Sashe 73
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abiey ya fada yana dariya. Maleek kuma ya kai hannu ya bude babbar kofar falon Abiey ya fara shiga sannan Maleek ya biyo baya. Falon farko babu kowa a ciki hakan ya bawa Abiey da ďansa Maleek damar shiga kofar dake cikin falon wacce zata sada su da corridor dakin Abiey ba sai sun bi ta cikin karamin falon da Namra ta sauki surikinsu ba. Abiey ya fara shiga dakinsa kai tsaye ya zauna tare da Maleek yana fadin.
“Kira Namra ka fada mata ta sanar da bakonta zamu shigo mu gaisa da shi yanzu nan”
“Abiey ba zaka huta ba?”
“Hutun me? Aiki na bari na zo nan fa kuma muna gama gaisawa zan koma”
Maleek ya ciro wayarsa dake aljihu a maimakon ya kira sai ya aika mata da sako. Abiey kuma ya kira Ummi Dr Zainab ta amsa wayar.
“Ka dawo”
“Eh ina dakina tare da Maleek”
“Toh bari idan kun gaisa da shi sai mu fito muma mu gaisa da shi”
“alright”
Ya aje wayar, after like 20 minutes Namra ta shigo dakin ta zube kasa ta gaishe da Abiey kanta a kasa tana mai jin kunyarsa abun da bata saba ba.
“Abiey na fada masa”
Mahaifinta yayi dariyar farinciki yana zolayarta daman ya saba wasa da yayansa ba maza ba matan ba balle kuma Ummi da take matarsa.
“Toh Gimbiya Namra bari mu tafi mu gaisa da Yarima”
Ta rufe ido tana dariya. Shi ma dariyar yake Maleek kam kallonsu kawai yake kamin ya mike tsaye tare da mahaifinsa suka fice daga ďakin. Shuraim na jin an taba kofar falon sai suka kara daidaita natsuwarsu domin Namra ta sanar musu mahaifinta zai shigo ya gaisa da su, kusan a tare Shuraim da abokinsa suka mika tsaye suna amsa sallamar Abiey. Maleek ne ya riga karasa inda suke ya mika musu hannu suka gaisa sannan ya zauna a kusa da inda suka zauna. Shuraim ya mikawa Abiey hannu biyu ya gaisa da shi as well as abokinsa.
“Bismillah”
Abiey ya fada yana nuna masa kujera, tsantsar ladabi da girmama na gaba ya hana Shuraim zama a saman kujera saboda Abiey ya zauna saman kujera yana ganin be dace shi ma ace yana kan kujera ba.
“Sannunku da zuwa”
Sai suka amsa da yauwa suka zauna a kasan Shuraim kansa na kasa kamar wani mace, Abiey kam kamar ya samu tv haka ya rika kallon saurayin mai shirin zama surukinsa.
“Namra ta fada mana zaka zo, saboda mun bata damar zabar wanda take so, mun yi maganganu da ita, sai dai ina tunanin yana da kyau mu kai ma ka gabatar mana da kanka, kuma ka yi hakuri da tambayoyin da zan maka”
“Ba komai Abbah, daman shiyasa na zo ai, saboda mu san juna kuma na yi bayanin kaina, idan na koma sai na sanar da iyayena su same ku da maganar ko a yanzu ma sun san da maganar sun dade da sanin Namra sai dai a yanzu ne magana mai karfi zata shigo”
Abiey ya tsuke ido yana kallon Shuraim tare da murza tsayansa daya da hannunsa kamar mai kokarin tuna wani abu.
“Sunana Muhammad Shuraim, ni likita ne ina aiki a General hospital Katsina, kuma ina dan taba aiki Peach Hospital Katsina sai dai ita Private Hospital ce, mahaifina ma likita ne sunansa Dr Hamid Muhammad iyayena yan asalin garin Kano ne, sai dai zama ya dawo da su a Katsina, na yi karatuna a jami'ar BUK na yi master a ABU zaria, kuma ina shirye shiyen fita waje domin cigaba da karatuna In Shaa Allah, ni na na farko a gidanmu ina kanwa wacce ta yi aure tana Kano akwai kuma dayar tana nan tare da mu ita ma tana kusa da yin auren In Shaa Allah, mahaifiyata tsohuwar malamar makaranta ce, yanzu kuma da ta yi ritaya tana kasuwanci na tufafi da kayan shafe shafe na mata”
“Kai ďan wajen Dr Hamid ne?”
