Sashe 40
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fuuu ya fice daga gurin be tsaya sauraren abun da Mahmood zai fada ba, baya jin komawa ya cikin gidan hakan ya saka shi nufar Katon Garden din dake gidan, Garden da aka kawata da itatuwa da fulawoyi ta ko'ina ta bangare daya kuma an yi Swimming Pool, an jera kujeru a kusa da gurin, ta dayan gefen dama kuma kebantattun tsuntsaye ne da aka yi musu muhalli na dabam, sai barewar dake ta kiwonta a gurin wani decoration na busashen itace. A hankali yake takawa har ya isa gurin da tsuntsayen suke ya bude yar wayar da aka kewasu da ita ya shiga cikin garden din, guri ya samu a gurin kujerun nan da ake na siminti ya zauna yana kallon yadda wasu suke tashi wasu na sauka. Wayarsa dake hannunsa ya bude Gallary ya shiga can wani gurin ajiyar sirrin ya kamo hoton mahaifiyarsa inda take zaune tare da Abiey aka yi musu hoto Tan murmushi har koranta sun bayyana. Yatsansa yakai ya shafa saitin inda take a jikin hoto yana jin wani launi marar dadi na masa yawo a zuciya. Shi ne kadai abun da yake iya, ya kalli hotonta ko ya shafa amman a fili ba zai iya zama yayi shawara ko hira da ita ba, ba zai iya kai hannu ya taba taba jikinta a matsayinta na mahaifinyarsa ba, ba zai iya kebewa daga ita sai shi na tsawon awa daya ba, tun da yayi wayo ya mallaki hankalin kansa be san wata rana da haka ta taba faruwa a tsakaninsu ba, sai dai duk da haka Ummi bata taba juya masa baya ba, bata taba jin ta tsana shi ba, tana kokarin ganin ta ja shi a jikin sai ta ga hakan ya gagara sannan ya saka masa ido ta daina kokarin kebewa da shi a cilas ko taba shi, sai ma taimaka masa da take na yadda zai rayu ba tare da yan'uwansa sun shiga rayuwarsa sun bata masa rai kamar yadda baya bukata ba.
Shi dai ya san ba tsanar mahaifiyarsa yayi ba, domin bata yi masa abun da zai saka ya tsane ta ba, idan ma ta yi masa dole ya so ta saboda ita din uwa ce, balle kuma bata yi ba, sai dai ya tsabarsa da mata ne ya saka ita din yake kaurace mata saboda ita ma tana daya daga cikin jinsin matan. To miyasa ya tsani matan? Why? Shi kasan ba zai iya fada ba, be yi soyayya ba balle yace yaudararsa akai yi, be zauna da matar uba ba balle yace ta cucheshi. Sai da aka kira Sallah magariba sannan fito daga gurin, a harabar gidan ya hadu da Ummi ta nufo Garden tana kallonsa.
“Mahmood yace min kana Garden tun dazu gashi Magariba ta yi baka san iya abin da zai sauko ba”
Cike da kulawa irin ta uwa take masa magana, lafiyarsa ce abar damuwarta a yanzu. Ya dan dauke kai daga barin kallonta ya kalli kasa.
“Ina taba waya ne ban ankaro lokaci yayi ba sai da na ji kira, bari na je na yi alwala”
Ya amsata yana tafiya sai ta juyo ta biyo bayansa domin inda sabo ta saba da halinsa. Yana gaba tana bayansa har suka shiga falon kai tsaye ya nufi Upstairs ita ma stairs din ta nufa domin gabatar da nata alwalan, daf da zai wuce dakin da Waira take ciki ya shiga nasa dakin sai gata ta fito da gudu daga dakin da yake bude kicibis suka yi da Maleek bata tsaya komai ba ta rumgume shi ta rike da mugun karfi.....
Duk wani abu mai rai da motsi a cikin jikinsa sai da ya tsaya cak, ciki har da bugun zuciyarsa da numfashinsa.
Ummi ta rufe baki daga bayansa da take tsaye domin ta ga abun da ya faru, Nimra da ta biyo bayanta da gudu ma ta tsaya cak ta zaro ido. Shisshikar kuka kawai Waira take tana kara rike shi ba dan ta san waye shi ba ita dai gurin boya da cuto kawai take nema. Ganin ya rumtse ido ya ya cige baki ya saka Ummi ta nufo inda yake da sauri ta banbare hannun Waira har da mai ciwon taja ta baya, a lokacin ne wani abu mai kamar ba suma ya ziyarce shi sai ya ji wani uban jiri da rawar jiki na neman kamashi ya bude ido zuciyarsa har gargada take numfashinsa na sarkewa. Waira sai kuche kushen ta subuce a hannun Ummi take ta sake rikeshi ganin take kamar maza sun fi mata yi mata kirki da kyautata. Tasss ya wanke mata fuska da mugun mari har sai da ta ji wata kara a kunnenta ganinta yayi batan wucin gadi, kwatankwacin tsayin da yayi a dazun da ta rumgume shi irinsa ta yi jini ya cika bakinta idonta ya cika da hawaye ya sauko mata...
