Sashe 70
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya rubuta daga karshe, Ummi ta mikawa Dr Zainab takardar ita ma ta karanta sannan Waira ta karba ta nade a hannunta ta tashi tsaye ta fito dakin, so take ta je ta nunawa Sulem bata jefar da takardar da ya bata ba, tana nufo Stairs ta fara saukowa dai ga Maleek ya fara haurowa sai ta juya da sauri ta koma. Mahmood dake zaune yana hangen abun da ke faruwa ya saka dariya yanayin yadda ta juya ta koma din da sauri ya nuna tsoron Maleek take. Bata shiga dakinta da Ummi take ciki ba sai ta shige bedroom din Ummi da babu kowa a ciki a zatonta Maleek zai yi magana da Ummi ne ko kuma dakinsa zai tafi. Tsayawa ta yi a dakin tana sauraren idan ya wuce sai ta fito, shi kuma hango Ummi da yayi a dakin Waira kasancewar kofar a bude take, sai yayi reverse ya dawo baya. Kamin ya tura kofar dakin Ummi sai Waira ta bude masa a zatonta ya wuce ita kuma ta fito, ita da shi duk suna rike da kofar ne, ita zata bude ta fita shi kuma zai tura ya shiga. Sakin kofar ta yi ta matsa baya shi kuma ya samu damar shigowa ya rufe kofar. Ba saboda ita ya shigo ba amman hakan be yana shi yi mata ishara data zauna da ido ba. Ta nufi gefen gadon Ummi ta zauna a kasa tana kallonsa da idanuwanta da ya fi tsana a yanzu domin haushi take ba shi, ta boye takardar hannunta a bayanta ta matse gadonta ta natsu sosai irin natsuwar nan ta tsoro. Yau wardrobe din Ummi ya nufa ya bude ya fara dubawa a hankali domin ita kadai ce be bincika na a kwana uku da ya kwashe yana bincikar ďakin a duk lokacin da ya samu sa'a Ummi bata ciki, yadda yake bin komai a sannu yana maida shi mazauninsa a yadda ya taba shi sai ka rantse da Allah criminal ne da ya kware a sata. Ita dai Waira kallonsa kawai take kamin ta mike tsaye ta nufi inda zomonta ya leko ta dauke abunta ta rike. A hankali ya rufe wardrobe din sannan ya juyo ya kalleta tana shafa zomon tana kallonsa. Ya bude dayan side din ya fara dubawa daga samna gaba daya akwati ne da Ummi ta saka a gurin. Hankali kwance ya bude akwatin yana saka yadda zai fadawa Ummi cewar Waira ce ta ce ya duba mata tufafinta a gurin, tufafi ne sabin da ba a dinka ba a ciki lace da atamfa kasan kayan kuma wata karamar jaka ce irin ta saka takaradu, sai da ya cire kayan sannan ya dauko jakar dake lake da karamin makulli, aje jakar yayi ya maida akwatin da ya rufe sannan ya rufe wardrobe din yana ta mamakin me ke ciki fatansa dai ace abun da yake nema ne, domin ya duba gun da Ummi ke aje takardunta be samu komai a gurin ba. Sai da ya gama ya dauki jakar ya nufi kofa sai kuma ya juyo ya kalli Waira.
“Sauran na ji kin ce na dauki wani abu, na cire miki ido”
Yana maganar yana zare mata ido, ita dai idon kawai ta sakar masa har ya fice, sai da ta ba shi mintunan da take kyautata zaton ya isa ya boya sannan ta nufi kofar ta bude ta fito tana sanda ta sauko kasa, sau daya ta kalli gurin da Mahmood yake zaune ta dauke kai bata ce masa komai ba, shi ma kuma be ce mata ba har ta fice. Harabar gidan ta fara kallo tana rabon ido bata san inda ya shiga ba balle ta bi shi, sai dai ta ga motar da ya shigo dan haka ta nufi gurin motar ta tsaya tana leka ciki ganin babu kowa ya saka ta zauna a gurin ta jingina da motar, a wayonta duk inda suka a cikin gidan dole idan suka fito za su tafi zata gansu ai idan tana gurin.
NAMRA POV.
Namra ta yi musu tarba irin wacce ta dace da mosoyi ita da Yesmin da Hanne suka jera musu abubuwan da aka shirya musu. Zaman minti talatin da ta yi a falon sai da ya fara bata labarin haduwarsa da Waira, a iyakar gaskiyarsa ya jidadin ganinta kuma ya kasa boye hakan, ita dai bata ce masa uffan ba akan Waira ba har ta fita ta ba su guri domin cin abinci.
