Sashe 9
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Gaskiyar da ba ki so, dole mu fada miki, kuma karki yarda na sake jin bakinki ya furta cewar baya son kowa?”
Miyewa ta yi sauye bayan fadar haka ta nufi wata karamar kofa dake falon ta bude ta fita tsakar gidan da ko'ina yake tsab, matsawa ta yi kusa da flowers ta mika hannunta tana taba su a hankali, babu ranar da bata tunanin ďanta, babu ranar da zata zauna ta yi hira da yaranta akan rayuwarsu bata tuna da ďanta, damuwarshi ta haifar mata da damuwa da yawa, ta haifar masa da rashin kuzarin iya rike kanta a duk lokacin da ta tuna kamar yadda hawaye suka fara wanke fuskarta, ta kasa cire kanta a damuwa ta kasa daina tunaninsa duk da kasancewar likita ya gargadeta da ta cire damuwa a ranta saboda hawan jinin da take fama da shi. A tsorace ta juyo jin muryar Mahmood yana kiranta. Kamar hoto ya tsaya yana kallonta ganin hawaye a idonta.
“Ummi lafiya?”
Ta taba fuskarta sai ta ji hawayen sa bata san lokacin da suka sauko mata ba, murmushi ta yi ta share hawayen.
“Lafiya kalau, yanzu ka dawo?”
“Eh ni ma dauko Abiey, amman Ummi ba lafiya ba kalli fa kuka kike yi”
“Tunani kawai nake yi, makomar yayana idan bana raye that's...”
Ta karasa wasu hawayen na sauko mata.
“Haba Ummi ki daina kawo wannan abun a ranki please, ba zai taba faruwa ba tare zamu rayuwa In Shaa Allah”
Ya rumgume yana jin wani emotional, he can't imagine his life without her, ta ya za su iya rayuwa.
“Ummi ba zamu iya rayuwa ba idan babu ke, babu wanda zai rayu babu uwa a kusa da shi kuma ya more rayuwa, there's no love like a mother love for her child”
Kalaman da Mahmood yayi sai ya kara sakata cikin damuwa, ta kara tausayin ďanta, su da suka san dadinta suke fadar haka ina ga wanda be sani ba.
Lumshe ido ta yi wasu hawayen masu zafi suna sauko mata, su da suka rayu da ita kenan suka san dadinta ina ga wanda ya rayu shi kadai be san dadinta ba.
‘Ko waye mahaifiyarsa a yanzu?’
Ta tambaye kanta, kamin ta dago fuskarta ta share hawayen ta nufi kofar fita daga gurin tana sauke kanta kasa domin bata son yaranta da suke falo su lura da kukanta. dakinta ta shiga ta ci kukanta iya wanda ya isheta sannan ta wanke fuskarta ta shafa hoda da kwalli saboda ta bata da fuskar kukan amman ina ya kasa boyuwa a idon mijinta, domin a duk lokacin da ta shiga bangarensa idonta yake fara kallo ta nan yake iya karantar damuwarta.
“Zahra kukan me kika yi?”
Ya tsayar da shirya kulolin abincin da take kuma ta kasa hada ido da shi.
“Na tashi ne bana jindadin jikina”
“Amman ba zan fita ba haka na barki ba, wani abun ya faru ne? Ko yarane suka bata miki rai?”
Ta kalleshi tare da girgiza masa kai.
“No, ina tunanin ďana ne, na kasa manta ciwon har yanzu, ban san ranar da zan warke ba”
Kamar daukewar wutar nepa haka Abiey yayi shiru be sake cewa komai ba, har ta gama zuba abincin ta aje masa a maimakon ya ci sai ya mike tsaye ba tare da ya kalli abincin ba ya fice daga falon na shi ya shige dakinsa, binsa ta yi da kallo hawaye na sauko mata, haka suke yawan samun sabani a duk lokacin da zata nuna masa kauna ko tausayin ďanta da baya tare da ita, wannan dalilin ya saka ta boye abin a ranta ta daina maganarsa ko son sanin halin da yake ciki, balle har ta tambaye shi, yana raye baya raye a halin yanzu duk bata sani ba.
“Lokuta da dama bana iya tunani mai kyau, na kan aikata abun da yake zuwa ya zame min na bakinciki da nadama, ni kawai bana iya aikata komai a daidai”
Ta furta tana girgiza kai kuka take sosai irin kukan nan marar sauti.
