Sashe 137
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
“Waira suna ne mai kyau, sai dai asalin sunan Nuwaira ne ba Waira zalla ba, saboda haka zamu iya kiranki da Nuwaira, ko kina sha'awar a canja miki sunan ne?”
Ta girgiza kai alamar aa, ta juyo ya rumgume Ummi.
“Allah ya miki albarka ya tsare rayuwarki da imaninki Nuwaira”
Duk suka amsa da Ameen. Matan da Iman din ya gayyato suka gabatar da Nuwaira yadda zata yi ibada, wanka tsarkin da zata yi na shiga addinin musulunci, da kuma dokokin da suka wajaba a kanta, suka tambayeta ko akwai wata matsala da take fuska ta musallin ko abinci ko kuma wata baraza ta amsa da cewar babu ko daya. Sai da aka fara tada Sallah azahar sannan Mahmood ya dawo da su Ummi gida, Ameer da Maleek suka yi sallah a masallacin tare da Abiey.
Ummi ce ta jagoranci Nuwaira gurin nuna mata yadda zata yi wankan tsarkin, bayan ta nuna mata a waya yadda zata yi a waya sai da ta tabbatar ta iya sannan ta fita ta bata guri, Nuwaira ta yi wanka da kanta ta fito tana daure da tawul ta rufe kanta da wani. Ummi dake zaune gafen gadonta tana jiranta ta mike tsaye ta mika mata sabuwar rigar abayar da zata sauko mata har kasa.
“Wannan kyauta ce daga gareni, farkon zuwana makka na siyo rigar nan amman ban taba sakawa ba, da na aje har sai idan daya daga cikin yayana za su yi aure na ba su saboda tsadar rigar, sai dai musuluntar da kika yi a yau, ya saka kin zama ďaya daga cikin yayana, zan iya miki komai fiye da yadda zan yi musu ma”
Nuwaira ta tara hannu ta karba tana kallon Ummi dake hawaye tare da murmushi.
“Na gode, ina ma ace zan iya saka miki da duk abun da kika yi min? Hakika ke uwa ce ta gari, kin cancanci ko wane irin Award na girmamawa da karanci”
“Idan kin shirya ki fito waje yan'uwanki suna kasa suna jiranki”
Ta gyada kai sannan ta karbi rigar ta aje saman gadon. Ummin ta juya ta fice daga dakin, Hannu Nuwaira ta kai ta taba rigar yadda ta sha stone tana kyali ga yadin sai walwalniya yake yana daukar ido, kana kallon rigar kasan an zuba guri gurin siyenta. Ta dade tana kallon rigar sannan ta mike tsaye ta cire tawul dinta ta dauki rigar ta zura, daman can bata mu'alama da birejiya dan haka bata damu da neman inda take ba balle ta saka. Tana zura rigar ta dauki mayafin abayar ta rufe kanta sai ta taka gurin madubi ta kalli kanta. Dan murmushi ganin yadda dark green din abayar ta yi mata masifar kyau kai kace sarauniyar Abuja ce, tsayin rigar 58 ne ita kuma tana saka 54 ne haka ya saka rigar ta yi mata fadi da tsayi, sai dai ko kadan hakan be rage komai daga kyaunta ba. Ta saka hannu ta rike rigar tana takawa a hankali har ta isa gurin kofar ta bude ta fita, tana fara saukowa stiars idon kowa ya dawo kanta, Ameer be san lokacin da ya mike tsaye yana kallonta kamin murmushinsa ya fara yi mata marhabun da saukowa. Maleek ya kalleshi ya kalli Abiey sannan shi da Mahmood suka kalli juna, Ummi ma kallonsa ta yi kamin ta dauke ido ta kalli Nuwaira. Tsaye ta fara yi a lokacin da ta sauko har sai da Namra ta mike tsaye ta isa gurinta ta riko hannunta.
