Sashe 93
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Waira ta fada itama tana hawaye ganin uwar dakinta na kuka. Ta madubin gaban mota ya kalleta da hawayen da take ita ma ta kalleshi, be sake cewa komai ba ja motar. Be tsaya ko'ina ba sai a bakin gate din gidansu Ameer ba zai iya shiga ciki ba dan haka ya faka motar a waje. Ya fito ya budewa Ummi ta fito tana gyara hijabinta mai 3 in 1, Waira ta bude side dinta ta fito ita da Ummi suka doshi gate din gidan. Masu gadin na ganinsu ya mike tsaye ya bude musu gate ana musu sannu da zuwa, Maleek binsu yayi da kallo har suka shige sannan ya koma cikin motar wani irin zafin zuciya na dibarsa. Suna shiga harabar gidan Waira ta jiyo busar sarewar irin wacce Eid yake mata a garinsu, busar da babu wanda iya ta sai Eid busar da aka kirkira da tsafi, wanda wani be isa ya kwaikwaya ba, balle har ya iya. A firgice ta saki hannun Ummi ta falla da gudu sai kuma ta ja ta tsaya tana kallon gabas da yamma ta juyo ta kalli nan ta kalli can ta rasa ta ina busar take fitowa. Kara matsawa ta yi compound din sai ta jiyo sautin na fita ta wani gurin da take kyautata zaton Garden ne, da gudu ta nufi gurin tana jefar da mayafin kanta tana kuka marar sauti hawaye sharrr kamar an sako teku...
[7/5, 9:39 PM] My S Line: 48
Ummi har ta yi kamar ta bi bayan Waira sai kuma wata zuciyarta tace mata focus on abun da ya kawo ki gidan nan, dan haka bata damu ta bi bayan Waira ko kuma ta san abun da take yi ma gudu ba, sai ta nufi kofar shiga cikin gidan domin yin abun da ya kawota. Door bell din ta fara danna tare da gyara tsayuwarta, gabanta faduwa yake sosai domin bata taba risking aikata wani abu kamar wannan ba. Wata matashiyar yarinya ce ta bude mata kofar sai ta tsaya tana kallonta ganin bakuwar fuska.
“Mahaifiyarki tana ciki? Ko Ameer”
“Duka suna nan shigo”
Ta kauce daga jikin kofar Ummi tayi taking deep breaths sannan ta saka kafarta cikin falon. Katon hoton Ameer da aka zana da art ya fara mata maraba da zuwa, bata bukatar izinin zama dan haka ta zauna a daya daga cikin kujerun da suka fi kusa da ita. One after the other ta bi hotunan da suke falon da kallo cikin har da wanda Mr Bashir ya dauka tare da Ameer da kuma wanda suka yi a matsayin iyali daya da Mommy da yaranta.
“Bakuwa muka yi?”
Mommy ta fada tana saukowa a yayinda take yi ma Ummi kallon rashin sani. Ummi ta juyo ta kalli stairs fuskarta cike da damuwa.
“Eh Sannu Hajiya”
“Yauwa sannu da zuwa”
Mommy ta amsa sannan ta sauko gaba daya ta zauna a kujerar dake fuskantar wadda Ummi ta zauna.
“Sai dai ban wayance ki ba”
“Ba lallai ki san ni ba, Sunana Zahra, na zo gurin Ameer ne, ko yana ciki?”
Mommy ta kara kallonta da kyau domin tantancewa.
“Eh toh amman ba zaki iya magana da shi kai tsaye ba, ya kamata ki fara neman izini gurin mahaifinsa tukuna”
Ummi ta yi shiru tana tsoron kar a hana ta ganin ďanta.
“Na zo ganinsa ne kawai ba wani abun tashin hankalin zan haifar ba”
“Waya fada miki ba shi da lafiya?”