AMEER POV.
10:24pm O'clock
Abincin ya masa dadi fiye da na kullum har cikin kwakwalwa kansa yake jin yadda abincin yake kai masa. Ba karyar Step Mother dinsa ta iya girki musamman na yau da ya zama na dabam.
“Da alama dai yau gaba daya zaka cinye jalof”
Ameer ya tsayar da cin abincin da yake yayi murmushi tare da daukar cup din ruwa ya sha.
“Sis don't fake it ke ma fa kin ji dadin abincin nan”
Sister ta yi murmushi tana cigaba da cin abincin. Wayar dake kam teburin ya dauka ya shiga Instagram dinsa ya the first thing da ya fara dubawa shi ne account din Nimra, sai kuma yayi sa'a ta amsa masa bukatarsa ta son following dinta.
“Good Girl, i like you”
Ya furta yana jin kamar wani target dinsa ya kama hanya.
“Is she the one?”
Ta tambaya duk kuwa da bata san abun da yake kallo a wayar ba, sai ya dago ya kalleta.
“Who?”
“Girlfriend”
Yayi wani miskilin murmushi
“Tun da kike a rayuwarki kin taba jin na yi maganar budurwa?”
“Noo amman na san kana da ita”
“No Fiyya ni bana boye komai ai, idan akwai ta definitely zaku sani, more especially you, kin san you're my favorite, so ni bana da budurwa?”
Ya maida hankalinsa gurin wayar yana tunanin irin sakon da zai tura mata.
“Amman miyasa? Ni Wallahi ban taba maka magana ba ne kawai amman na dauka kana da girlfriend”
“Idan har zan yi budurwa zan zabo mai tsada ce, kuma har yanzu ban taba cin karo da wanda ta yi daidai da ra'ayi na ba, idan har zan so mace dole sai mai matukar tsabta wanda bata taba sanin miye kazanta ba a rayuwarta, wacce ke wanka da tsabta kamar yadda nake, who can cook delicious food, mai yawan kamshi wacce idan an rabe ta babu abun da zan ji sai Kamshi, mai matukar kyau fara sosai yar gidan masu kudi, mai ji da kanta, kuma wacce idan na ce ta aske gashin kanta zata aske yi kamar dai Angel, sannan kuma Virgin”
“Wacece kuma Angel”
“Wata Ahlil Kitab ce, kin san su babu ruwansu da barin gashi, kuma tana da tsabta irin yadda nake so a jikin mace”
“Tab za a samu duk mai abun da ka lisaffa amman ban da yawan tsabtarka da kuma aske gashin kai, sai idan ka samu wacce bata ta gashin daman”
“Za a samu wata rana, duk da na san dukan abun da na lissafa abu ne mai wahala a yanzu ba musamman ma virgin din, domin yan mata yanzu tun a waje suke siyar da mutuncinsu da kudi ko da sunan soyayya, ke kanki bana iya shaidarki a yanzu”
Ta zaro ido tana kallonsa da mugun mamaki har tana nuna kanta.
“Ni.... Na yarda na bada mutuncin ne ai sai Momy ta ci Ubana”
“Lokacin da za ku yi ai babu wanda zai sani, ita kanta Momyn ba zaki bari ta gane ba, ku yaran zamani ne kun fi iyayenku wayo”
Ya fada kamar ba da shi ba, ya mike tsaye yaja kujerar baya.
“Good Night”
Ya fice daga gurin yana taba wayar, fiyya ta bishi da kallon mamaki har fice daga falon gaba daya.
“Kasan yan matan da ka lalata kenan shiyasa kake fadar haka”
Ta fada bayan ya fice.
Motarsa ya nufa ya sai jingina yana jin nan ne safe place da zai samu damar aikata abun da yake son yi.