“Zo na nuna miki wani abu little Sis”
Gurin wata Laptop dake aje kan kujera Namra ta nufa da ita, suna isa ta saki hannunta ta bude laptop din ta shiga whatsapp din ta kunna video call, few seconds Shuraim yayi picking fuskarsa da murmushi, Nuwaira na ganinsa ta durkusa a gaban laptop din tana kallonsa da murmushi a fuskarta.
“Sulem...”
“Baby girl Welcome to World Of Islam, na yi matukar farinciki na jidadi a lokacin da na Namra takw fada min hukuncin da kika yanke, na yi bakinciki da bana kusa da ke, da yanzu da ni za a samu wannan ladar, amman a haka ma ina farinciki yanzu kin kallama komai duk wani abu da ake so a mace a yanzu kin hada shi”
“I miss you”
Ta fada hawaye na sauko mata.
“I miss you too baby girl, idan zan zo zan kawo miki tsaraba mai yawa kuma mai ban mamaki”
“Maybe ba zaka same ni ba, zan tafi gida gobe”
Shuraim ya dan yi jimm for some seconds sannan ya kalli Namra dake gafenta.
“Why? Akwai matsala ne Namra?”
“No ita dai take ra'ayin zuwa”
“Ina fatar ba za su cutar da ke ba”
“Nima ina fatar haka”
“Zan tare a Katsina, sai na ganki i miss you so much”
“Ina da labari da yawa da zan baka”
“Ni ma ina da labarai da yawa Baby girl ”
Ta taba hancinta ta kai hannunta ta taba jikin computer sai yayi dariya shi a ya taba hancinsa ya taba computer.
“See you”
Namra ta rufe computer, Nuwaira ta juya ta kalli Namra tana murmushi.
“Nuwaira ga wannan na san zai taimaka miki gurin Sallah saboda yanzu kika fara, yana magana kuma yana fadar duk wani tasbihi da ya kamata ki yi a cikin Sallah”
Nuwaira ta karasa kusa da Abiey ta tara hannu biyu ta karbi prayer mat din.
“Na gode”
Ta shafa carpet din dake cikin wani jacket mai kyau kamar ba prayer mat. Ameer ya tashi ya fita, Namra kuma ta shiga dakinta sai gata ta fito da katon akwaiti ta sauko da shi.
“Ban san me zan baki ba, kuma na san kayana ba su miki, so shiyasa na zabi baki tufafin da ban danka ba gasu na hada miki guri daya a akwaiti, akwai turarukan jiki da na fesawa, kuma akwai mayuka da sabulai masu kyau”
“Na gode”
Nuwaira ta yi mata godiya tana kallon madaidaicin akwatin. Kamin ta juyo ta kalli Ameer da ya mika mata box, ta karba da hannu biyu ta bude sai ta yi arba da kur'ane mai kyau. Ta bude ido ta risina kasa ta saka hannu biyu ta ciro kur'anen ta sumbanceshi sannan ta kalli Ameer idonta na cika da hawaye.
“Na gode”
Ta sakar mata murmushinsa mai matukar tsada ta warware wata yar karamar sarka ya daura mata a hannu a yayin da take rike da kur'anen, abun hannuna ne mai kyau fari mai kamar azurfa.
“Welcome to the peace”
“Thank you, duk wannan saboda kai ne Ameer”
Abiey ya mike tsaye yana fadin.
“Ameer ka yi abun a yaba, ka kyauta kuma na jidadin haka Allah ya baka lada, ya saka maka da alheri, ina fatar a yanzu ba za a sake samun matsala ko tsabanin tsakaninka da yan'uwanka ba, Allah ya hada kanku”
“Ameen”
Ya amsa yana kallon Nuwaira da ta aje kur'anen tana ta taba abun hannun da ya saka mata cikin farinciki da jindadi.
“Yayi kyau”
“Do you like it?”