Abiey ya tambaya yana nunashi daman zuciyarsa ta raya masa haka tun shigowarsu ta farko a falon da yayi arba da fuskarsa.
“Eh ni dansa ne”
Maleek ya kalli Mahaifinsa.
“Kama san mahaifinsa kenan Abiey?”
“Ni kuwa na san Dr Hamid farin sani, daman ina ganin fuskarka na san cewa kai dansa ne”
Cikin yanayi na rashin jindadi Abiey yayi maganar yana kebe baki ya girgiza kai. Sannan ya kalli Maleek ya ce.
“Kira mahaifiyarku tare da Dr ta zo su ganshi”
Maleek ya tashi ya fice, Shuraim kuma ya dan dago ya kalli Abiey da ya tsare shi da ido irin kallon da ke nuna ba a maraba da kai, suka hada ido da abokinsa ya sauke kansa kasa yana jin wani iri, domin dai be san shi ko mahaifinsa da wani abun da za a nuna shi ba, ba kuma mamakin jin cewar Abiey ya san shi yake ba domin mahaifinsa kwararen likita kamin jinya ta ci karfinsa wata kila shi ma ya san mahaifinsa ne da hanyar aikin da mahaifinsa yake. Kusan gaba daya suka shigo falon ban da Jabir da baya gidan sai kuma Umar dake can dakin Mahmood yana safgar gabansa, Dr Zainab da Mahmood sai Ummi da Waira ke bayanta ita kuma tana covering din face dinta saboda kukan da ta yi, Yesmin da Juwairiyyya suka shigo daga karshe Maleek na bayansu. Waira na hango Shuraim ta bar gurin Ummi ta nufi inda yake ta zauna jikinta na gogar nasa, ta saka hannunta ta kama hanshi hannun ta danka mishi takardar daya rubuta mata kuma ta lakame hannu. Kunya da ganin kamar hakan be dace ba ya saka ya matsa ya cire hannunsa cikin nata sai ta kara matsowa daman can a a'adarsu zama a kusa da wanda ba muharraminsu ba ko taba shi ba wani abun zunubi ko laifi ba ne a gurinsu. Idonta ya rufe bata ganin kowa a falon sai Sulem dinta yadda take washe hakora ma kadai ya isa ya fahimtar da mutun cewar akwai kyakkyawar alaka tsakaninsu, yana matsawa sai itama ta matsa ta kama hannunsa zata rike sai ya fisge. Dukawa ta yi zata leke fuskarsa Maleek ya daka mata tsawar da sai da yawun bakinta suka tsarke ta fara tari babu shiri.
“Ke.... Waira... Me yasa baki da hankali wai? Tashi daga nan ko na takaki get out”
Ta mike tsaye da sauri hawaye na zuba tari na zo mata kamar wacce ta taba taji, a take Shuraim ya ji ba dadi ya dago ya kalli Maleek da fuskarsa ke daure yana watsawa Waira harara. Rikice ta nufi gurin Ummi Maleek ya sake daka mata tsawa data saka ta fashewa da kuka mai karfi.
“Get out na ce, na rantse da Allah sai kin fita”
Ta kalli Shuraim ta fice da sauri jikinta na rawa. Ummi bata cikin yanayin mai dadi hakan ya saka bata ce komai ba, ita ma kuma ta san abun da Waira take yi be dace ba.
“Ai ba laifinta ba ne, tun da ba a koya mata addini ba, yarinyar da bata san halak da haram ba? Bata san Allah da ma'aikinsa ba, Kai ta san ka ne?”
“Eh ni ne likitan da ya karbe ta a lokacin da aka kawo ta asibiti maciji ya cijeta, dan sabu da nine a lokacin”
Shuraim ya amsa cikin muryar dake nuna be jidadin abun da aka yi ma Waira ba, kuma yana son sanin abubuwa da yawa a game da zamanta a gidan da kuma alakarsu. Abiey ya kalli Ummi yana nuna Shuraim.
“Ga ďan Dr Hamid yarki ta kawo mana a matsayin wanda zata aura, kamar dai Nimra”
Ummi ta yi gyaran murya ta ce.