“After all abun da kika Hada kai da dan'uwanki kika min be wadatar ba sai kin sake cutar da ni da cewar na dauko wata yarinya a motar? Why Nimra? Me na tare muku ne? Miyasa ba ku son ganin farincikina?. Ban tsammanci kalar wannan rayuwar daga gareki ba, a farkon ganin da na yi miki na aminta da ke shiyasa zuviyata ta natsu da ke, ashe akwai abun da kike shirya min, kin kyauta Nimra kuma na gode”
Ya tura mata bayan ya gama rubutawa, so yake ya kalailaye zuciyarta ya siye da kalaman dauraya ya yaudare ya karye mata guiwa kamar yadda ta yi masa.
“By the way, akwai sarewata a cikin motar, ki aiko min da ita a inda muka saba haduwa dake”
Ya sake aikawa, daman sarewar na daga dalilin da ya saka ya nemi handling dinta a IG. after ya gama tura mata ya dago jikin motar ya dawo cikin gidan, yana tunanin yadda sakon zai riske ta, yana misalta irin amsar da zata ba shi Idan har yayi nasarar karya mata zuciyar.
Yana shiga dakinsa amsar sakon da ya tura ya fara dawo masa tun yana karantawa a tsaye har ya kai ga zaunawa.
Shi dai ya san ba tsanar mahaifiyarsa yayi ba, domin bata yi masa abun da zai saka ya tsane ta ba, idan ma ta yi masa dole ya so ta saboda ita din uwa ce, balle kuma bata yi ba, sai dai ya tsabarsa da mata ne ya saka ita din yake kaurace mata saboda ita ma tana daya daga cikin jinsin matan. To miyasa ya tsani matan? Why? Shi kasan ba zai iya fada ba, be yi soyayya ba balle yace yaudararsa akai yi, be zauna da matar uba ba balle yace ta cucheshi. Sai da aka kira Sallah magariba sannan fito daga gurin, a harabar gidan ya hadu da Ummi ta nufo Garden tana kallonsa.
“Mahmood yace min kana Garden tun dazu gashi Magariba ta yi baka san iya abin da zai sauko ba”
Cike da kulawa irin ta uwa take masa magana, lafiyarsa ce abar damuwarta a yanzu. Ya dan dauke kai daga barin kallonta ya kalli kasa.
“Ina taba waya ne ban ankaro lokaci yayi ba sai da na ji kira, bari na je na yi alwala”
Ya amsata yana tafiya sai ta juyo ta biyo bayansa domin inda sabo ta saba da halinsa. Yana gaba tana bayansa har suka shiga falon kai tsaye ya nufi Upstairs ita ma stairs din ta nufa domin gabatar da nata alwalan, daf da zai wuce dakin da Waira take ciki ya shiga nasa dakin sai gata ta fito da gudu daga dakin da yake bude kicibis suka yi da Maleek bata tsaya komai ba ta rumgume shi ta rike da mugun karfi.....
Duk wani abu mai rai da motsi a cikin jikinsa sai da ya tsaya cak, ciki har da bugun zuciyarsa da numfashinsa.
Ummi ta rufe baki daga bayansa da take tsaye domin ta ga abun da ya faru, Nimra da ta biyo bayanta da gudu ma ta tsaya cak ta zaro ido. Shisshikar kuka kawai Waira take tana kara rike shi ba dan ta san waye shi ba ita dai gurin boya da cuto kawai take nema. Ganin ya rumtse ido ya ya cige baki ya saka Ummi ta nufo inda yake da sauri ta banbare hannun Waira har da mai ciwon taja ta baya, a lokacin ne wani abu mai kamar ba suma ya ziyarce shi sai ya ji wani uban jiri da rawar jiki na neman kamashi ya bude ido zuciyarsa har gargada take numfashinsa na sarkewa. Waira sai kuche kushen ta subuce a hannun Ummi take ta sake rikeshi ganin take kamar maza sun fi mata yi mata kirki da kyautata. Tasss ya wanke mata fuska da mugun mari har sai da ta ji wata kara a kunnenta ganinta yayi batan wucin gadi, kwatankwacin tsayin da yayi a dazun da ta rumgume shi irinsa ta yi jini ya cika bakinta idonta ya cika da hawaye ya sauko mata...
AMEER POV.
10:24pm O'clock
Abincin ya masa dadi fiye da na kullum har cikin kwakwalwa kansa yake jin yadda abincin yake kai masa. Ba karyar Step Mother dinsa ta iya girki musamman na yau da ya zama na dabam.
“Da alama dai yau gaba daya zaka cinye jalof”
Ameer ya tsayar da cin abincin da yake yayi murmushi tare da daukar cup din ruwa ya sha.
