Sashe 168
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Daga lokacin ne wata sabuwar alaka da shakuwa ta fara shiga tsakanin Humaira da Ameer, ita dai daman kaunar Ameer ta dade ginuwa a zuciyarta, a yanzu kuma sai ta tarairayi barta tana gina masa kaunarta a zuciyarsa. A month later suka shirya har Hajiya da Bahijja suka tafi Kano gurin dangin mahaifin Deen da kuma Hajiya daman ta labarta musu komai a waya, tun a lokacin da abubuwan suka faru, su suka sauka a family house dinsu shi kuma ya sauka gidan Ammynsa wato Hajiya Jamila ba karamin murna ta yi ba ganin Ameer domin Allah ya saka mata kaunarsa ba kadan ba, satinsa biyu a sokoto babu inda be zaga ba gurin yan'uwa da suke kusa kowa mamakin ganinsa suke a nan ma sai da aka samu masu zagin Ummi akan abun da ta aikata, wasu kuma suka ce gobarar titi a jos, domin a familynsu babu mai rufin asiri da arziki da Ameer yake da shi a yanzu wadda har Hajiya da Bahijja suka samu, suna ganin da ace Ummi bata aikata hakan ba da yanzu babu wannan shataletalen arzikin, daman fahimtar kowa dabam wasu na ganin bata kyauta ba, kuma ta dauki alkali wasu kuma na ganin bata yi laifi ba domin bata bar shi a wahala ba. Har gurin dangin mahaifin Humairah sai da Ameer ya je ya gaishesu a matsayin dan'uwanta kuma mai kudirin aurenta, kusan duk inda ya tafi sai ya karar da aljihunsa domin dangin nasa ba wasu masu arziki ba ne, su ma nema suke yi, a nan ya gane Ummi ba karamin taimakon ta yi masa ba na bada shi gurin Mr Bashir ko da be tashi cikin wahala a gurin dangin Deen ba, saboda tana raye ya san ba zai samu kalar gatan da ya samu a yanzu ba, domin Abiey ba zai rike shi ya sakar masa dukiyarsa kamar yadda Mr Bashir yayi ba, ya saka tufafin da yake so idan zai yi tafiya a gari ma sai dai idan ya isa garin ya siye wasu tufafin amman baya tafiya da kaya duk inda zai ji saboda yana jin sun zame masa aiki, idan zai dawo ma ba zai dauko su ba, motar sai wadda ya ga dama yake shiga tsabar gatan da Mr Bashir yayi masa shi taba sanin akwai talauci mai tsanani ba sai da ya hadu da Humairah a yanzu kuma zuwansu gurin dangin mahaifinsa ya fahimci komai. Ta waya Ummi ta hada shi da Yayarta Maryam dake shirin barin kano zuwa duba Ummi, ba karamin sanyi da dadi ya ji ganinta domin tana kama da Ummi sosai ta hada shi da duka yayanta da suka manyata har da iyalansu suka yi exchanging number junan, bata yarda ya bar gidan ba sai da yayi kwana biyu, nasiha sosai ta yi masa ta labarta masa irin soyayyar da Zahra ta yi da Deen kamin rai yayi halinsa, ya nan ya fahimci ita ta bada gudumawa gurin samun lafiyar mahaifinsa a lokacin da ba a haife shi ba, domin ta siyar da kayan dakinta kuma ta yardar a siyar da gidansu na gado a hada da kasonta a nema masa lafiya. Sosai suka yi hira ya saki jikinsa yana jinta kamar Ummi, domin ta yi masa maraba yayanta ma sun nuna masa kauna haka ma Mijinta. A nan ita ma ta kai shi gurin wasu dangin mahaifinsu da kuma na Mahaifiya ya gaisa da mutane da yawa kowa sai mamaki yake idan ya ji cewar dan Zahra ne.