“Maa Shaa Allah, muna maraba da hakan ga dukan alamu yaro ne mai hankali da tarbiya, kuma muna fatan abun da muka gani a fuska mu jishi a zahiri idan mun bincika, idan akwai alheri aurenka da Namra, Allah ya saukar da natsuwa da kwanciyar hankali da fahimtar juna a tsakaninmu da kuma kai da ita, idan kuma babu alheri Allah shi ne mafi sanin daidai ina fatar rabuwa ta zo cikin mutunci da aminci ba tare da an cutar da juna ba”
Yanayi maganar farko ta Abiey da kuma amsar da Ummi ta biyo baya da ita ya karantar da shi cewar akwai wani abu da be sani ba kuma suke kallonsa da shi. Kowa ya amsa da Ameen a falon har shi sannan ya dago ya kalli Dr Zainab dake tambayarsa mahaifinsa.
“Tana nan, ya bar aiki yanzu saboda shekaru sun ja kuma yana fama da ciwon sashe ba komai yake iya yi ma kansa da kuma spinal cord injury”
“Dole...”
Abiey ya fada sai duk suka kalleshi har Ummi dake kokarin nuna masa abun da yake ba daidai ba ne da ido, balle kuma Maleek da Mahmood da ba su fahimci komai ba, Shuraim ma kallon Abiey yayi da karshen zancensa ya biyo tare da kora da hali.
“Mun gode sosai da gabatar da kai Shuraim sai ka ji daga garemu”
Abiey ya mike tsaye ya fice daga falon, Ummi ta bi bayansa. Abiey na shiga dakin ta rufe shi da fada.
“Abun da ka aikata be kamata, yaron nan be san abun da mahaifinsa ya aikata ba, kuma be kamata laifin mahaifinsa ya shafe shi ba”
“Toh me kike tunani? Na bada yata aure ga zuri'ar Dr Hamid? Ko kin manta waye shi?”
“Kai da kake kokarin ganin sirrin nan be fita ba, kuma kai zaka ce ba zaka aurawa yarka wanda take so ba, saboda laifin da bana jin yaron nan ya san mahaifinsa ya aikata”
“Kika san wane kalar hali da shi? Ana son idan zaka yi aure ka zabawa yarka miji na gari”
“To me ye aibun Shuraim? Karka rusa farincikin Namra saboda wani selfish interest na ka, Nimra ta yi kuskure kuma addini ya haramta aurenta da Ameer amman Namra fa? To kake duk yaran su taro suna mana kallon azzalumai? Ka fi kowa sanin meye so karka saka yarka a damuwa saboda abun da wani ya aikata, Namra tana son yaron nan kuma idan har bincike ya tabbatar da ba shi da matsala za mu aura mata shi”
“Kira Namra ka fada mata ta sanar da bakonta zamu shigo mu gaisa da shi yanzu nan”
“Abiey ba zaka huta ba?”
“Hutun me? Aiki na bari na zo nan fa kuma muna gama gaisawa zan koma”
Maleek ya ciro wayarsa dake aljihu a maimakon ya kira sai ya aika mata da sako. Abiey kuma ya kira Ummi Dr Zainab ta amsa wayar.
“Ka dawo”
“Eh ina dakina tare da Maleek”
“Toh bari idan kun gaisa da shi sai mu fito muma mu gaisa da shi”
“alright”
Ya aje wayar, after like 20 minutes Namra ta shigo dakin ta zube kasa ta gaishe da Abiey kanta a kasa tana mai jin kunyarsa abun da bata saba ba.
“Abiey na fada masa”
Mahaifinta yayi dariyar farinciki yana zolayarta daman ya saba wasa da yayansa ba maza ba matan ba balle kuma Ummi da take matarsa.
“Toh Gimbiya Namra bari mu tafi mu gaisa da Yarima”
Ta rufe ido tana dariya. Shi ma dariyar yake Maleek kam kallonsu kawai yake kamin ya mike tsaye tare da mahaifinsa suka fice daga ďakin. Shuraim na jin an taba kofar falon sai suka kara daidaita natsuwarsu domin Namra ta sanar musu mahaifinta zai shigo ya gaisa da su, kusan a tare Shuraim da abokinsa suka mika tsaye suna amsa sallamar Abiey. Maleek ne ya riga karasa inda suke ya mika musu hannu suka gaisa sannan ya zauna a kusa da inda suka zauna. Shuraim ya mikawa Abiey hannu biyu ya gaisa da shi as well as abokinsa.
“Bismillah”
Abiey ya fada yana nuna masa kujera, tsantsar ladabi da girmama na gaba ya hana Shuraim zama a saman kujera saboda Abiey ya zauna saman kujera yana ganin be dace shi ma ace yana kan kujera ba.