“Dr zaka kufular da yarinyar nan fa, taya zaka rumgume wata budurwa a gabanta kuma ka zo kana ta bata labarin haduwarku?”
Dr Shuraim ya aje kofin lemun dake hannunsa.
“Haba karka min kuskuren fahimta mana, Namra ba yarinya ba ce ai tasan kanta ba zata ce kishi take akan haka ba, kuma ni ba son wannan yarinyar nake ba, kawai dai ta shiga raina ne sosai dan zaman da muka yi na kwana biyu daga asibiti zuwa gidanmu Allah ya sanya shakuwa a tsakaninmu, baka lura ita ta yi tsalle ta rumgume ni ba?”
“Eh amman mace bata son ko kwalliyar wata macen ka yaba a gaban wata fa, kai baka lura yanayinta ya canja ba, kuma ka zo kana ta son dole sai ka fada mata yadda kuka shaku”
Shuraim yayi murmushi.
“Kamal kana nufin kishi take? Ai dalili ake ma kishi da ace ganin ta yi nace jna sonta shi ne zata yi kishi”
“Ka dai kiyaye kar garin neman gira a rasa ido, kuma karka manta abun da ya kawo ka a gidan nan”
“Ba zan manta ba, ni da na dade ina jiran zuwan wannan ranar, kuma zan manta a yau? Kaima tunaninka ne ya baka wani abu amman babu abun da kake tunani a zuciyata”
Be sake cewa komai ba, ya bude fruit salad. Shuraim be ci komai ba bayan lemun da Namra ta zuba masa ya sha, Kamal ne kawai ya ci abinci shi ma kuma ba sosai ba.
[6/17, 10:57 PM] My S Line: *Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
37
AMEER POV.
Tun da ya shigo gurin Humaira ta lura da yanayinsa, yau ya dan fi sakewa fiye da jiya da shekaranjiya. Gorar ruwa ta dauka ta nufi inda yake, sai da ta fara aje masa ruwan sannan ta ciro biro da dan karamin littafi.
“Me za a kawo?”
Ya daga kai ya kalleta be jin zai iya amsa mata dan haka ya sauke kansa ya saka hannu aljihu ya ciro wayarsa ya fara latsawa.
“Me zaa a kawo maka?”
Ya mata banza, ta daure ta sake tambaya a karo na uku.
“Me za a kawo? Idan na bar gurin nan baka fada min ba, ko na kira ni ba zan dawo ba, me yasa kai a rayuwarka kake son ƙuntatawa mutane ne? Kai baka san dan adam yana da daraja ba?”
Ya dago ya kalleta a hankade.
“Nuna min inda taki darajar take, kina mace kin so kina aikin siyar da abinci a karkashin mahaifina, kina daukar order ko wane shege da dan'iskan, sannan ki tsaya a gabana kina min zancen daraja, be kamata kalmar ta fito daga bakinki ba ai, domin ke baki da ita, kudi su ne daraja, daraja shi ne ka cire talkami wani ya zo da gudu ya dauka ya wanke maka, ka zo restaurant wata ta zo ta tsaya a gabanka da abun rubutu tana jiran ka fada mata abun ka kake son ci ta kawo maka, daraja ka shiga mota idan ka tsaya mutane ta nufoka suna son ka ba su kudi, daraja ka zama mai ikonka kanka ba a karkashin ikon wani ba”
Ta kalleshi da kyau zuciyarta cike da bakincikin kalaman da ya fada mata.
“Dan'adam ba shi da zabin rayuwa kamin a haife shi, zabin iyaye ko yan'uwa ko gari ko addini, yadda Allah ya so haka yake halittar bayinsa, amman dan'adan yana da zabin yadda zai gode Allah bayan ya samu kansa a cikin wadannan abubuwan da na lissafa, saboda Allah ya baka kudi ko iyaye masu kudi, ba shi yake nufin ni baya so na, kuma be yi alkawarin zan tabbata a haka ba, Ameer kana butulce Allah da ni'imar da yayi maka, kana yawan fariya da abun da Allah baya so, girman kai ma alama ce ta yan wuta. Aikin da nake a nan ya fiye min na je na yi zina ko na lalata rayuwar wani hakkin zai min yawa. Amman a nan ko ba komai zan iya rike mutuncina kuma na kula da tarbiyar da iyayena suka min”
Tana akai aya ta juya zata tafi.
“Wonderful, ina yaba yadda idonki ya tsaya kam kike iya fada min magana any how”
Ta juyo ta kalleshi tana murmushi.