AMEER POV.
A gurin da suka saba shakatawa suke zaune, sai dai a yau a waje suke zaune ba VIP ba kamar yadda suka saba, saboda Ameer da ya riga su zuwa ya kama guri a harabar da wasu suke zama ya zauna, a ka'ida idan ya zauna a guri, siye gurin yake irin siyewar da ko awa nawa zai yi ba za a shigo ko a zaunar da wani costumer ba, sai idan ya bar gurin ko da kuwa zuwansa ne na farko a guri, Ameer na jin wata kalar isa da kasaita kamar wani Sarki da shi kadai ya ke da ikon yin yadda yake so a ciki jama'a, sai dai a mamakinsu yau yana zaune cikin mutane and nishadin dake fuskarsa sai ka yi zaton irin samarin nan ne da ba su dauki duniya da zafi ba.
“Miyasa za mu zauna a nan wai?”
Tarig ya tambaya domin basa jin sakewa a public place like this one.
“Ban cilastawa kowa zama ba, ni kuka tarar a nan zaune kuma kuka yi deciding ku zauna, zaku iya shiga ciki idan kuna ra'ayi”
Ya fada tamkar ba shi yake maganar ba, ya tattara hankalinsa gaba daya ya maida gurin mutane dake kai da kawo a gurin.
“Ameer ya kamata ku sasanta kanku da Maleek”
“Miyasa na zauna a nan”
Ameer ya fada da sauri yana rufe idonsa domin ko maganar Maleek baya so. Tarig da yayi maganar ya kalleshi da mamakin jin furuncin da be tsammaci jinsa daga bakinsa a yanzu ba.
“Kana nufin saboda ku shirya ka zauna a nan?”
“Saboda mu kara nisantar juna dai, bana son ko gurin da na zauna Maleek ya sake zama”
“No Ameer wannan dabi'un yara ne, mu kuma ba yara ba ne, be kamata mu yi haka ba?”
“Idan ka sake min wata maganar da ta shafi Maleek Tarig sai na hada kai da shi na bindigeku, baka san yadda yaron nan ya bata min rai ba ko? Kawai yawu ya watsa min a fuska fa haba”
Ameer ya fada babu alamar wasa a fuskarsa. Tarig ya wasa masa wani kallon banza.
“Go ahead waya rike ka? Ka saka bindigar ka halbemu mana sai ka gani idan kai zama zaka yi a duniyar, kai babu wanda ya isa ya fada maka gaskiya ko ya nuna maka abun da kai ba ba daidai ba ne, wane irin girman kai ne a tare da kai?”
“Irin wanda ba a siye da kudi balle ka siye, kuma ba a saukewa balle ka raba ni da shi, ya zaka yi?”
Kallon kallo akuya kallon kura suka rika yi ma junansu. Kamin Ameer ya mike tsaye yana ya nufi motarsa hango Maleek ya fito daga motarsa ya doso gurin. Maleek ya kalli Ameer kamar ya yi masa magana domin shi baya son gaba kuma be iya gaba ba, duk yadda zaka bata masa rai sai yayi maka magana, sai dai kuma wata zuciyar ta hana shi gudun kar Ameer ya disgashi a gaban jama'a.
“Tafiya yayi?”
Maleek ya fada a yayinda yake kokarin zama. Tarig ya sauke ajiyar zuciya ya ciro wayarsa aljihu ya soma tabawa yana fadin.
“Wani lokacin na kan rasa gane kan Ameer, yana da fushi sosai kuma yana dadewa be sauka ba, kai ma kuma abun da ka yi baka kyauta masa, na san yadda ya tsani kazanta taya zaka tofa masa yawu a fuska”
Maleek ya hade yawu na rashin jindadin abun da yayi.
“I know that's why I'm here hakuri na so na ba shi, kuma shi ma ya kamata ace yana kiyaye abun da bana so”
“idan wani ya ciza sai wani ya hura, ba wai kai ka yi fushi ba shi yayi fushi, dukamu tare muke ba zamu zabeka mu cireshi a cikinmu ba, haka kuma na za mu cireka mu zauna da shi”
A kokarin Maleek na kawar da maganar ya tambaye dayan abokin na su.
“Ina Abdull?”
“Be zo ba”
“And miyasa kuka zauna a nan?”
