawo ta kitchen din sannan ta yi dakon jiran umarnisa kamin ta aje. Sai dai a yanzu bata yi ko ďaya ba, hakan kuma sai ya ji kamar dan dame shi, fushi take da shi? Or ranta ne a bace? Be raba ďayan biyu ba aje kankarar ya fito daga kitchen din, yana daf da ficewa falon ya ji Ummi na fadin.
“Shiga ďakina ki dauko wayar sai a kira shi”
[7/8, 5:19 PM] My S Line: 50
Yana rike da wani littafi na turanci yana dubawa kanwarsa Fiyya ta turo kofar dakin a hankali ta shigo.
“Ya Ameer”
“Favorite”
Ta fada ba tareda ya dago ya kalleta ba. Sai ta zauna kusa da shi tana leka abun da yake dubawa, a lokacin ya kalleta.
“Wani abu kike so?”
“Ya Ameer duk ka canja, kusan three days kullum kana daki”