“Sis don't fake it ke ma fa kin ji dadin abincin nan”
Sister ta yi murmushi tana cigaba da cin abincin. Wayar dake kam teburin ya dauka ya shiga Instagram dinsa ya the first thing da ya fara dubawa shi ne account din Nimra, sai kuma yayi sa'a ta amsa masa bukatarsa ta son following dinta.
“Good Girl, i like you”
Ya furta yana jin kamar wani target dinsa ya kama hanya.
“Is she the one?”
Ta tambaya duk kuwa da bata san abun da yake kallo a wayar ba, sai ya dago ya kalleta.
“Who?”
“Girlfriend”
Yayi wani miskilin murmushi
“Tun da kike a rayuwarki kin taba jin na yi maganar budurwa?”
“Noo amman na san kana da ita”
“No Fiyya ni bana boye komai ai, idan akwai ta definitely zaku sani, more especially you, kin san you're my favorite, so ni bana da budurwa?”
Ya maida hankalinsa gurin wayar yana tunanin irin sakon da zai tura mata.
“Amman miyasa? Ni Wallahi ban taba maka magana ba ne kawai amman na dauka kana da girlfriend”
“Idan har zan yi budurwa zan zabo mai tsada ce, kuma har yanzu ban taba cin karo da wanda ta yi daidai da ra'ayi na ba, idan har zan so mace dole sai mai matukar tsabta wanda bata taba sanin miye kazanta ba a rayuwarta, wacce ke wanka da tsabta kamar yadda nake, who can cook delicious food, mai yawan kamshi wacce idan an rabe ta babu abun da zan ji sai Kamshi, mai matukar kyau fara sosai yar gidan masu kudi, mai ji da kanta, kuma wacce idan na ce ta aske gashin kanta zata aske yi kamar dai Angel, sannan kuma Virgin”
“Wacece kuma Angel”
“Wata Ahlil Kitab ce, kin san su babu ruwansu da barin gashi, kuma tana da tsabta irin yadda nake so a jikin mace”
“Tab za a samu duk mai abun da ka lisaffa amman ban da yawan tsabtarka da kuma aske gashin kai, sai idan ka samu wacce bata ta gashin daman”
“Za a samu wata rana, duk da na san dukan abun da na lissafa abu ne mai wahala a yanzu ba musamman ma virgin din, domin yan mata yanzu tun a waje suke siyar da mutuncinsu da kudi ko da sunan soyayya, ke kanki bana iya shaidarki a yanzu”
Ta zaro ido tana kallonsa da mugun mamaki har tana nuna kanta.
“Ni.... Na yarda na bada mutuncin ne ai sai Momy ta ci Ubana”
“Lokacin da za ku yi ai babu wanda zai sani, ita kanta Momyn ba zaki bari ta gane ba, ku yaran zamani ne kun fi iyayenku wayo”
Ya fada kamar ba da shi ba, ya mike tsaye yaja kujerar baya.
“Good Night”
Ya fice daga gurin yana taba wayar, fiyya ta bishi da kallon mamaki har fice daga falon gaba daya.
“Kasan yan matan da ka lalata kenan shiyasa kake fadar haka”
Ta fada bayan ya fice.
Motarsa ya nufa ya sai jingina yana jin nan ne safe place da zai samu damar aikata abun da yake son yi.
“After all abun da kika Hada kai da dan'uwanki kika min be wadatar ba sai kin sake cutar da ni da cewar na dauko wata yarinya a motar? Why Nimra? Me na tare muku ne? Miyasa ba ku son ganin farincikina?. Ban tsammanci kalar wannan rayuwar daga gareki ba, a farkon ganin da na yi miki na aminta da ke shiyasa zuviyata ta natsu da ke, ashe akwai abun da kike shirya min, kin kyauta Nimra kuma na gode”
Ya tura mata bayan ya gama rubutawa, so yake ya kalailaye zuciyarta ya siye da kalaman dauraya ya yaudare ya karye mata guiwa kamar yadda ta yi masa.
“By the way, akwai sarewata a cikin motar, ki aiko min da ita a inda muka saba haduwa dake”
Ya sake aikawa, daman sarewar na daga dalilin da ya saka ya nemi handling dinta a IG. after ya gama tura mata ya dago jikin motar ya dawo cikin gidan, yana tunanin yadda sakon zai riske ta, yana misalta irin amsar da zata ba shi Idan har yayi nasarar karya mata zuciyar.
Yana shiga dakinsa amsar sakon da ya tura ya fara dawo masa tun yana karantawa a tsaye har ya kai ga zaunawa.