“Ameer na tarar a nan, baya son shiga ciki saboda kar ku zauna a guri daya”
Maleek yayi murmushi mai sauti
“Yara ne suke wannan, of course zamu yi fada mu batawa juna rai amman ban da gaba ko tsanar juna ko kyamar zama kusa da juna”
Maleek ya fadar hakan Dawood da ya karaso inda suke zaune ya daki kafadarsa yana dariya.
“That's right bro, zaman da babu fada ba taren amana ba ce, zo mu zauna shi ne zo mu saba dole ne mu rika hakuri da juna”
Maleek ya mika masa hannu suka gaisa, kana suka mike tsaye gaba dayansu suka shiga can cikin VIP din suka zauna, wani sabon shafin hira ya bude, waiter dake kawo musu lemu ya kawo tare da zubawa kowa a cups dinsa sannan ya aje ragowar, ya koma gurin aikinsa Maleek ne ya fara dauka ya sha domin coconut drink ne favorite dinsa, sannan Dawood ya sha, an jima kadan aka kawo musu abin tabawa kowaya ci ya sha, daman Ameer ne kawai baya ci ko shan wani abu a gurin saboda tsabdar da yake da ita, wai shi ba zai iya cin abincin restaurant ba domin be san iya sharing din da aka yi da spoon din ko plate ba, and be san wadanda suka girka ba, kuma ba shi da tabbacin an tsabtace girkin ko akasin haka.
After like 20 min da shan lemin Ameer ya ji kansa na masa nauyi har yana saukowa cikin idonsa, ba kuma ciwo yake jin kan na masa ba nauyi yake irin na wadanda bachi be wadace su ba, sai dai ya daure duk hirar da ake be nuna komai ba duk da kasancewar baya cewa komai sai kallonsu yake yana murmushin karfin hali.
“Hey Bachi kake ji?”
Tarig ya tambaya lura da yadda Ameer yake lumshe ido yana budewa a kokarinsa na hana kanshi bachin da be san ta ina yake fito masa ba.
“Maybe”
Ya fada cikin rashin tabbacin idan bachin ne domin ya san yayi enough bachi jiya. Ya mike tsaye ya dauki keys dinsa dake kan table din
“Bari na tafi”
Miyewa ta yi sauye bayan fadar haka ta nufi wata karamar kofa dake falon ta bude ta fita tsakar gidan da ko'ina yake tsab, matsawa ta yi kusa da flowers ta mika hannunta tana taba su a hankali, babu ranar da bata tunanin ďanta, babu ranar da zata zauna ta yi hira da yaranta akan rayuwarsu bata tuna da ďanta, damuwarshi ta haifar mata da damuwa da yawa, ta haifar masa da rashin kuzarin iya rike kanta a duk lokacin da ta tuna kamar yadda hawaye suka fara wanke fuskarta, ta kasa cire kanta a damuwa ta kasa daina tunaninsa duk da kasancewar likita ya gargadeta da ta cire damuwa a ranta saboda hawan jinin da take fama da shi. A tsorace ta juyo jin muryar Mahmood yana kiranta. Kamar hoto ya tsaya yana kallonta ganin hawaye a idonta.
“Ummi lafiya?”
Ta taba fuskarta sai ta ji hawayen sa bata san lokacin da suka sauko mata ba, murmushi ta yi ta share hawayen.
“Lafiya kalau, yanzu ka dawo?”
“Eh ni ma dauko Abiey, amman Ummi ba lafiya ba kalli fa kuka kike yi”
“Tunani kawai nake yi, makomar yayana idan bana raye that's...”
Ta karasa wasu hawayen na sauko mata.
“Haba Ummi ki daina kawo wannan abun a ranki please, ba zai taba faruwa ba tare zamu rayuwa In Shaa Allah”
Ya rumgume yana jin wani emotional, he can't imagine his life without her, ta ya za su iya rayuwa.
“Ummi ba zamu iya rayuwa ba idan babu ke, babu wanda zai rayu babu uwa a kusa da shi kuma ya more rayuwa, there's no love like a mother love for her child”
Kalaman da Mahmood yayi sai ya kara sakata cikin damuwa, ta kara tausayin ďanta, su da suka san dadinta suke fadar haka ina ga wanda be sani ba.