Ba karamin dadin ziyarar Ameer ya ji ba, domin ya gane shi dan dangi ne kauna ta ko'ina, har ya ji kamar kar ya dawo. Tare da su Hajiya ya dawo aka bar Bahijja gurin dangin babanta kasancewar sun zana jarabarwarsu ta karshe kuma ta dade bata zo gida ba, sai da ya dawo Abuja ya ji kamar ba zai iya hakurin har zuwa lokacin da ta diba zata dawo ba, kewarta sosai ta cika masa zuciya suna waya su yi video call amman hakan be wadatar da shi ba. A week later da dawowarsa Daddy ya shirya tare da mutanensa da Ameer din kansa da Maleek suka tafi har Kano suka gaisa da dangin Ameer, kuma ya nema masa auren Humairah a gurin dangin mahaifinta suka ba shi bayan sun nemi izininta kamar yadda Addinin musulunci ya shar'anta. Bayan dawowarsu Mummy ta shiga hada hadar hada kayan lefensa da kuma kayan auren nata yayan uku da Daddy yake son ya hada su ya aurar a tare da Ameer Fiyya ce kawai zata rage a gidan daman kuma ita ce auta.
[8/19, 4:48 PM] 🦋-🦋: 84
Abuja 8:14pm
Maleek ne zaune a kujera system na gabansa yana mug din coffee kuma na gefensa, Nuwaira gaban System din tasa yayi wallpaper da hotonta wanda ya dauka ba tare da saninta ba. Calling ya taba yana fara ringing ta yi picking sai ta yi saurin boye abun da ke hannunta a bayanta tana murmushi.
“My cry cry Baby me kika boye?”
Ta ware masa hannayenta ta nuna masa babu komai.
“Chocolate ne na sani, kullum sai na miki magana kuma sai kin ci ko? Ya kamata ace kin rage cinsa a yanzu Nuwaira baki san yana da illa ba”
“Ku kuka saba min ai na saba, amman zan daina”
“Ina dankwalinki”
Ya saka hannunta ta maida gashinta baya sannn ta duka ta dauko chocolate din ta cigaba da ci tana lashe baki, idonsa be ko'ina sai akan karamin bakinta da take juyawa be kallon wani abu a jikinta ya ji zuciyarsa ta kwadatun da son tabawa ba irin yau, yadda take juya bakin tana leko halshe ta lashe.
“Ya Maleek wai Mama ta ce zamu tafi mu ga Ummi?”
Ya dauki coffee ya sha ya aje.
“Yaushe?”
Ta turo bakin ta tabe shi hakan sai ya kara yi masa kyau.
“Ni na ban sani ba, amman dai haka ta ce min, ta fada maka?”
“Aa amman zan yi magana da ita”
Ta gyara gashinta ta sake dubansa ganin yana kallonta ya saka ta yi murmushi, shi ma tattausan murmushi yayi yana jin wani irin sonta na fisgarsa.
“Me yasa kake son shan wannan coffee ne Ya Maleek? Ba shi da dadi fa”
“Yana da dadi sai idan baki saba ba, da kin gwada sha zaki ji dadinsa”
“Na taba sha ai, lokacin da zaka tafi Airport tare da Abiey kamin ku wuce ka hada shi sai kuma ka shiga dakinka a nan na dauka na sha na ji babu dadi”
Ta karasa tana yamutsa fuska.
“Da wani abun na saka a ciki fa?”
“Ni ina ruwana toh, ai dai na ga kana sha na so na ji me ake ji ne a ciki, a nan ma na ga Mama da mijinta suna sha amman bana sha”
“Kara ki fara sha ma tun yanzu, domin idan muka yi aure dole ki koyi shan shi”
Ta rufe ido tana giggle jin ya ambaci aure, shi ma dariyar yayi ya shafa kansa.
“Ina aka kaiki yau?”
“Gurin dilka kawai sai gyara kafa, matar nan bata da musulunci tana ta murza min jiki kamar zata cire min fata”
“Imani ake cewa”
“Koma yayane dai bata da shi, muguwa ce sosai, ai idan na yi waya da Ummi sai na fada mata ni bana son wannan bakin dilka”
“Ke kadai ake yi ma?”
“Ana yi ma Anty Namra ma, amman ni ai jikina ya fi jin wahala ita bata kuka ni kadai nake yi”
“Saboda ke ai da am bata miki rai kuka kike?”
“Toh dariya zan yi?”
Ta bata ran a take ta turo masa baki ta kawar da fuska ta cikin video call din take son masa kukan shagwaba saboda ya fadi haka.
“Cry cry look at me here”
Ta juyo ta kalleshi ta dauke kai.
