← Book details Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 107 OF 176

Sashe 107

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“No one will force you, sai dai na miki alkawari matukar ina gidan nan sai rayuwarki ta haskaka zuciyarki ta bude ki karbi gaskiya”

Zancen zama a gidan da yayi ya tuna mata da abun da Ummi ta fada mata, cikin zumudi ta ce.

“Ummi tace zaka zauna a nan da gaske ne? Wai na raka ka zaka dauko kayanka?”

“Yes for, for her. Happy?”

Ta yi tsalle.

“Yes, can I hug you?”

“Da can da kike rumgumata izini kike nema?”

“Toh ai Ya Maleek ne ya ce ba kyau, wai harame ne”

Ta fada a shagwabe tana dan turo baki gaba, kalmar Haram ta kira da Harame domin haka kalmar ta zauna a kanta. Ya sakarwa fuskarta ido babu ko kyaftawa.

“Ke ai yanzu baki san banbancin Haram da Halal ba, hukuncin be hau kanki ba”

Ya rage tsawo tare da mika bakinsa ya sumbanci karan hancinta, yana dagowa motar Maleek na kunno kai cikin gidan, sai da ya kalli motar sannan ya sake maida bakinss ya sumbanci saman fatar idonta dake rufe tun a lokacin da ta ji numfashinsa na kokarin kwaurawa da nata. Jin karar motar ya saka ta bude idon da sauri ta juyo tana kallon motar dake fake saitinsu sai dai nesa da su, hakan kuma be hana ta yi ido hudu da Maleek ba, da ya kasa fitowa motar sai kallonsu yake, yaƙin duniya na uku na shirin haduwa a kirjinsa, yan sojojin zuciyarsa sai kawo makamai suke, jinin dake circulating a a jikinsa yana jefo masa da bomabamai.
[7/17, 6:22 PM] My S Line: 55

Ameer ya kai hannu ya juyo da fuskarta ta fuskance shi, sai ya sakar mata murmushi.

“Waya baki wannan zoben?”

Ya kai hannunsa ya taba zoben wuyanta, ta sauke kai ta kalli zoben.

“Sulem”

“Wane Sulem?”

Bata amsa masa ba ta juya ta kalli Maleek da ya bude mota ya fito idonsa na kansu. Ameer ya sake kai hannu ya juyo da fuskarta.

“Hey kalleni a nan karki sake juyawa, Sulem dan'uwanki ne?”

Ta girgiza kai tsoro na bayyana a fuskarta. Sai ya saka hannu biyu ya tsinka sarkar ba tare da tsayawa ya ji waye Sulem din a gurinta ba.

“Kai waya ce ka tsinka ina so fa”

“Zan siya miki wani, bana son ganinki da abun kowa sai nawa”

Tana mika hannu ta karba sai yayi baya da hannu yana murmushi, kamin ya juyo ya kalli Maleek dake magana yana aje numfashi da karfi.

“What a shame kamar kai? Yaushe ka gama da Nimra kuma ace cikin gidansu kana kokarin yi ma wata? Na yi zaton abubuwan da suka faru sun koya maka darasi, ashe kara maka kawai suka yi”

A take murmushin da fuskarta Ameer ya gushe, Waira ta koya bayan Ameer ta boya ganin Maleek ya tsaya daf inda take tsaye, sai tunaninta ya bata cewar dukanta zai yi.

“Ban zo dan yi rigima da wani ba, ban kira sunan wani ba, dan haka bana gayyatarka a rayuwata, ni ba yaro ba ne kamar kai, ina magana da Waira ne kawai, kuma ina tunanin babu alakata tsakanin Waira da Nimra, dan haka zanen kaddarar kowa ma dabam ne”

“Hakane. Shiyasa ya zama abun dariya da mamaki idan aka ganka da wata, watan ma yarinyar da ka yi ikirarin baka sani ba, baka tsoron hakki zai bibiye rayuwarka? Kissing her ka taba ta ba abun kunya ba ne a gurinka Maleek”

“Ita fa bata san banbancin halal da haram ba, a addininta komai daidai ne? Me kake kokarin karewa game da ita? Kai da na san babu ruwanka da rayuwar mata amman har kake iya magana saboda na taba ta? Miye damuwarka da haka? Ko dai kai ma ka fara rai ne? Na yi tunanin mataccen ne kai ai”

Ameer ya fada sannan ya kama Waira ya dawo da ita gabansa ya rike hannunta.

“Ni da kai muna da alaka da Nimra Ummi ta fada min, amman wannan ajiyata ce, ka daina shiga tsakanin bawa da Ubangidansa”

Yana fadar hakan ya nufi inda ya faka motar Ummi. Maleek ya hade yawu da karfi ya danne numfashinsa da duk wani bacin rai dake kokuwar barin zuciyarsa ya fito fili. Jin kamar ba zai iya jurewa ba ya saka shi juyowa ya kalli Waira dake kokarin shiga motar.

“Waira wuce ki shiga cikin gidan”

Kamar daman can umarnin take jira sai ta a juyo da sauri ta kalleshe ganin babu wasa a fuskarsa ya saka ta bar jikin motar da sauri ta nufi main door din gidan tana gadawa da gudu.

“Aa nonono karka tsallake layi Maleek, ba kamata haka na faruwa tsakaninmu ba, ya kamata ka zama mai tunani mana”

“Matukar ina raye ba zan bari ka lalata rayuwar yarinyar nan ba, tana a gidanmu under my father control”

“To zamu gani idan ka fini gata a gidan...!”