“Sannunku da zuwa”
Sai suka amsa da yauwa suka zauna a kasan Shuraim kansa na kasa kamar wani mace, Abiey kam kamar ya samu tv haka ya rika kallon saurayin mai shirin zama surukinsa.
“Namra ta fada mana zaka zo, saboda mun bata damar zabar wanda take so, mun yi maganganu da ita, sai dai ina tunanin yana da kyau mu kai ma ka gabatar mana da kanka, kuma ka yi hakuri da tambayoyin da zan maka”
“Ba komai Abbah, daman shiyasa na zo ai, saboda mu san juna kuma na yi bayanin kaina, idan na koma sai na sanar da iyayena su same ku da maganar ko a yanzu ma sun san da maganar sun dade da sanin Namra sai dai a yanzu ne magana mai karfi zata shigo”
Abiey ya tsuke ido yana kallon Shuraim tare da murza tsayansa daya da hannunsa kamar mai kokarin tuna wani abu.
“Sunana Muhammad Shuraim, ni likita ne ina aiki a General hospital Katsina, kuma ina dan taba aiki Peach Hospital Katsina sai dai ita Private Hospital ce, mahaifina ma likita ne sunansa Dr Hamid Muhammad iyayena yan asalin garin Kano ne, sai dai zama ya dawo da su a Katsina, na yi karatuna a jami'ar BUK na yi master a ABU zaria, kuma ina shirye shiyen fita waje domin cigaba da karatuna In Shaa Allah, ni na na farko a gidanmu ina kanwa wacce ta yi aure tana Kano akwai kuma dayar tana nan tare da mu ita ma tana kusa da yin auren In Shaa Allah, mahaifiyata tsohuwar malamar makaranta ce, yanzu kuma da ta yi ritaya tana kasuwanci na tufafi da kayan shafe shafe na mata”
“Kai ďan wajen Dr Hamid ne?”
Abiey ya tambaya yana nunashi daman zuciyarsa ta raya masa haka tun shigowarsu ta farko a falon da yayi arba da fuskarsa.
“Eh ni dansa ne”
Maleek ya kalli Mahaifinsa.
“Kama san mahaifinsa kenan Abiey?”
“Ni kuwa na san Dr Hamid farin sani, daman ina ganin fuskarka na san cewa kai dansa ne”
Cikin yanayi na rashin jindadi Abiey yayi maganar yana kebe baki ya girgiza kai. Sannan ya kalli Maleek ya ce.
“Kira mahaifiyarku tare da Dr ta zo su ganshi”
Maleek ya tashi ya fice, Shuraim kuma ya dan dago ya kalli Abiey da ya tsare shi da ido irin kallon da ke nuna ba a maraba da kai, suka hada ido da abokinsa ya sauke kansa kasa yana jin wani iri, domin dai be san shi ko mahaifinsa da wani abun da za a nuna shi ba, ba kuma mamakin jin cewar Abiey ya san shi yake ba domin mahaifinsa kwararen likita kamin jinya ta ci karfinsa wata kila shi ma ya san mahaifinsa ne da hanyar aikin da mahaifinsa yake. Kusan gaba daya suka shigo falon ban da Jabir da baya gidan sai kuma Umar dake can dakin Mahmood yana safgar gabansa, Dr Zainab da Mahmood sai Ummi da Waira ke bayanta ita kuma tana covering din face dinta saboda kukan da ta yi, Yesmin da Juwairiyyya suka shigo daga karshe Maleek na bayansu. Waira na hango Shuraim ta bar gurin Ummi ta nufi inda yake ta zauna jikinta na gogar nasa, ta saka hannunta ta kama hanshi hannun ta danka mishi takardar daya rubuta mata kuma ta lakame hannu. Kunya da ganin kamar hakan be dace ba ya saka ya matsa ya cire hannunsa cikin nata sai ta kara matsowa daman can a a'adarsu zama a kusa da wanda ba muharraminsu ba ko taba shi ba wani abun zunubi ko laifi ba ne a gurinsu. Idonta ya rufe bata ganin kowa a falon sai Sulem dinta yadda take washe hakora ma kadai ya isa ya fahimtar da mutun cewar akwai kyakkyawar alaka tsakaninsu, yana matsawa sai itama ta matsa ta kama hannunsa zata rike sai ya fisge. Dukawa ta yi zata leke fuskarsa Maleek ya daka mata tsawar da sai da yawun bakinta suka tsarke ta fara tari babu shiri.
