Sashe 134
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Ameer ya hade yawu ya girgiza kai ya soma magana kamar zai yi kuka.
“Ba zaka iya ba Daddy, wani abu ne da kudi baya siya, kyau ilmin martaba ko isa basa siya, kima mutumci da daraja basa siya”
Daga saman kafardarsa Daddy ya gangaro zuwa kasa ya rika hannunsa.
“Zo mu shiga ciki”
Ameer ya jera tare da Daddy suka shiga cikin gidan, sai da suka isa a inda za su zauna sannan Daddy ya sake hannun Ameer ya zauna a kujerar da ya saba zama.
“Ina iya fahimtar halin da kake ciki Ameer, na san damuwarka na san farincikinka, sai dai wannan karon ka shiga a wata kalar damuwa da ta wuce misali, a yanayin yadda ka jera min abubuwan da na za su iya siyen damuwarka su kawo maka farinciki ba sai na fahimci so ne am I right?”
Ya daga kai ba tare da ya kalli Daddy ba.
“Ya sani yi maka karya Daddy, ya maida ni mahaukaci, ya jefa ni a halin da ban taba mafarkin shiga ba, sanin cewar kai ba mahaifina ba ne, sanin abun da Ummi ta yi, gorin da za ayi min da duk wani abun da zan rasa ko na ji, ba kai yadda nake ji a yanzu da na rasa Waira ba”
“How comes ka rasata? Wane irin sake ka yi har ka rasata? Garin ya?”
“Bata sona Daddy, ta fada min kuma na ga haka a idonta, na karanta a kalamanta wani take so dabam ba ni ba”
Daddy ya tashi daga inda yake zaune ya dawo kusa da Ameer ya zauna ya dafa kafadarsa.
“Ameer kana da kyau da asali da kudi da muruba da kwarjini da farin jini da haiba da cikar zati da siffar da ko wace mace zata so ka, ko da kuwa kai baka furta mata ba ita zata so haka, balle kuma ace har ka furta mata ko da kuwa yar zinarice, kasan abun da na dade ina jira arayuwata? Ganin Ranar da zaka zama mai hankali da sanin ya kamata, ranar aurenka”
“Daddy Yarinyar nan ta wuce duk yadda kake tunani, ita bata duba dayan ababen nan da ka lissafa, kuma ta banban da sauran mata, ina ji Kamar babu wata mace da ta kaita kyau da iya mu'alama, Daddy ta dauke hankalina a komai komai ta yi burge ni take i lie to you Saboda ita amman ban a daura mana au...”
Daddy yayi murmushi yana girgiza masa kai.
“Ba sai ka fada ba, na fahimci karya kake tun a ranar da ka fada min haka, kawai dai na saka maka ido ne, shiyasa ban ce maka komai ba, kuma a yanzu na kara tabbatarwa kana son yarinyar nan sosai”
“Amman ita bata so na Daddy”
“Karamar yarinyar ce fa, ina tunanin kamar Safiyya ma zata girma ta, to miye abun mamaki idan tace bata son namiji kamar kai, ita ai bata san so ba, kuma irin sun fi dadin zama domin kai zaka koya mata sonka da kaunarka hankali kwance”
“How Daddy how? Ita bata fahimta tana so na amman na so na aure ba, kuma barin garin zata yi ta fada min, yanzu ma zuwan da na yi na zo ne saboda tace tana son ta musulumta ta hannunna domin ni na koya mata addinin musulumci har ta fahimceshi”
“Wow ka yi abu mai kyau, wannan ma ai first step ne na jefa kaunarka a zuciyarta, baka bukatar fada da wani dan ka burge mace, baka bukatar mace ta tare maka fada dan kasan tana sonka, Saboda ita mace ba a iya mata, zaka iya abun burgewa kuma ita ta ji be mata ba, wata kila ma shi ne silar batawarku, idan tana sonka tana sonka ne ko da kuwa kai kafi kowa zama rago a cikin garinku, idan kuma bata sonka bata sonka ko da ka fi kowa zama gwarzo a garin. Sai dai ta wani bangaren kana bukatar ka yi Gwarjanta saboda ka nunawa duniya kai gwarzo ne, kuma zaka iya a kowane fanni, karka da bata sonka ko tana sonka. Kai da ka maida hankali gurin bi da ita a yadda take so, ka cigaba da dagewa gurin koya mata addinin. Zan yi magana da Imam na Masjid din mu, sai ya fada mana yadda ya kamata mu yi zuwa gobe zamu gabatar da komai”
Ameer ya mike tsaye
“Okay Daddy”
Har ya fara takawa Daddy ya kirashi.
