Sashe 149
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ranka ya dade ka taba jin labarin mutanen nan kuwa? Wallahi ba su ragawa kowa kuma dokokinsu ne a haka ya kamata mu tsaya bakin iyakarmu kar mu wuce gona da iri, wannan abun da kake kokarin yi zaka jefa kanka a matsala ne, ba film muke ba, ko a film indiawa suke wannan wautar ba hausawa ba”
“Office karka bata min rai, dan Allah ka dauki mutanenka ku tafi, ba wani abu nake kokarin nunawa na jarumta ba, na fada cewar ba zan tafi ba sai na yi magana da sarkinsu kuma sai na tabbatar Nuwaira zata rayu cikin aminci that's it”
Cikin kakkausan lafazi Maleek yake fadar hakan still yana rike da hannun Nuwaira. Ganin da gaske Maleek yake ya saka office nufar yan'uwansa ya ja su gefe domin tattaunawa. Nuwaira ta kalli Maleek dake rike da hannunta gam da dukanin karfinsa ta ce.
“Ya Maleek zan zauna lafiya na maka alkawari babu abun da zai same ni, please ka bi abun da suka fada maka ka tafi gida, idan Ummi ko Abiey suka ji abun da kake kokarin yi ba za su jidadi ba”
“Babu ruwanki a nan karki sake magana”
Ya fisgi hannunta har tana lilo ya nufi gurin motarsa ya bude ya sakata ciki ya rufe motar. Ya saka hannunsa aljihu ya ciro wayarsa ya yi dialing number Abiey a take kiran ya yanke yana muna masa no network, su ma police din kokarin kira suke network dinsu ya yanke, hakan kuma ba karamin daga musu hankali yayi ba gashi wanda yayi jagorancin zuwa gurin ya nuna musu hanya ya kara fada musu yadda garin da jama'ar garin suke. Gashi kuma bakin shiga garin ma kadai babu network ina ga ciki kuma? A haka kuma Maleek yake son su yi risking rayuwarsu saboda rai daya, ran da za su iya kashe su ita ba su kasheta ba, waya sani ma ko plan ne. Dukansu zuciyarsu bata natsu da biyewa Maleek su shiga cikin garin ba, saboda haka suka yanke shawarar juyawa su koma tare da Maleek din da Nuwaira har sai an sake shawara, domin ba za su bar Maleek ya shiga garin ba, ba kuma zai yiyu su tafi su bar shi ba, kamar yadda ba za su yarda su shiga cikin garin ba.
“Ranka ya dade, ina tunanin abun da ya fi, mu tattara gaba dayanmu mu koma gida, albashi idan aka yanke shawarar yadda ya kamata ayi sai a aiwatar daga baya, idan ma su za su zo su dauke ko kuma mu sake kawota ka ga dai sai mu san irin shirin da zamu yi”
Maleek ya dan yi jimmm alamar tunani sannan ya juya ya kalli Nuwaira dake cikin motar tana kallonsa.
“Hakan yayi bari na yi magana da ita”
Ya zagaya ya bude motar ya shiga sai ya bar kofar a bude.
“Mun yanke shawarar zamu koma tare da ke, daga baya sai mu yi tunanin abun da ya dace mu yi”
“Ba zan iya komawa ba Ya Maleek kuma idan ka ce zaka tafi da ni Eid ba zai bari ba, zai iya cutar da kai dan Allah ka tafi”
“Ki daina jin tsoro babu abun da zai iya min, ina da addu'a akwai tsari a tare da ni ke ma ba zai iya cutar da ke ba balle kuma ni, ki cire komai a ranki”
“Ba zan iya komawa ba, ina jin wani abu a cikin jikina ba zan iya komawa ba”
“Zai daina da zarar mun bar nan na miki alkawari kin ji?”
Ta yi shiru sai wani abu take kamar wadda bata cikin hayyacinta.
“Nuwaira kalleni”
Ta tsayar kanta a saitin fuskarsa kwayar idonta ta sauka cikin ta shi, wani irin natsuwa da kwarjinin kasa yi masa musu suka cika idonta ta samu kanta da yarda da kalamansa ta kasa sake musu masa.
“Mu tafi?”
Ta daga masa kai.