“Kasan dalilin wannan kwarin guiwar? Saboda wannan kamfanin na mahaifinka ne ba naka ba, mahaifinki nake yi ma aiki ba kai ba, yanzu da za a tambaye ka waye kai ka ce ne mai gurin nan zai fi burgewa fiye da ka ce a tambaye ka kace kai ne ďan mai gurin nan, kimarka zata ragu, kuma ka ga arzikin ba naka ba ne na mahaifinka ne, ina tausayin rayuwarka Ameer dadi da wahala basa tabbata har abada ka ji tsoron ranar da wannan jindadi zai gushe”
“Matsakar talaka kenan hassada ke yanzu har fata kike jindadin da nake ciki ya gushe?”
Ta saka hannu ta share hawayen da suka zubo mata.
“Arzikin da kake cin amanar yayan mutane kana lalata rayuwar yar mutane ka haifar da iyayensu bakinciki da damuwa, Allah sai ya isar musu”
“Baki ma san yadda abun yake ba sai na dandana miki”
“Na fi karfinka Ameer ko hannu baka isa ka rike ba balle har ka aikata abun da kake so da ni, ni ba irin dolayen karuwanka ba ne domin ni ba mazinaciya ba ce irinka..!”
Ta fada cikin ihu da kururuwa har hankalin mutanen da nesa da su sai da suka dago suna kallonsu.
“Kina wasa da wuta yarinya, ni zaki yi ma duniyanci? You will regret this”
Ta jefa masa littafin dake hannunta.
“Aiki ne? Na daina ko da kuwa rai ne a gurin nan sai dai na rasa shi”
“Sauran na ji kin ce na dauki wani abu, na cire miki ido”
Yana maganar yana zare mata ido, ita dai idon kawai ta sakar masa har ya fice, sai da ta ba shi mintunan da take kyautata zaton ya isa ya boya sannan ta nufi kofar ta bude ta fito tana sanda ta sauko kasa, sau daya ta kalli gurin da Mahmood yake zaune ta dauke kai bata ce masa komai ba, shi ma kuma be ce mata ba har ta fice. Harabar gidan ta fara kallo tana rabon ido bata san inda ya shiga ba balle ta bi shi, sai dai ta ga motar da ya shigo dan haka ta nufi gurin motar ta tsaya tana leka ciki ganin babu kowa ya saka ta zauna a gurin ta jingina da motar, a wayonta duk inda suka a cikin gidan dole idan suka fito za su tafi zata gansu ai idan tana gurin.
NAMRA POV.
Namra ta yi musu tarba irin wacce ta dace da mosoyi ita da Yesmin da Hanne suka jera musu abubuwan da aka shirya musu. Zaman minti talatin da ta yi a falon sai da ya fara bata labarin haduwarsa da Waira, a iyakar gaskiyarsa ya jidadin ganinta kuma ya kasa boye hakan, ita dai bata ce masa uffan ba akan Waira ba har ta fita ta ba su guri domin cin abinci.
“Dr zaka kufular da yarinyar nan fa, taya zaka rumgume wata budurwa a gabanta kuma ka zo kana ta bata labarin haduwarku?”
Dr Shuraim ya aje kofin lemun dake hannunsa.
“Haba karka min kuskuren fahimta mana, Namra ba yarinya ba ce ai tasan kanta ba zata ce kishi take akan haka ba, kuma ni ba son wannan yarinyar nake ba, kawai dai ta shiga raina ne sosai dan zaman da muka yi na kwana biyu daga asibiti zuwa gidanmu Allah ya sanya shakuwa a tsakaninmu, baka lura ita ta yi tsalle ta rumgume ni ba?”
“Eh amman mace bata son ko kwalliyar wata macen ka yaba a gaban wata fa, kai baka lura yanayinta ya canja ba, kuma ka zo kana ta son dole sai ka fada mata yadda kuka shaku”
Shuraim yayi murmushi.
“Kamal kana nufin kishi take? Ai dalili ake ma kishi da ace ganin ta yi nace jna sonta shi ne zata yi kishi”
“Ka dai kiyaye kar garin neman gira a rasa ido, kuma karka manta abun da ya kawo ka a gidan nan”
“Ba zan manta ba, ni da na dade ina jiran zuwan wannan ranar, kuma zan manta a yau? Kaima tunaninka ne ya baka wani abu amman babu abun da kake tunani a zuciyata”
Be sake cewa komai ba, ya bude fruit salad. Shuraim be ci komai ba bayan lemun da Namra ta zuba masa ya sha, Kamal ne kawai ya ci abinci shi ma kuma ba sosai ba.