Lumshe ido ta yi wasu hawayen masu zafi suna sauko mata, su da suka rayu da ita kenan suka san dadinta ina ga wanda ya rayu shi kadai be san dadinta ba.
‘Ko waye mahaifiyarsa a yanzu?’
Ta tambaye kanta, kamin ta dago fuskarta ta share hawayen ta nufi kofar fita daga gurin tana sauke kanta kasa domin bata son yaranta da suke falo su lura da kukanta. dakinta ta shiga ta ci kukanta iya wanda ya isheta sannan ta wanke fuskarta ta shafa hoda da kwalli saboda ta bata da fuskar kukan amman ina ya kasa boyuwa a idon mijinta, domin a duk lokacin da ta shiga bangarensa idonta yake fara kallo ta nan yake iya karantar damuwarta.
“Zahra kukan me kika yi?”
Ya tsayar da shirya kulolin abincin da take kuma ta kasa hada ido da shi.
“Na tashi ne bana jindadin jikina”
“Amman ba zan fita ba haka na barki ba, wani abun ya faru ne? Ko yarane suka bata miki rai?”
Ta kalleshi tare da girgiza masa kai.
“No, ina tunanin ďana ne, na kasa manta ciwon har yanzu, ban san ranar da zan warke ba”
Kamar daukewar wutar nepa haka Abiey yayi shiru be sake cewa komai ba, har ta gama zuba abincin ta aje masa a maimakon ya ci sai ya mike tsaye ba tare da ya kalli abincin ba ya fice daga falon na shi ya shige dakinsa, binsa ta yi da kallo hawaye na sauko mata, haka suke yawan samun sabani a duk lokacin da zata nuna masa kauna ko tausayin ďanta da baya tare da ita, wannan dalilin ya saka ta boye abin a ranta ta daina maganarsa ko son sanin halin da yake ciki, balle har ta tambaye shi, yana raye baya raye a halin yanzu duk bata sani ba.
“Lokuta da dama bana iya tunani mai kyau, na kan aikata abun da yake zuwa ya zame min na bakinciki da nadama, ni kawai bana iya aikata komai a daidai”
Ta furta tana girgiza kai kuka take sosai irin kukan nan marar sauti.
AMEER POV.
A gurin da suka saba shakatawa suke zaune, sai dai a yau a waje suke zaune ba VIP ba kamar yadda suka saba, saboda Ameer da ya riga su zuwa ya kama guri a harabar da wasu suke zama ya zauna, a ka'ida idan ya zauna a guri, siye gurin yake irin siyewar da ko awa nawa zai yi ba za a shigo ko a zaunar da wani costumer ba, sai idan ya bar gurin ko da kuwa zuwansa ne na farko a guri, Ameer na jin wata kalar isa da kasaita kamar wani Sarki da shi kadai ya ke da ikon yin yadda yake so a ciki jama'a, sai dai a mamakinsu yau yana zaune cikin mutane and nishadin dake fuskarsa sai ka yi zaton irin samarin nan ne da ba su dauki duniya da zafi ba.
“Miyasa za mu zauna a nan wai?”
Tarig ya tambaya domin basa jin sakewa a public place like this one.
“Ban cilastawa kowa zama ba, ni kuka tarar a nan zaune kuma kuka yi deciding ku zauna, zaku iya shiga ciki idan kuna ra'ayi”
Ya fada tamkar ba shi yake maganar ba, ya tattara hankalinsa gaba daya ya maida gurin mutane dake kai da kawo a gurin.
“Ameer ya kamata ku sasanta kanku da Maleek”
“Miyasa na zauna a nan”
Ameer ya fada da sauri yana rufe idonsa domin ko maganar Maleek baya so. Tarig da yayi maganar ya kalleshi da mamakin jin furuncin da be tsammaci jinsa daga bakinsa a yanzu ba.
“Kana nufin saboda ku shirya ka zauna a nan?”
“Saboda mu kara nisantar juna dai, bana son ko gurin da na zauna Maleek ya sake zama”
“No Ameer wannan dabi'un yara ne, mu kuma ba yara ba ne, be kamata mu yi haka ba?”
“Idan ka sake min wata maganar da ta shafi Maleek Tarig sai na hada kai da shi na bindigeku, baka san yadda yaron nan ya bata min rai ba ko? Kawai yawu ya watsa min a fuska fa haba”
Ameer ya fada babu alamar wasa a fuskarsa. Tarig ya wasa masa wani kallon banza.