“Zuciyata ce, na ji bana da natsuwa har sai na zo na duba shi”
“Duk da haka dai, ni da shi duka muna karkashin kulawar Mai gidan ne, be kamata na yanke hukunci ba tare da saninsa ba, ko da kuwa baya kusa balle ma yana cikin gidan saboda yau weekend ne, bari na kira shi ku yi magana tukuna”
Ummi ta amsa mata da kai, zuciyarta na raya mata Mr Bashir ba zai bari ta ga Ameer ba. Mommy ta tashi ta nufi wata kofar sai kuma ta juyo ta kalli Ummi.
“Ke ce matar da aka ce kin ce Ameer ďanki ne?”
“Ba ance ba ne, Ameer ďana ne zan iya tutuya da fadar hakan a gaban kowa”
Ummi ta amsa mata kai tsaye ba tare da ka kalleta ba. Mommy ta sauke ajiyar zuciya ta fice daga falon. Bayan ficewar Mommy Ummi ta dora jakarta a kan kujera tana ta sake sake a ranta. Ummi ta yi zaman da kai minti ashirin a falon sannan ta ji muryar Mr Bashir kamar daga sama.
“Ban yi zaton na karya daya daga cikin alkawuran da na daukar miki ba, me zai saka ki bada kyautar da zaki dawo daga baya ki tambaya”
Ummi ta juyo tana kallon Mr Bashir da ya tunkarota fuskarsa dauke da damuwa, duk yadda ya shirya yin fada da Zahra da yi mata barazana da duk wani abun bacin rai sai ya ji lagunsa ya karye a lokacin da kalli fuskarta, kwarjininta ya cika idonsa har ya ji kamar yana gudun bata mata rai.
“Ni ban yi zaton zan tambaya ba, fadar gaskiya ko kuma bayyana ta baya nufin canja komai daga alakarku da Ameer, kawai dai ina son na yi duty na a matsayina na uwarsa, ina son na gyara komai kamar yadda na bata”
Mr Bashir ya kalli Mommy bayan ya zauna.
“Ba mu guri”
Ta mike tsaye ta haye sama, sai da Daddy ya tabbatar ta shige dakinta sannan ya kalli Zahra ya ce.
“Wani ya taba kai miki gulmar Ameer ya rasa wani na gata ko kewa daga uwa?”
Ta girgiza kai.
“Aa na kasa jurewa ne, fiye da yadda ka kasa jurewa a yanzu da kake ganin kamar zan rabaka da shi ne, kai kenan balle kuma ni da nake uwa? A ko wane dare ina kwana da kaunar Ameer a raina da kewarsa, na baka amanarsa ne saboda ma gamsu zaka kula da shi, bayan na yi hakan kuma zuciyata ta kasa natsuwa da abun da na aikata, na cutar da wasu domin ba ni kadai nake da hakki da Ameer ba, tsoron hukuncin da zai biyo baya da kuma kurciya a wacan lokacin na cewar idan suka san na siyar musu da jika, kuma ina ganin kiyayyar ďana a cikin idon mijin da nake aure a wacan lokaci shiya karya min guiwar duk wani buri da nake da shi, kai ma zai taba mutumcinka shiyasa na bar komai ya tafi kamar yadda muka tsara, ban yi zaton Allah zai sake dawo da Ameer a kusa da inda zan ganshi ba, sai gashi ya kulla alaka da ďan'uwansa kuma ya zaunar da mu a gari daya, na furta masa hakan ne a lokacin da hankali ya gushe saboda abun da ya aikatawa yarinyar da na yi riko kuma na shayar da ita da nono na, wanda sanin kanka babu aure a tsakaninsu, duk abun da ba mu sani ba, Ameer daman ba son ta yake ba, kawai ya shirya hakan ne saboda ya dauki fansa na gabar dake tsakaninsa da Maleek, sai kuma aka yi daidai da ajali, ya fada mata gaskiya a lokacin da zuciyarta ta kasa dauka har sai da zuciyarta ta buga aka kwantar da ita asibiti, kuma rai yayi halinsa mai ajiya ya karba jiya aka yi sadakan ukun”
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un
Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un
Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Shi ne abun da yake ta fita a bakin Daddy ya cire hular kansa ya dafe kansa, Ummi ta sauke kanta kasa tana hawaye.