“Good”
Ya juya ya fita yayi magana da jami'an tsaron ya fada musu ta aminta. Sai duk suka shiga motocinsu ba tare da sun ce komai ba Maleek ya shiga motar da suka zo ya saka key a gurin tashi motar tace ku tuka ni ku gani, ko wace mota ta tashi ban da ta Maleek su kansu sai da mamaki ya kamasu, kuma suka kara tsorata da musamman da suka hango Eid yana kara doso inda suke, biyu daga cikin police din suka fita suna nuna Eid da pistol dinsu.
“Karka matso nan”
“Ba ku san taba ba, bani da matsala da ku Waira zan dauka”
Be fasa nufar inda Maleek yake ba, su kuma suka kasa harbinsa domin ba su da hujjar haka, Maleek kuma sai buga mota yake taki tashi Nuwaira na ganin hakan ta bude motar ta fito, ganin hakan ya saka Maleek bude motar shi ma ya fito gabansa faduwa yake amman ya dake saboda ba ya son Nuwaira ta cuto.
“Kin dawo gida, idan zai saka ki a mota dubu ba zata tashi ba, Sarki ne yake kira dole ne kuma amsa kiran, kai na idan ka shiryawa mutuwa ka taho mu tafi”
“Idan har zan tafi ba tare da ita ba, ba zan taba samun kaina cikin aminci ba, zan yi tunanin wane hali take ciki, kariyar da muka mata alkawari ba mu cika ba, saboda haka ba zan iya tafiya ya bar yarinyar nan ba”
Eid ya juya baya ya nuna ma Maleek kofar. Office yayi saurin karasowa kusa da inda suke
“Maleek karka yarda ka shiga baka san manufar ba”
“Ku dai ku tafi babu mai cutar da wani sai Allah zan fito lafiya na muku alkawari”
“Maleek...”
Dayan office ya dakatar mai kokarin hana Maleek.
“Ranka ya dade ra'ayinsa ya bi, mun dai mun yi iya namu idan ya ji zai iya shiga ciki sai masa addu'ar fitowa lafiya”
Duk yadda suka so su yi convince din Maleek kar ya bi Nuwaira be sauraresu ba, not just because of Nuwairar kanta, har dan yana son na nunawa Eid ba zai iya masa komai ba sai abun da Allah ya hukunta masa. Su dai kam ba za su iya kasada ba dan haka suka shiga motar su suka masa sallama suka tafi aka bar shi a gurin daga shi sai Nuwaira da Eid da kuma mutanen da ke bakin kofar garin suna jiran isowar Nuwaira.
“Yanzu zamu iya shiga da motar?”
Eid ya watsa ma Maleek wani mugun kallo ya kai hannunsa ya rika hannun Nuwaira sai ta fisge hannunta.
“Karka sake taba ni, ni a yanzu musulma ce haramun wanda ba dan'uwana ko uba ko mijina ya rike ni, na canja addini a yanzu ba addinina daya da kai ba, kamar yadda ba zuciyarmu ta banbanta”
Daga Maleek har Eid din kallonta suke babu wanda ya ce mat uffan. Eid ya juya ya fara tafiya sai kuma ya juyo ya kalli Maleek daga sama zuwa kasa ya dauke kai ya cigaba da tafiyarsa. Sai da ya ba su tazara mai yawa sannan Maleek da Nuwaira suka bi bayansa, kamin su iso an bude kofar garin mutanen dake jiranta suka matsa suka bata kofa ta wuce tare da Maleek, ban da mamaki da kallon ikon Allah babu abun da Maleek yake, shi ko a mafarki be taba ganin mutane masu kalar tufafin da ke sanye a jikin jama'ar garin ba, daga maza har mata babu wanda yake sanye da rigar da ta sauko masa har masa, kuma babu wanda ya saka tufafin da suka suturta jikinsu kamar yadda shi yayi ko kuma Nuwaira. Tun daga kan gine ginen garin zuwa abubuwan amfaninsu gaba daya Maleek be taba ganinsu ba, domin bw rayu a kauye ba balle ya san wasu abubuwa, haka ma ba dan da ba ne balle ya ce ya taba ganin yadda rayuwar baya take. Sai dai wani abun da ya bashi mamaki ganinsu tsab tsab ba kamar yadda ya fara atba da Nuwaira ba da kazanta, yayi zaton zai tararda kusan rabin garin da kazanta amman be ga haka ba. Duk gurin da suka ratsa kallonsu ake wasu na mamakin dawowar Nuwaira tare da wani, bayan an yi shelar ta gudu, wasu kuma na mamakin yadda ta sauya tufafin jikinta take tare da wanda ya aaka tufafin da suka banbanta da na su, ga kuma fatar jikinta dake sheki farinta ta fita fess kamar wadda aka sauyawa mata.