Tambayarta yake tana kallonta kamar daga shi sai ita ne a falon, gaba daya ta dauke masa hankali baya ganin kowa. Ta daga alamar yes she like it kamin ta dago ta kalleshi wannan karon hakoranta a waje yake, can kuma ta juya ta kalli Mahmood da ya mika mata chocolate da carbin hannunaa yar maroko, wato counter.
“Ga wannan zaki iya yin tasbihi da ita ko salati, zata kirga miko ko adadin guda nawa kike son yi, kuma ga chocolate kowa ya baki komai ban san me zan baki ba”
“Thank you”
Ta karba ta dora saman jikinta sannan ta kalli Maleek, shi kam be roko mata komai ba domin ba sa ran su ma za su mata kyauta ba, idan ma zai bata be san wace kyautar zai bata ba. Hakan kuma ba karamin dadi yayi ma Ameer ba daman shi so yake ya zama shi kadai ne yake burge Nuwaira baya son abokin takara.
“Maybe next time ni ban riko miki komai ba”
Ta yi murmushi ta maida hankalinta gurin abun hannun da Ameer ya daura mata, ita dai tana kaunar ayi mata kyauta wani abun da ya danganci sarka ko abun hannu.
“Ameer kai ka katse min sarkar da Sulem ya ba ni ka tuna?”
“Gashi nan ai na baki wani”
Ta yi dariya ta mike tsaye ta rufe kur'anen ta dauka ta rumgume.
“Na gode All”
Ta nufi stairs duk suka bita da kallo, Ummi na ji kamar tace mata kar ta tafi.
“Har a yanzu da ta musulumta tafiya zata ti Ummi?”
Namra ta tambaya. Sai Abiey ya amsa mata.
“Tafiyar zata fi zaman, ko ba komai zamu san yan'uwanta kuma tafiyarta ba yana nufin mu barta a can shikenan ba, no zamu bibiyeta ko dan sanin halin da take ciki, shiyasa na ce ba zata tafi ita kadai ba sai tare da jami'an tsaro, kuma Maleek zai rakata kamar yadda Ameer ya bukata, zuwa gobe zamu shirya komai jibi sai ta tafi”
“Haka ne, Allah yasan hakan ne alheri a gareta da mu gaba daya”
Ta girgiza kai alamar aa, ta juyo ya rumgume Ummi.
“Allah ya miki albarka ya tsare rayuwarki da imaninki Nuwaira”
Duk suka amsa da Ameen. Matan da Iman din ya gayyato suka gabatar da Nuwaira yadda zata yi ibada, wanka tsarkin da zata yi na shiga addinin musulunci, da kuma dokokin da suka wajaba a kanta, suka tambayeta ko akwai wata matsala da take fuska ta musallin ko abinci ko kuma wata baraza ta amsa da cewar babu ko daya. Sai da aka fara tada Sallah azahar sannan Mahmood ya dawo da su Ummi gida, Ameer da Maleek suka yi sallah a masallacin tare da Abiey.
Ummi ce ta jagoranci Nuwaira gurin nuna mata yadda zata yi wankan tsarkin, bayan ta nuna mata a waya yadda zata yi a waya sai da ta tabbatar ta iya sannan ta fita ta bata guri, Nuwaira ta yi wanka da kanta ta fito tana daure da tawul ta rufe kanta da wani. Ummi dake zaune gafen gadonta tana jiranta ta mike tsaye ta mika mata sabuwar rigar abayar da zata sauko mata har kasa.
“Wannan kyauta ce daga gareni, farkon zuwana makka na siyo rigar nan amman ban taba sakawa ba, da na aje har sai idan daya daga cikin yayana za su yi aure na ba su saboda tsadar rigar, sai dai musuluntar da kika yi a yau, ya saka kin zama ďaya daga cikin yayana, zan iya miki komai fiye da yadda zan yi musu ma”
Nuwaira ta tara hannu ta karba tana kallon Ummi dake hawaye tare da murmushi.