“Da ace Ameer ya aureta, ko sun aikata wani kuskuren laifin waye? A yanzu ma da ta rasu laifin waye? Kai ma uba ne ka bude zuciyarta ka kalli yadda zaka ji idan hakan ya faru da kai, Maleek da Ameer gaba suke da junansu bayan kuma su yan'uwan juna ne, idan na fadi na mutu a yau wace amsa zan bawa Allah? Na aikata abun da na aikata ne saboda ina tunanin mahaifinsa zai rayu, na aikata saboda ba ni da mafita, talauci ne silar komai a yanzu kuma ba arzikinka nake so ba, so nake na gyara komai ina da wasu yayan kuma mai arziki nake aure a yanzu idan har saboda kudi ne to me zai saka na yo haka? Me na rasa? Ina ta kokarin kaucewa amman kaddara ta rubuta haka, shiyasa har Nimra ta gabatar mana da Ameer a maysayin wanda take son aure, bayan shi yar'uwarta Namra kuma ta gabatar mana da ďan likitan da yayi min hanyar ganin Hajiya Jamila wato yayanta a matsayin wanda take son aure, me ka gani shim ke kamata mu bawa kaddara damar rubuta abun da ta tsara akan mu ba? Idan na kauce wannan to abun nawa ya zama son kai, dan Allah ka ba ni dama ni ma na wanzu a rayuwar Ameer ya kalleni a uwa kamar yadda yake kallonka a mahaifi”
Ummi ta karasa tana saukowa daga kan kujera ta zube kasa kamar zata roke shi. Sai yayi saurin mikewa tsaye ya girgiza kai.
“Ameer be yi lalacewar da uwar da ta haife shi zata duka ta roki wani abu ba, idan har wani zai tsuguna ya roki wata alfarma to ni ya dace na duka na yi miki godiya kuma ya roki Alfarmar ki bar Ameer ya cigaba da zama a matsayin ďana, dan Allah koma ki zauna”
Ummi ta tashi ta zauna kan kujerar, Mr Bashir ya zauna a karo na biyu yana kallon fuskarta tausayinta shimfide a fuskarsa.
“Allah ya mata rahma, hakika ban tarbiyar da Ameer da wata kalar tarbiyar makamanciyar wannan ba, sai dai rayuwa da kuma jarrabawa babu ta inda bata zuwa, ni kaina halayen Ameer sun jefa ni a cikin damuwa kala kala, sai dai be kara min komai ba sai kaunarsa, a da ina ganin kamar kin yi hakan ne saboda ki yake ni, sai dai a yanzu na fahimci ba mu isa mu yi ma Allah wayo ba, kuma Ameer deserve to know the truth, My condolences”
“Ameen”
Ummi ta amsa tana share hawayenta.
[7/5, 9:39 PM] My S Line: 48
Ummi har ta yi kamar ta bi bayan Waira sai kuma wata zuciyarta tace mata focus on abun da ya kawo ki gidan nan, dan haka bata damu ta bi bayan Waira ko kuma ta san abun da take yi ma gudu ba, sai ta nufi kofar shiga cikin gidan domin yin abun da ya kawota. Door bell din ta fara danna tare da gyara tsayuwarta, gabanta faduwa yake sosai domin bata taba risking aikata wani abu kamar wannan ba. Wata matashiyar yarinya ce ta bude mata kofar sai ta tsaya tana kallonta ganin bakuwar fuska.
“Mahaifiyarki tana ciki? Ko Ameer”
“Duka suna nan shigo”
Ta kauce daga jikin kofar Ummi tayi taking deep breaths sannan ta saka kafarta cikin falon. Katon hoton Ameer da aka zana da art ya fara mata maraba da zuwa, bata bukatar izinin zama dan haka ta zauna a daya daga cikin kujerun da suka fi kusa da ita. One after the other ta bi hotunan da suke falon da kallo cikin har da wanda Mr Bashir ya dauka tare da Ameer da kuma wanda suka yi a matsayin iyali daya da Mommy da yaranta.