“Ke.... Waira... Me yasa baki da hankali wai? Tashi daga nan ko na takaki get out”
Ta mike tsaye da sauri hawaye na zuba tari na zo mata kamar wacce ta taba taji, a take Shuraim ya ji ba dadi ya dago ya kalli Maleek da fuskarsa ke daure yana watsawa Waira harara. Rikice ta nufi gurin Ummi Maleek ya sake daka mata tsawa data saka ta fashewa da kuka mai karfi.
“Get out na ce, na rantse da Allah sai kin fita”
Ta kalli Shuraim ta fice da sauri jikinta na rawa. Ummi bata cikin yanayin mai dadi hakan ya saka bata ce komai ba, ita ma kuma ta san abun da Waira take yi be dace ba.
“Ai ba laifinta ba ne, tun da ba a koya mata addini ba, yarinyar da bata san halak da haram ba? Bata san Allah da ma'aikinsa ba, Kai ta san ka ne?”
“Eh ni ne likitan da ya karbe ta a lokacin da aka kawo ta asibiti maciji ya cijeta, dan sabu da nine a lokacin”
Shuraim ya amsa cikin muryar dake nuna be jidadin abun da aka yi ma Waira ba, kuma yana son sanin abubuwa da yawa a game da zamanta a gidan da kuma alakarsu. Abiey ya kalli Ummi yana nuna Shuraim.
“Ga ďan Dr Hamid yarki ta kawo mana a matsayin wanda zata aura, kamar dai Nimra”
Ummi ta yi gyaran murya ta ce.
“Maa Shaa Allah, muna maraba da hakan ga dukan alamu yaro ne mai hankali da tarbiya, kuma muna fatan abun da muka gani a fuska mu jishi a zahiri idan mun bincika, idan akwai alheri aurenka da Namra, Allah ya saukar da natsuwa da kwanciyar hankali da fahimtar juna a tsakaninmu da kuma kai da ita, idan kuma babu alheri Allah shi ne mafi sanin daidai ina fatar rabuwa ta zo cikin mutunci da aminci ba tare da an cutar da juna ba”
Yanayi maganar farko ta Abiey da kuma amsar da Ummi ta biyo baya da ita ya karantar da shi cewar akwai wani abu da be sani ba kuma suke kallonsa da shi. Kowa ya amsa da Ameen a falon har shi sannan ya dago ya kalli Dr Zainab dake tambayarsa mahaifinsa.
“Tana nan, ya bar aiki yanzu saboda shekaru sun ja kuma yana fama da ciwon sashe ba komai yake iya yi ma kansa da kuma spinal cord injury”
“Dole...”
Abiey ya fada sai duk suka kalleshi har Ummi dake kokarin nuna masa abun da yake ba daidai ba ne da ido, balle kuma Maleek da Mahmood da ba su fahimci komai ba, Shuraim ma kallon Abiey yayi da karshen zancensa ya biyo tare da kora da hali.
“Mun gode sosai da gabatar da kai Shuraim sai ka ji daga garemu”
Abiey ya mike tsaye ya fice daga falon, Ummi ta bi bayansa. Abiey na shiga dakin ta rufe shi da fada.
“Abun da ka aikata be kamata, yaron nan be san abun da mahaifinsa ya aikata ba, kuma be kamata laifin mahaifinsa ya shafe shi ba”
“Toh me kike tunani? Na bada yata aure ga zuri'ar Dr Hamid? Ko kin manta waye shi?”
“Kai da kake kokarin ganin sirrin nan be fita ba, kuma kai zaka ce ba zaka aurawa yarka wanda take so ba, saboda laifin da bana jin yaron nan ya san mahaifinsa ya aikata”
“Kika san wane kalar hali da shi? Ana son idan zaka yi aure ka zabawa yarka miji na gari”
“To me ye aibun Shuraim? Karka rusa farincikin Namra saboda wani selfish interest na ka, Nimra ta yi kuskure kuma addini ya haramta aurenta da Ameer amman Namra fa? To kake duk yaran su taro suna mana kallon azzalumai? Ka fi kowa sanin meye so karka saka yarka a damuwa saboda abun da wani ya aikata, Namra tana son yaron nan kuma idan har bincike ya tabbatar da ba shi da matsala za mu aura mata shi”