“Ameer”
Sai ya juyo ya kalli Daddy.
“Kai yanzu mai bukata ne a gurin Allah, bachin dare, ba naka ba ne, aikata sabo da duk wani abun da addinin ya haramta ba na mutumen dake nema a gurin Allah ba ne, ka hana kanka bachi ka yi ta fadawa Allah bukatarka ka kai kukanka a gareshi ka fada masa damuwarka, kuma ban ce ka roki Allah ya baka yarinyar ba, aa ka roki Allah ya baka ita idan ita din alheri ce a gareka ka karkarto da hankalinta izuwa gareka, idan kuma babu alheri a zamanku ya yaye maka damuwarta ya musanya maka da wanda ta fita, kuma ya saka maka natsuwar rashinta da kwanciyar hankali, saboda ta fadi bata sonka ko ta nuna karka ya karya maka guiwa, ita mace kamar hawainiya ce mai canja kala, ka ga tsufan Mommy nan ta ku? Da ace ba ni nake aurenta ba zaka iya zuwa da kalamai da hayyala da dake so a gurin namiji kuma ka kwace min ita ta manta da ni idonta ya rufe ta ce sai karamin yaro irinka, saboda haka karka dauki soyayyar mace a banza tun da har ta nuna tana sonka son aurene kawai bata maka, zata fara maka na haihuwa ma soon”
Ameer ya dawo da sauri yana murmushi ya rumgume Daddy.
“I love you Daddy idan ka raye ban san ya rayuwata zata kasance ba”
“Allah ya maka albarka, je ka samu abun da ka ci ka kwanta da wuri saboda ka samu tashi da dare nima zan taya ka, farincikinka shi ne nawa Ameer”
Tun da Ameer yake a duniya be taba jin kaunar Daddy irin na yau ba, domin shi ne ya fahimci damuwarsa kuma ya dauko hanyar magance masa ita. Be samu cin komai ba Before ya kwanta domin tunanin Waira ba ya barin shi jin yunwa haka ma bachi ko kadan kasa yi yayi, shi dai gani yake kamar idan ya runtse zai farka ne ya ga babu kaunar yar kyakkyawar matashiyar budurwa nan a ransa. Kamin lokacin da zai yi tsayuwar daren yayi duk ya kagu, domin ya san Allah ma ji rokon bawansa ne, kuma matukar ya dage kamar yadda Daddy ya fada masa zai samu biya bukata, walau Waira ta kaunace shi fiye da yadda yake sonta, ko kuma Allah ya musayya masa da wanda ta fita alheri a gareshi.
Haka ya saka shi dagewa yayi ta nafila har sai da ya ji ya yi iya yadda zai iya, sannan ya zauna ya bude al'qur'ane yayi ta karatu, daman dai sani da iya karatun Allah akwai shi a tare da shi, sai dai shashanci da bin hanyar shaida ne ya saka a gaba ya saka ya watsar da wadanda kyakkyawa halayyar da Daddy ya dade yana son gani a tare da shi. Kamin ya gabatar da bukatarsa sai da yayi tuba ga Allah ya daukarwa kansa alkawarin ba zai sake komawa a cikin wacan kazantar da ya taba kasancewa ba, ko da kuwa ya rasa Waira, a yanzu ya kai munzalin da zai san daidai da akasin haka. Lokaci yayi da ya kamata ya natsu ya fuskanci rayuwa domin akwai rayuwa akwai mutuwa at least ya kamata ya zama mutumen kirki kamar yadda Daddy da Umminsa da duk wani masoyinsa na gaske yake son gani.