“Bakuwa muka yi?”
Mommy ta fada tana saukowa a yayinda take yi ma Ummi kallon rashin sani. Ummi ta juyo ta kalli stairs fuskarta cike da damuwa.
“Eh Sannu Hajiya”
“Yauwa sannu da zuwa”
Mommy ta amsa sannan ta sauko gaba daya ta zauna a kujerar dake fuskantar wadda Ummi ta zauna.
“Sai dai ban wayance ki ba”
“Ba lallai ki san ni ba, Sunana Zahra, na zo gurin Ameer ne, ko yana ciki?”
Mommy ta kara kallonta da kyau domin tantancewa.
“Eh toh amman ba zaki iya magana da shi kai tsaye ba, ya kamata ki fara neman izini gurin mahaifinsa tukuna”
Ummi ta yi shiru tana tsoron kar a hana ta ganin ďanta.
“Na zo ganinsa ne kawai ba wani abun tashin hankalin zan haifar ba”
“Waya fada miki ba shi da lafiya?”
“Zuciyata ce, na ji bana da natsuwa har sai na zo na duba shi”
“Duk da haka dai, ni da shi duka muna karkashin kulawar Mai gidan ne, be kamata na yanke hukunci ba tare da saninsa ba, ko da kuwa baya kusa balle ma yana cikin gidan saboda yau weekend ne, bari na kira shi ku yi magana tukuna”
Ummi ta amsa mata da kai, zuciyarta na raya mata Mr Bashir ba zai bari ta ga Ameer ba. Mommy ta tashi ta nufi wata kofar sai kuma ta juyo ta kalli Ummi.
“Ke ce matar da aka ce kin ce Ameer ďanki ne?”
“Ba ance ba ne, Ameer ďana ne zan iya tutuya da fadar hakan a gaban kowa”
Ummi ta amsa mata kai tsaye ba tare da ka kalleta ba. Mommy ta sauke ajiyar zuciya ta fice daga falon. Bayan ficewar Mommy Ummi ta dora jakarta a kan kujera tana ta sake sake a ranta. Ummi ta yi zaman da kai minti ashirin a falon sannan ta ji muryar Mr Bashir kamar daga sama.
“Ban yi zaton na karya daya daga cikin alkawuran da na daukar miki ba, me zai saka ki bada kyautar da zaki dawo daga baya ki tambaya”
Ummi ta juyo tana kallon Mr Bashir da ya tunkarota fuskarsa dauke da damuwa, duk yadda ya shirya yin fada da Zahra da yi mata barazana da duk wani abun bacin rai sai ya ji lagunsa ya karye a lokacin da kalli fuskarta, kwarjininta ya cika idonsa har ya ji kamar yana gudun bata mata rai.
“Ni ban yi zaton zan tambaya ba, fadar gaskiya ko kuma bayyana ta baya nufin canja komai daga alakarku da Ameer, kawai dai ina son na yi duty na a matsayina na uwarsa, ina son na gyara komai kamar yadda na bata”
Mr Bashir ya kalli Mommy bayan ya zauna.
“Ba mu guri”
Ta mike tsaye ta haye sama, sai da Daddy ya tabbatar ta shige dakinta sannan ya kalli Zahra ya ce.
“Wani ya taba kai miki gulmar Ameer ya rasa wani na gata ko kewa daga uwa?”
Ta girgiza kai.