“I love you”
Ba karamin dadin ziyarar Ameer ya ji ba, domin ya gane shi dan dangi ne kauna ta ko'ina, har ya ji kamar kar ya dawo. Tare da su Hajiya ya dawo aka bar Bahijja gurin dangin babanta kasancewar sun zana jarabarwarsu ta karshe kuma ta dade bata zo gida ba, sai da ya dawo Abuja ya ji kamar ba zai iya hakurin har zuwa lokacin da ta diba zata dawo ba, kewarta sosai ta cika masa zuciya suna waya su yi video call amman hakan be wadatar da shi ba. A week later da dawowarsa Daddy ya shirya tare da mutanensa da Ameer din kansa da Maleek suka tafi har Kano suka gaisa da dangin Ameer, kuma ya nema masa auren Humairah a gurin dangin mahaifinta suka ba shi bayan sun nemi izininta kamar yadda Addinin musulunci ya shar'anta. Bayan dawowarsu Mummy ta shiga hada hadar hada kayan lefensa da kuma kayan auren nata yayan uku da Daddy yake son ya hada su ya aurar a tare da Ameer Fiyya ce kawai zata rage a gidan daman kuma ita ce auta.
[8/19, 4:48 PM] 🦋-🦋: 84
Abuja 8:14pm
Maleek ne zaune a kujera system na gabansa yana mug din coffee kuma na gefensa, Nuwaira gaban System din tasa yayi wallpaper da hotonta wanda ya dauka ba tare da saninta ba. Calling ya taba yana fara ringing ta yi picking sai ta yi saurin boye abun da ke hannunta a bayanta tana murmushi.
“My cry cry Baby me kika boye?”
Ta ware masa hannayenta ta nuna masa babu komai.
“Chocolate ne na sani, kullum sai na miki magana kuma sai kin ci ko? Ya kamata ace kin rage cinsa a yanzu Nuwaira baki san yana da illa ba”
“Ku kuka saba min ai na saba, amman zan daina”
“Ina dankwalinki”
Ya saka hannunta ta maida gashinta baya sannn ta duka ta dauko chocolate din ta cigaba da ci tana lashe baki, idonsa be ko'ina sai akan karamin bakinta da take juyawa be kallon wani abu a jikinta ya ji zuciyarsa ta kwadatun da son tabawa ba irin yau, yadda take juya bakin tana leko halshe ta lashe.
“Ya Maleek wai Mama ta ce zamu tafi mu ga Ummi?”
Ya dauki coffee ya sha ya aje.
“Yaushe?”
Ta turo bakin ta tabe shi hakan sai ya kara yi masa kyau.
“Ni na ban sani ba, amman dai haka ta ce min, ta fada maka?”
“Aa amman zan yi magana da ita”
Ta gyara gashinta ta sake dubansa ganin yana kallonta ya saka ta yi murmushi, shi ma tattausan murmushi yayi yana jin wani irin sonta na fisgarsa.
“Me yasa kake son shan wannan coffee ne Ya Maleek? Ba shi da dadi fa”
“Yana da dadi sai idan baki saba ba, da kin gwada sha zaki ji dadinsa”
“Na taba sha ai, lokacin da zaka tafi Airport tare da Abiey kamin ku wuce ka hada shi sai kuma ka shiga dakinka a nan na dauka na sha na ji babu dadi”
Ta karasa tana yamutsa fuska.
“Da wani abun na saka a ciki fa?”
“Ni ina ruwana toh, ai dai na ga kana sha na so na ji me ake ji ne a ciki, a nan ma na ga Mama da mijinta suna sha amman bana sha”
“Kara ki fara sha ma tun yanzu, domin idan muka yi aure dole ki koyi shan shi”
Ta rufe ido tana giggle jin ya ambaci aure, shi ma dariyar yayi ya shafa kansa.
“Ina aka kaiki yau?”
“Gurin dilka kawai sai gyara kafa, matar nan bata da musulunci tana ta murza min jiki kamar zata cire min fata”
“Imani ake cewa”
“Koma yayane dai bata da shi, muguwa ce sosai, ai idan na yi waya da Ummi sai na fada mata ni bana son wannan bakin dilka”
“Ke kadai ake yi ma?”
“Ana yi ma Anty Namra ma, amman ni ai jikina ya fi jin wahala ita bata kuka ni kadai nake yi”
“Saboda ke ai da am bata miki rai kuka kike?”
“Toh dariya zan yi?”
Ta bata ran a take ta turo masa baki ta kawar da fuska ta cikin video call din take son masa kukan shagwaba saboda ya fadi haka.
“Cry cry look at me here”
Ta juyo ta kalleshi ta dauke kai.
“I love you”