“Na gode, ina ma ace zan iya saka miki da duk abun da kika yi min? Hakika ke uwa ce ta gari, kin cancanci ko wane irin Award na girmamawa da karanci”
“Idan kin shirya ki fito waje yan'uwanki suna kasa suna jiranki”
Ta gyada kai sannan ta karbi rigar ta aje saman gadon. Ummin ta juya ta fice daga dakin, Hannu Nuwaira ta kai ta taba rigar yadda ta sha stone tana kyali ga yadin sai walwalniya yake yana daukar ido, kana kallon rigar kasan an zuba guri gurin siyenta. Ta dade tana kallon rigar sannan ta mike tsaye ta cire tawul dinta ta dauki rigar ta zura, daman can bata mu'alama da birejiya dan haka bata damu da neman inda take ba balle ta saka. Tana zura rigar ta dauki mayafin abayar ta rufe kanta sai ta taka gurin madubi ta kalli kanta. Dan murmushi ganin yadda dark green din abayar ta yi mata masifar kyau kai kace sarauniyar Abuja ce, tsayin rigar 58 ne ita kuma tana saka 54 ne haka ya saka rigar ta yi mata fadi da tsayi, sai dai ko kadan hakan be rage komai daga kyaunta ba. Ta saka hannu ta rike rigar tana takawa a hankali har ta isa gurin kofar ta bude ta fita, tana fara saukowa stiars idon kowa ya dawo kanta, Ameer be san lokacin da ya mike tsaye yana kallonta kamin murmushinsa ya fara yi mata marhabun da saukowa. Maleek ya kalleshi ya kalli Abiey sannan shi da Mahmood suka kalli juna, Ummi ma kallonsa ta yi kamin ta dauke ido ta kalli Nuwaira. Tsaye ta fara yi a lokacin da ta sauko har sai da Namra ta mike tsaye ta isa gurinta ta riko hannunta.
“Zo na nuna miki wani abu little Sis”
Gurin wata Laptop dake aje kan kujera Namra ta nufa da ita, suna isa ta saki hannunta ta bude laptop din ta shiga whatsapp din ta kunna video call, few seconds Shuraim yayi picking fuskarsa da murmushi, Nuwaira na ganinsa ta durkusa a gaban laptop din tana kallonsa da murmushi a fuskarta.
“Sulem...”
“Baby girl Welcome to World Of Islam, na yi matukar farinciki na jidadi a lokacin da na Namra takw fada min hukuncin da kika yanke, na yi bakinciki da bana kusa da ke, da yanzu da ni za a samu wannan ladar, amman a haka ma ina farinciki yanzu kin kallama komai duk wani abu da ake so a mace a yanzu kin hada shi”
“I miss you”
Ta fada hawaye na sauko mata.
“I miss you too baby girl, idan zan zo zan kawo miki tsaraba mai yawa kuma mai ban mamaki”
“Maybe ba zaka same ni ba, zan tafi gida gobe”
Shuraim ya dan yi jimm for some seconds sannan ya kalli Namra dake gafenta.
“Why? Akwai matsala ne Namra?”
“No ita dai take ra'ayin zuwa”
“Ina fatar ba za su cutar da ke ba”
“Nima ina fatar haka”
“Zan tare a Katsina, sai na ganki i miss you so much”
“Ina da labari da yawa da zan baka”
“Ni ma ina da labarai da yawa Baby girl ”
Ta taba hancinta ta kai hannunta ta taba jikin computer sai yayi dariya shi a ya taba hancinsa ya taba computer.
“See you”
Namra ta rufe computer, Nuwaira ta juya ta kalli Namra tana murmushi.
“Nuwaira ga wannan na san zai taimaka miki gurin Sallah saboda yanzu kika fara, yana magana kuma yana fadar duk wani tasbihi da ya kamata ki yi a cikin Sallah”
Nuwaira ta karasa kusa da Abiey ta tara hannu biyu ta karbi prayer mat din.