[8/3, 9:50 PM] My S Line: 70
“Ba zaka iya ba Daddy, wani abu ne da kudi baya siya, kyau ilmin martaba ko isa basa siya, kima mutumci da daraja basa siya”
Daga saman kafardarsa Daddy ya gangaro zuwa kasa ya rika hannunsa.
“Zo mu shiga ciki”
Ameer ya jera tare da Daddy suka shiga cikin gidan, sai da suka isa a inda za su zauna sannan Daddy ya sake hannun Ameer ya zauna a kujerar da ya saba zama.
“Ina iya fahimtar halin da kake ciki Ameer, na san damuwarka na san farincikinka, sai dai wannan karon ka shiga a wata kalar damuwa da ta wuce misali, a yanayin yadda ka jera min abubuwan da na za su iya siyen damuwarka su kawo maka farinciki ba sai na fahimci so ne am I right?”
Ya daga kai ba tare da ya kalli Daddy ba.
“Ya sani yi maka karya Daddy, ya maida ni mahaukaci, ya jefa ni a halin da ban taba mafarkin shiga ba, sanin cewar kai ba mahaifina ba ne, sanin abun da Ummi ta yi, gorin da za ayi min da duk wani abun da zan rasa ko na ji, ba kai yadda nake ji a yanzu da na rasa Waira ba”
“How comes ka rasata? Wane irin sake ka yi har ka rasata? Garin ya?”
“Bata sona Daddy, ta fada min kuma na ga haka a idonta, na karanta a kalamanta wani take so dabam ba ni ba”
Daddy ya tashi daga inda yake zaune ya dawo kusa da Ameer ya zauna ya dafa kafadarsa.
“Ameer kana da kyau da asali da kudi da muruba da kwarjini da farin jini da haiba da cikar zati da siffar da ko wace mace zata so ka, ko da kuwa kai baka furta mata ba ita zata so haka, balle kuma ace har ka furta mata ko da kuwa yar zinarice, kasan abun da na dade ina jira arayuwata? Ganin Ranar da zaka zama mai hankali da sanin ya kamata, ranar aurenka”
“Daddy Yarinyar nan ta wuce duk yadda kake tunani, ita bata duba dayan ababen nan da ka lissafa, kuma ta banban da sauran mata, ina ji Kamar babu wata mace da ta kaita kyau da iya mu'alama, Daddy ta dauke hankalina a komai komai ta yi burge ni take i lie to you Saboda ita amman ban a daura mana au...”
Daddy yayi murmushi yana girgiza masa kai.
“Ba sai ka fada ba, na fahimci karya kake tun a ranar da ka fada min haka, kawai dai na saka maka ido ne, shiyasa ban ce maka komai ba, kuma a yanzu na kara tabbatarwa kana son yarinyar nan sosai”
“Amman ita bata so na Daddy”
“Karamar yarinyar ce fa, ina tunanin kamar Safiyya ma zata girma ta, to miye abun mamaki idan tace bata son namiji kamar kai, ita ai bata san so ba, kuma irin sun fi dadin zama domin kai zaka koya mata sonka da kaunarka hankali kwance”
“How Daddy how? Ita bata fahimta tana so na amman na so na aure ba, kuma barin garin zata yi ta fada min, yanzu ma zuwan da na yi na zo ne saboda tace tana son ta musulumta ta hannunna domin ni na koya mata addinin musulumci har ta fahimceshi”
“Wow ka yi abu mai kyau, wannan ma ai first step ne na jefa kaunarka a zuciyarta, baka bukatar fada da wani dan ka burge mace, baka bukatar mace ta tare maka fada dan kasan tana sonka, Saboda ita mace ba a iya mata, zaka iya abun burgewa kuma ita ta ji be mata ba, wata kila ma shi ne silar batawarku, idan tana sonka tana sonka ne ko da kuwa kai kafi kowa zama rago a cikin garinku, idan kuma bata sonka bata sonka ko da ka fi kowa zama gwarzo a garin. Sai dai ta wani bangaren kana bukatar ka yi Gwarjanta saboda ka nunawa duniya kai gwarzo ne, kuma zaka iya a kowane fanni, karka da bata sonka ko tana sonka. Kai da ka maida hankali gurin bi da ita a yadda take so, ka cigaba da dagewa gurin koya mata addinin. Zan yi magana da Imam na Masjid din mu, sai ya fada mana yadda ya kamata mu yi zuwa gobe zamu gabatar da komai”
Ameer ya mike tsaye
“Okay Daddy”
Har ya fara takawa Daddy ya kirashi.