“Aa na kasa jurewa ne, fiye da yadda ka kasa jurewa a yanzu da kake ganin kamar zan rabaka da shi ne, kai kenan balle kuma ni da nake uwa? A ko wane dare ina kwana da kaunar Ameer a raina da kewarsa, na baka amanarsa ne saboda ma gamsu zaka kula da shi, bayan na yi hakan kuma zuciyata ta kasa natsuwa da abun da na aikata, na cutar da wasu domin ba ni kadai nake da hakki da Ameer ba, tsoron hukuncin da zai biyo baya da kuma kurciya a wacan lokacin na cewar idan suka san na siyar musu da jika, kuma ina ganin kiyayyar ďana a cikin idon mijin da nake aure a wacan lokaci shiya karya min guiwar duk wani buri da nake da shi, kai ma zai taba mutumcinka shiyasa na bar komai ya tafi kamar yadda muka tsara, ban yi zaton Allah zai sake dawo da Ameer a kusa da inda zan ganshi ba, sai gashi ya kulla alaka da ďan'uwansa kuma ya zaunar da mu a gari daya, na furta masa hakan ne a lokacin da hankali ya gushe saboda abun da ya aikatawa yarinyar da na yi riko kuma na shayar da ita da nono na, wanda sanin kanka babu aure a tsakaninsu, duk abun da ba mu sani ba, Ameer daman ba son ta yake ba, kawai ya shirya hakan ne saboda ya dauki fansa na gabar dake tsakaninsa da Maleek, sai kuma aka yi daidai da ajali, ya fada mata gaskiya a lokacin da zuciyarta ta kasa dauka har sai da zuciyarta ta buga aka kwantar da ita asibiti, kuma rai yayi halinsa mai ajiya ya karba jiya aka yi sadakan ukun”
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un
Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un
Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Shi ne abun da yake ta fita a bakin Daddy ya cire hular kansa ya dafe kansa, Ummi ta sauke kanta kasa tana hawaye.
“Da ace Ameer ya aureta, ko sun aikata wani kuskuren laifin waye? A yanzu ma da ta rasu laifin waye? Kai ma uba ne ka bude zuciyarta ka kalli yadda zaka ji idan hakan ya faru da kai, Maleek da Ameer gaba suke da junansu bayan kuma su yan'uwan juna ne, idan na fadi na mutu a yau wace amsa zan bawa Allah? Na aikata abun da na aikata ne saboda ina tunanin mahaifinsa zai rayu, na aikata saboda ba ni da mafita, talauci ne silar komai a yanzu kuma ba arzikinka nake so ba, so nake na gyara komai ina da wasu yayan kuma mai arziki nake aure a yanzu idan har saboda kudi ne to me zai saka na yo haka? Me na rasa? Ina ta kokarin kaucewa amman kaddara ta rubuta haka, shiyasa har Nimra ta gabatar mana da Ameer a maysayin wanda take son aure, bayan shi yar'uwarta Namra kuma ta gabatar mana da ďan likitan da yayi min hanyar ganin Hajiya Jamila wato yayanta a matsayin wanda take son aure, me ka gani shim ke kamata mu bawa kaddara damar rubuta abun da ta tsara akan mu ba? Idan na kauce wannan to abun nawa ya zama son kai, dan Allah ka ba ni dama ni ma na wanzu a rayuwar Ameer ya kalleni a uwa kamar yadda yake kallonka a mahaifi”
Ummi ta karasa tana saukowa daga kan kujera ta zube kasa kamar zata roke shi. Sai yayi saurin mikewa tsaye ya girgiza kai.
“Ameer be yi lalacewar da uwar da ta haife shi zata duka ta roki wani abu ba, idan har wani zai tsuguna ya roki wata alfarma to ni ya dace na duka na yi miki godiya kuma ya roki Alfarmar ki bar Ameer ya cigaba da zama a matsayin ďana, dan Allah koma ki zauna”
Ummi ta tashi ta zauna kan kujerar, Mr Bashir ya zauna a karo na biyu yana kallon fuskarta tausayinta shimfide a fuskarsa.
“Allah ya mata rahma, hakika ban tarbiyar da Ameer da wata kalar tarbiyar makamanciyar wannan ba, sai dai rayuwa da kuma jarrabawa babu ta inda bata zuwa, ni kaina halayen Ameer sun jefa ni a cikin damuwa kala kala, sai dai be kara min komai ba sai kaunarsa, a da ina ganin kamar kin yi hakan ne saboda ki yake ni, sai dai a yanzu na fahimci ba mu isa mu yi ma Allah wayo ba, kuma Ameer deserve to know the truth, My condolences”
“Ameen”
Ummi ta amsa tana share hawayenta.