“Na gode”
Ta shafa carpet din dake cikin wani jacket mai kyau kamar ba prayer mat. Ameer ya tashi ya fita, Namra kuma ta shiga dakinta sai gata ta fito da katon akwaiti ta sauko da shi.
“Ban san me zan baki ba, kuma na san kayana ba su miki, so shiyasa na zabi baki tufafin da ban danka ba gasu na hada miki guri daya a akwaiti, akwai turarukan jiki da na fesawa, kuma akwai mayuka da sabulai masu kyau”
“Na gode”
Nuwaira ta yi mata godiya tana kallon madaidaicin akwatin. Kamin ta juyo ta kalli Ameer da ya mika mata box, ta karba da hannu biyu ta bude sai ta yi arba da kur'ane mai kyau. Ta bude ido ta risina kasa ta saka hannu biyu ta ciro kur'anen ta sumbanceshi sannan ta kalli Ameer idonta na cika da hawaye.
“Na gode”
Ta sakar mata murmushinsa mai matukar tsada ta warware wata yar karamar sarka ya daura mata a hannu a yayin da take rike da kur'anen, abun hannuna ne mai kyau fari mai kamar azurfa.
“Welcome to the peace”
“Thank you, duk wannan saboda kai ne Ameer”
Abiey ya mike tsaye yana fadin.
“Ameer ka yi abun a yaba, ka kyauta kuma na jidadin haka Allah ya baka lada, ya saka maka da alheri, ina fatar a yanzu ba za a sake samun matsala ko tsabanin tsakaninka da yan'uwanka ba, Allah ya hada kanku”
“Ameen”
Ya amsa yana kallon Nuwaira da ta aje kur'anen tana ta taba abun hannun da ya saka mata cikin farinciki da jindadi.
“Yayi kyau”
“Do you like it?”
Tambayarta yake tana kallonta kamar daga shi sai ita ne a falon, gaba daya ta dauke masa hankali baya ganin kowa. Ta daga alamar yes she like it kamin ta dago ta kalleshi wannan karon hakoranta a waje yake, can kuma ta juya ta kalli Mahmood da ya mika mata chocolate da carbin hannunaa yar maroko, wato counter.
“Ga wannan zaki iya yin tasbihi da ita ko salati, zata kirga miko ko adadin guda nawa kike son yi, kuma ga chocolate kowa ya baki komai ban san me zan baki ba”
“Thank you”
Ta karba ta dora saman jikinta sannan ta kalli Maleek, shi kam be roko mata komai ba domin ba sa ran su ma za su mata kyauta ba, idan ma zai bata be san wace kyautar zai bata ba. Hakan kuma ba karamin dadi yayi ma Ameer ba daman shi so yake ya zama shi kadai ne yake burge Nuwaira baya son abokin takara.
“Maybe next time ni ban riko miki komai ba”
Ta yi murmushi ta maida hankalinta gurin abun hannun da Ameer ya daura mata, ita dai tana kaunar ayi mata kyauta wani abun da ya danganci sarka ko abun hannu.
“Ameer kai ka katse min sarkar da Sulem ya ba ni ka tuna?”
“Gashi nan ai na baki wani”
Ta yi dariya ta mike tsaye ta rufe kur'anen ta dauka ta rumgume.
“Na gode All”
Ta nufi stairs duk suka bita da kallo, Ummi na ji kamar tace mata kar ta tafi.
“Har a yanzu da ta musulumta tafiya zata ti Ummi?”
Namra ta tambaya. Sai Abiey ya amsa mata.
“Tafiyar zata fi zaman, ko ba komai zamu san yan'uwanta kuma tafiyarta ba yana nufin mu barta a can shikenan ba, no zamu bibiyeta ko dan sanin halin da take ciki, shiyasa na ce ba zata tafi ita kadai ba sai tare da jami'an tsaro, kuma Maleek zai rakata kamar yadda Ameer ya bukata, zuwa gobe zamu shirya komai jibi sai ta tafi”
“Haka ne, Allah yasan hakan ne alheri a gareta da mu gaba daya”