“Ameer”
Sai ya juyo ya kalli Daddy.
“Kai yanzu mai bukata ne a gurin Allah, bachin dare, ba naka ba ne, aikata sabo da duk wani abun da addinin ya haramta ba na mutumen dake nema a gurin Allah ba ne, ka hana kanka bachi ka yi ta fadawa Allah bukatarka ka kai kukanka a gareshi ka fada masa damuwarka, kuma ban ce ka roki Allah ya baka yarinyar ba, aa ka roki Allah ya baka ita idan ita din alheri ce a gareka ka karkarto da hankalinta izuwa gareka, idan kuma babu alheri a zamanku ya yaye maka damuwarta ya musanya maka da wanda ta fita, kuma ya saka maka natsuwar rashinta da kwanciyar hankali, saboda ta fadi bata sonka ko ta nuna karka ya karya maka guiwa, ita mace kamar hawainiya ce mai canja kala, ka ga tsufan Mommy nan ta ku? Da ace ba ni nake aurenta ba zaka iya zuwa da kalamai da hayyala da dake so a gurin namiji kuma ka kwace min ita ta manta da ni idonta ya rufe ta ce sai karamin yaro irinka, saboda haka karka dauki soyayyar mace a banza tun da har ta nuna tana sonka son aurene kawai bata maka, zata fara maka na haihuwa ma soon”
Ameer ya dawo da sauri yana murmushi ya rumgume Daddy.
“I love you Daddy idan ka raye ban san ya rayuwata zata kasance ba”
“Allah ya maka albarka, je ka samu abun da ka ci ka kwanta da wuri saboda ka samu tashi da dare nima zan taya ka, farincikinka shi ne nawa Ameer”
Tun da Ameer yake a duniya be taba jin kaunar Daddy irin na yau ba, domin shi ne ya fahimci damuwarsa kuma ya dauko hanyar magance masa ita. Be samu cin komai ba Before ya kwanta domin tunanin Waira ba ya barin shi jin yunwa haka ma bachi ko kadan kasa yi yayi, shi dai gani yake kamar idan ya runtse zai farka ne ya ga babu kaunar yar kyakkyawar matashiyar budurwa nan a ransa. Kamin lokacin da zai yi tsayuwar daren yayi duk ya kagu, domin ya san Allah ma ji rokon bawansa ne, kuma matukar ya dage kamar yadda Daddy ya fada masa zai samu biya bukata, walau Waira ta kaunace shi fiye da yadda yake sonta, ko kuma Allah ya musayya masa da wanda ta fita alheri a gareshi.
Haka ya saka shi dagewa yayi ta nafila har sai da ya ji ya yi iya yadda zai iya, sannan ya zauna ya bude al'qur'ane yayi ta karatu, daman dai sani da iya karatun Allah akwai shi a tare da shi, sai dai shashanci da bin hanyar shaida ne ya saka a gaba ya saka ya watsar da wadanda kyakkyawa halayyar da Daddy ya dade yana son gani a tare da shi. Kamin ya gabatar da bukatarsa sai da yayi tuba ga Allah ya daukarwa kansa alkawarin ba zai sake komawa a cikin wacan kazantar da ya taba kasancewa ba, ko da kuwa ya rasa Waira, a yanzu ya kai munzalin da zai san daidai da akasin haka. Lokaci yayi da ya kamata ya natsu ya fuskanci rayuwa domin akwai rayuwa akwai mutuwa at least ya kamata ya zama mutumen kirki kamar yadda Daddy da Umminsa da duk wani masoyinsa na gaske yake son gani.
[8/3, 9:50 PM] My S Line: 70