[6/17, 10:57 PM] My S Line: *Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
37
AMEER POV.
Tun da ya shigo gurin Humaira ta lura da yanayinsa, yau ya dan fi sakewa fiye da jiya da shekaranjiya. Gorar ruwa ta dauka ta nufi inda yake, sai da ta fara aje masa ruwan sannan ta ciro biro da dan karamin littafi.
“Me za a kawo?”
Ya daga kai ya kalleta be jin zai iya amsa mata dan haka ya sauke kansa ya saka hannu aljihu ya ciro wayarsa ya fara latsawa.
“Me zaa a kawo maka?”
Ya mata banza, ta daure ta sake tambaya a karo na uku.
“Me za a kawo? Idan na bar gurin nan baka fada min ba, ko na kira ni ba zan dawo ba, me yasa kai a rayuwarka kake son ƙuntatawa mutane ne? Kai baka san dan adam yana da daraja ba?”
Ya dago ya kalleta a hankade.
“Nuna min inda taki darajar take, kina mace kin so kina aikin siyar da abinci a karkashin mahaifina, kina daukar order ko wane shege da dan'iskan, sannan ki tsaya a gabana kina min zancen daraja, be kamata kalmar ta fito daga bakinki ba ai, domin ke baki da ita, kudi su ne daraja, daraja shi ne ka cire talkami wani ya zo da gudu ya dauka ya wanke maka, ka zo restaurant wata ta zo ta tsaya a gabanka da abun rubutu tana jiran ka fada mata abun ka kake son ci ta kawo maka, daraja ka shiga mota idan ka tsaya mutane ta nufoka suna son ka ba su kudi, daraja ka zama mai ikonka kanka ba a karkashin ikon wani ba”
Ta kalleshi da kyau zuciyarta cike da bakincikin kalaman da ya fada mata.
“Dan'adam ba shi da zabin rayuwa kamin a haife shi, zabin iyaye ko yan'uwa ko gari ko addini, yadda Allah ya so haka yake halittar bayinsa, amman dan'adan yana da zabin yadda zai gode Allah bayan ya samu kansa a cikin wadannan abubuwan da na lissafa, saboda Allah ya baka kudi ko iyaye masu kudi, ba shi yake nufin ni baya so na, kuma be yi alkawarin zan tabbata a haka ba, Ameer kana butulce Allah da ni'imar da yayi maka, kana yawan fariya da abun da Allah baya so, girman kai ma alama ce ta yan wuta. Aikin da nake a nan ya fiye min na je na yi zina ko na lalata rayuwar wani hakkin zai min yawa. Amman a nan ko ba komai zan iya rike mutuncina kuma na kula da tarbiyar da iyayena suka min”
Tana akai aya ta juya zata tafi.
“Wonderful, ina yaba yadda idonki ya tsaya kam kike iya fada min magana any how”
Ta juyo ta kalleshi tana murmushi.
“Kasan dalilin wannan kwarin guiwar? Saboda wannan kamfanin na mahaifinka ne ba naka ba, mahaifinki nake yi ma aiki ba kai ba, yanzu da za a tambaye ka waye kai ka ce ne mai gurin nan zai fi burgewa fiye da ka ce a tambaye ka kace kai ne ďan mai gurin nan, kimarka zata ragu, kuma ka ga arzikin ba naka ba ne na mahaifinka ne, ina tausayin rayuwarka Ameer dadi da wahala basa tabbata har abada ka ji tsoron ranar da wannan jindadi zai gushe”
“Matsakar talaka kenan hassada ke yanzu har fata kike jindadin da nake ciki ya gushe?”
Ta saka hannu ta share hawayen da suka zubo mata.
“Arzikin da kake cin amanar yayan mutane kana lalata rayuwar yar mutane ka haifar da iyayensu bakinciki da damuwa, Allah sai ya isar musu”
“Baki ma san yadda abun yake ba sai na dandana miki”
“Na fi karfinka Ameer ko hannu baka isa ka rike ba balle har ka aikata abun da kake so da ni, ni ba irin dolayen karuwanka ba ne domin ni ba mazinaciya ba ce irinka..!”
Ta fada cikin ihu da kururuwa har hankalin mutanen da nesa da su sai da suka dago suna kallonsu.
“Kina wasa da wuta yarinya, ni zaki yi ma duniyanci? You will regret this”
Ta jefa masa littafin dake hannunta.
“Aiki ne? Na daina ko da kuwa rai ne a gurin nan sai dai na rasa shi”