Ameer ya fada sannan ya rufe motar da karfi, ya rufawa Waira baya. Yana shiga cikin falon Waira na sauko da gudu daga stairs tana kuka, bata son fadan da suke akanta, gashi ta shiga ta yi ma Ummi complain bata same ta a dakinta ba.

“Me ya faru?”

Ameer ya tambaya yana jin wani irin tashin hankali a kallon hawayenta da yake. Tsoron zuwa bangaren Abiey take domin bata taba gwadawa ba, ganin kamar basa lasar miya a kwano daya ya saka bata sha'awar bin Ummi a duk lokacin da ta shiga bangaren. Hakan ya sakata ta zauna a saman kujera nesa da inda Ameer yake tsaye

“Ta so mu je”

Ya nufo inda take yana zaunawa sai ta mike tsaye tana kallon kofa.

“Ya Maleek zai iya dukaba”

Juyawa yayi ya kalli kofar a zatonsa ko ta ga Maleek din ne tsaye a gurin, juyowar da zai yi sai yayi arba da Ummi ta fito ta wata kofa da a ina take fitar da mutum ba. Waira ta nufe ta da sauri tana kuka.

“Ummi Ya Maleek zai iya dukana yau ba zai bar ni ba”

“Babu abun da zai miki kwantar da hankalinki, na yi masa magana”

“Baki san me ya faru ba”

Waira zata fada Ummi ta tare numfashinta tana saka hannu ta dago kanta.

“Na sani je gurin mota ki jira Ameer”

“Toh ba zai doke ni ba?”

“Babu mai ikon dukanki a cikinsu je ki jira shi”

Waira ta saki hannu Ummi ta juya ta kalli Ameer dake kallonta sannan ta fice daga falon tana share hawayenta. Ummi ta matso kusa da Ameer dake tsaye yana kallonta ta ce.

“Ba dan ni ba, wata kila ni ba ni da wannan kimar da zaka min alfarma, amman ina rokonka saboda ita Waira dan Allah ku daina rigima kamar kananan yara a kanta kuna daga mata hankali, Waira kamar amana take a gurinmu dan Allah ka kula da ita, bata da gata sai mu bata da dangi bata da kowa sai mu, idan bata ji sanyi a gurinmu ba a gurin waye zata ji?”

“Karki damu da wannan, na san Maleek ya kitsa karya da gaskiya ya fada miki, wata kila ma na fiki son kula da ita a yanzu, ke kina daukarta a ƴa ne, ni kuma ina kallonta a wani natsayi na dabam ne, ni ba zan gidanki dan na daga miki hankali ko iyalinki ba, idan ma baku da bukatata zan iya tafiya...”

Ummi ta kara matsowa kusa da shi tana girgiza masa kai da sauri.

“Aa nan din ma gidanku ne, sai dai ka yi kora ba wai a koreka ba, kawai ina damuwa da Waira ne ka yi hakuri”

Ba ce mata komai ba ya juya ya fice daga falon, windows ta nufa tana leken motarta, ta saka hannu ta rike curtains din idonta na bin motar da kallo har sai da har ya bar gurin da idonta suke iya gani. Fitar Ameer da minti biyar Maleek ya shigo falon ta kofar da Ummi ta fito dazun, wato kofar dake sada mutum da part din Abiey.

“Ya fa tafi da ita”

Ummi ta saki curtains din ta juyo ta kalleshi.

“Miye damuwarka da hakan ne Maleek?”

“Amman dai kin san abun da ya faru da Nimra”

“Abun da ya faru da Nimra kamar ya? Fyade yayi mata? Soyayya ce kawai shi ma kuma na tabbatar da ace ya san haka zai faru da ba zai aikata ba, kuma ita ma hanyar mutuwarta ce a haka, ko da ba Ameer ba dole wani zai yi sanadiyar bugawar zuciyarta”

“Idan kuma fansa ya zo dauka fa, zai iya amfani da Waira sabo...”

Wani irin kallo Ummi ta watsa masa da ya saka shi kasa karasa maganar.

“Fansa? Ka taba ganin ďan da ke daukar fansa a gurin uwar ta dauki cikinsa ta yi nakudarsa ta haife shi? Ka taba gani? Me yasa zuciyarka bata raya alheri akan ďa?”

Maleek ya gyara tsayuwarsa a yanzu ya san duk wani abu da zai fadawa Ummi ba lallai ne ta fahimta ba, amman shi a baibai yake kallon abin domin ya fi kowa sanin waye Ameer, ba kamar ita da a yanzu take saninsa ba. Ummi ta nuna shi da yatsa.

“Ka cire idonka akan Ameer, ka kawar da kanka ga barin kallon alakar dake shiga tsakaninsa da Waira, ina son farincikin kowa a cikinku, kuma ina iya karantar abun da ke idon Ameer, na da yakini da tabbacin ba zai taba cutar da Waira ba, Ameer ya canja a yanzu sanin da kai masa a ad ba shi ba ne, dan Allah kar ka bari shaidan yayi tasiri a zuciyarka ya dasa maka kiyayyar dan'uwanka”

“Ni bana kiyayya da Ameer, kawai ina fadar halinsa ne, kuma ke nake tausayi idan Ameer ya aikata abun da baki yi tsammani ba zaki fi kowa shiga damuwa da bakinciki”

“Ba zai aikata ba ina baka wannan tabbacin, ka saka ranka a inuwa domin a yanzu zai dawo da zama a gidan nan ne, dole ne ka dauke idonka daga alakarsa da Waira wata kila alakar da kake tsammani ba itace a gabansa ba”

Ya hade yawu har ta yi kamar zata wuce sai kuma ta dawo ta kalleshi
Chapter 107 · 0% Book details