“Go ahead waya rike ka? Ka saka bindigar ka halbemu mana sai ka gani idan kai zama zaka yi a duniyar, kai babu wanda ya isa ya fada maka gaskiya ko ya nuna maka abun da kai ba ba daidai ba ne, wane irin girman kai ne a tare da kai?”
“Irin wanda ba a siye da kudi balle ka siye, kuma ba a saukewa balle ka raba ni da shi, ya zaka yi?”
Kallon kallo akuya kallon kura suka rika yi ma junansu. Kamin Ameer ya mike tsaye yana ya nufi motarsa hango Maleek ya fito daga motarsa ya doso gurin. Maleek ya kalli Ameer kamar ya yi masa magana domin shi baya son gaba kuma be iya gaba ba, duk yadda zaka bata masa rai sai yayi maka magana, sai dai kuma wata zuciyar ta hana shi gudun kar Ameer ya disgashi a gaban jama'a.
“Tafiya yayi?”
Maleek ya fada a yayinda yake kokarin zama. Tarig ya sauke ajiyar zuciya ya ciro wayarsa aljihu ya soma tabawa yana fadin.
“Wani lokacin na kan rasa gane kan Ameer, yana da fushi sosai kuma yana dadewa be sauka ba, kai ma kuma abun da ka yi baka kyauta masa, na san yadda ya tsani kazanta taya zaka tofa masa yawu a fuska”
Maleek ya hade yawu na rashin jindadin abun da yayi.
“I know that's why I'm here hakuri na so na ba shi, kuma shi ma ya kamata ace yana kiyaye abun da bana so”
“idan wani ya ciza sai wani ya hura, ba wai kai ka yi fushi ba shi yayi fushi, dukamu tare muke ba zamu zabeka mu cireshi a cikinmu ba, haka kuma na za mu cireka mu zauna da shi”
A kokarin Maleek na kawar da maganar ya tambaye dayan abokin na su.
“Ina Abdull?”
“Be zo ba”
“And miyasa kuka zauna a nan?”
“Ameer na tarar a nan, baya son shiga ciki saboda kar ku zauna a guri daya”
Maleek yayi murmushi mai sauti
“Yara ne suke wannan, of course zamu yi fada mu batawa juna rai amman ban da gaba ko tsanar juna ko kyamar zama kusa da juna”
Maleek ya fadar hakan Dawood da ya karaso inda suke zaune ya daki kafadarsa yana dariya.
“That's right bro, zaman da babu fada ba taren amana ba ce, zo mu zauna shi ne zo mu saba dole ne mu rika hakuri da juna”
Maleek ya mika masa hannu suka gaisa, kana suka mike tsaye gaba dayansu suka shiga can cikin VIP din suka zauna, wani sabon shafin hira ya bude, waiter dake kawo musu lemu ya kawo tare da zubawa kowa a cups dinsa sannan ya aje ragowar, ya koma gurin aikinsa Maleek ne ya fara dauka ya sha domin coconut drink ne favorite dinsa, sannan Dawood ya sha, an jima kadan aka kawo musu abin tabawa kowaya ci ya sha, daman Ameer ne kawai baya ci ko shan wani abu a gurin saboda tsabdar da yake da ita, wai shi ba zai iya cin abincin restaurant ba domin be san iya sharing din da aka yi da spoon din ko plate ba, and be san wadanda suka girka ba, kuma ba shi da tabbacin an tsabtace girkin ko akasin haka.
After like 20 min da shan lemin Ameer ya ji kansa na masa nauyi har yana saukowa cikin idonsa, ba kuma ciwo yake jin kan na masa ba nauyi yake irin na wadanda bachi be wadace su ba, sai dai ya daure duk hirar da ake be nuna komai ba duk da kasancewar baya cewa komai sai kallonsu yake yana murmushin karfin hali.
“Hey Bachi kake ji?”
Tarig ya tambaya lura da yadda Ameer yake lumshe ido yana budewa a kokarinsa na hana kanshi bachin da be san ta ina yake fito masa ba.
“Maybe”
Ya fada cikin rashin tabbacin idan bachin ne domin ya san yayi enough bachi jiya. Ya mike tsaye ya dauki keys dinsa dake kan table din
“Bari na tafi”