A madadin ta bi hanyar gidan Sarki sai ta zabi dauke hanyar da dakinta yake, bangaren da take rayuwa a gurin da ta girma, kuma gurin da ta gudu ta bari, tna tafiya tana tunanin yadda rayuwa zata kasance mata ita da Maleek domin abu ne mai wahala ace Sarki ya yafe mata ita kanta da take yar garin balle kuma Maleek da ya karya dokar garin bayab yayi hayayya d Eid, idan ma sarkin ya yafe mata to zai tabbatar da mata da kudirinsa na bata sarauta ne, abun da take ta fargaba tun farkon tashinta, saboda ta san idan ta haihu mutuwa zata yi kamar yadda aka kashe iyayenta bayan haihuwarta, kuma addinin da ta sauya a yanzu ba zata iya aje shi ba, tufafin ba zata daina sakawa ba, haka ma abincin garin Garuk bata jin zata iya cinsa a yanzu, rayuwa a dakin kasa da babu wuta babu ac babu kujera babu babban gado, babu mai damuwa da tashinta ko bachinta anya zata iya a yanzu?
“Ina ne?”
Tambayar Maleek ce ta dawo da ita daga dogon tunanin da ya kwashe ta har ta iso gurin ba tare da ta sani ba. Gaba dakin ya kara lalacewa wani bangare na dakin ya rufga ciki, datti ciki ya karu daga ciki har wajen dakin kamar gurin zuba shara haka yake, sharar ma ta kazamai masu bari bola ba tare da sun tsabta ce ba.
“A nan na yi rayuwa, a cikin dakin nan na girma a nan makwancina yake, ci da sha na duk a nan suke abincina yayan itatuwa ne, zakaru da beraye ne abokaina”
Kusan mutuwar tsaye yayi yana kallonta, how come zata ce masa ta yi rayuwa a nan?
“Nuwaira ko dabobi ba za su iya rayuwa a nan ba balle mutum, ina danginki suke?”
“Office karka bata min rai, dan Allah ka dauki mutanenka ku tafi, ba wani abu nake kokarin nunawa na jarumta ba, na fada cewar ba zan tafi ba sai na yi magana da sarkinsu kuma sai na tabbatar Nuwaira zata rayu cikin aminci that's it”
Cikin kakkausan lafazi Maleek yake fadar hakan still yana rike da hannun Nuwaira. Ganin da gaske Maleek yake ya saka office nufar yan'uwansa ya ja su gefe domin tattaunawa. Nuwaira ta kalli Maleek dake rike da hannunta gam da dukanin karfinsa ta ce.
“Ya Maleek zan zauna lafiya na maka alkawari babu abun da zai same ni, please ka bi abun da suka fada maka ka tafi gida, idan Ummi ko Abiey suka ji abun da kake kokarin yi ba za su jidadi ba”
“Babu ruwanki a nan karki sake magana”
Ya fisgi hannunta har tana lilo ya nufi gurin motarsa ya bude ya sakata ciki ya rufe motar. Ya saka hannunsa aljihu ya ciro wayarsa ya yi dialing number Abiey a take kiran ya yanke yana muna masa no network, su ma police din kokarin kira suke network dinsu ya yanke, hakan kuma ba karamin daga musu hankali yayi ba gashi wanda yayi jagorancin zuwa gurin ya nuna musu hanya ya kara fada musu yadda garin da jama'ar garin suke. Gashi kuma bakin shiga garin ma kadai babu network ina ga ciki kuma? A haka kuma Maleek yake son su yi risking rayuwarsu saboda rai daya, ran da za su iya kashe su ita ba su kasheta ba, waya sani ma ko plan ne. Dukansu zuciyarsu bata natsu da biyewa Maleek su shiga cikin garin ba, saboda haka suka yanke shawarar juyawa su koma tare da Maleek din da Nuwaira har sai an sake shawara, domin ba za su bar Maleek ya shiga garin ba, ba kuma zai yiyu su tafi su bar shi ba, kamar yadda ba za su yarda su shiga cikin garin ba.
“Ranka ya dade, ina tunanin abun da ya fi, mu tattara gaba dayanmu mu koma gida, albashi idan aka yanke shawarar yadda ya kamata ayi sai a aiwatar daga baya, idan ma su za su zo su dauke ko kuma mu sake kawota ka ga dai sai mu san irin shirin da zamu yi”
Maleek ya dan yi jimmm alamar tunani sannan ya juya ya kalli Nuwaira dake cikin motar tana kallonsa.
“Hakan yayi bari na yi magana da ita”
Ya zagaya ya bude motar ya shiga sai ya bar kofar a bude.
“Mun yanke shawarar zamu koma tare da ke, daga baya sai mu yi tunanin abun da ya dace mu yi”
“Ba zan iya komawa ba Ya Maleek kuma idan ka ce zaka tafi da ni Eid ba zai bari ba, zai iya cutar da kai dan Allah ka tafi”
“Ki daina jin tsoro babu abun da zai iya min, ina da addu'a akwai tsari a tare da ni ke ma ba zai iya cutar da ke ba balle kuma ni, ki cire komai a ranki”
“Ba zan iya komawa ba, ina jin wani abu a cikin jikina ba zan iya komawa ba”
“Zai daina da zarar mun bar nan na miki alkawari kin ji?”
Ta yi shiru sai wani abu take kamar wadda bata cikin hayyacinta.
“Nuwaira kalleni”
Ta tsayar kanta a saitin fuskarsa kwayar idonta ta sauka cikin ta shi, wani irin natsuwa da kwarjinin kasa yi masa musu suka cika idonta ta samu kanta da yarda da kalamansa ta kasa sake musu masa.
“Mu tafi?”
Ta daga masa kai.
“Good”
Ya juya ya fita yayi magana da jami'an tsaron ya fada musu ta aminta. Sai duk suka shiga motocinsu ba tare da sun ce komai ba Maleek ya shiga motar da suka zo ya saka key a gurin tashi motar tace ku tuka ni ku gani, ko wace mota ta tashi ban da ta Maleek su kansu sai da mamaki ya kamasu, kuma suka kara tsorata da musamman da suka hango Eid yana kara doso inda suke, biyu daga cikin police din suka fita suna nuna Eid da pistol dinsu.
“Karka matso nan”
“Ba ku san taba ba, bani da matsala da ku Waira zan dauka”
Be fasa nufar inda Maleek yake ba, su kuma suka kasa harbinsa domin ba su da hujjar haka, Maleek kuma sai buga mota yake taki tashi Nuwaira na ganin hakan ta bude motar ta fito, ganin hakan ya saka Maleek bude motar shi ma ya fito gabansa faduwa yake amman ya dake saboda ba ya son Nuwaira ta cuto.
“Kin dawo gida, idan zai saka ki a mota dubu ba zata tashi ba, Sarki ne yake kira dole ne kuma amsa kiran, kai na idan ka shiryawa mutuwa ka taho mu tafi”
“Idan har zan tafi ba tare da ita ba, ba zan taba samun kaina cikin aminci ba, zan yi tunanin wane hali take ciki, kariyar da muka mata alkawari ba mu cika ba, saboda haka ba zan iya tafiya ya bar yarinyar nan ba”
Eid ya juya baya ya nuna ma Maleek kofar. Office yayi saurin karasowa kusa da inda suke
“Maleek karka yarda ka shiga baka san manufar ba”
“Ku dai ku tafi babu mai cutar da wani sai Allah zan fito lafiya na muku alkawari”
“Maleek...”
Dayan office ya dakatar mai kokarin hana Maleek.
“Ranka ya dade ra'ayinsa ya bi, mun dai mun yi iya namu idan ya ji zai iya shiga ciki sai masa addu'ar fitowa lafiya”
Duk yadda suka so su yi convince din Maleek kar ya bi Nuwaira be sauraresu ba, not just because of Nuwairar kanta, har dan yana son na nunawa Eid ba zai iya masa komai ba sai abun da Allah ya hukunta masa. Su dai kam ba za su iya kasada ba dan haka suka shiga motar su suka masa sallama suka tafi aka bar shi a gurin daga shi sai Nuwaira da Eid da kuma mutanen da ke bakin kofar garin suna jiran isowar Nuwaira.
“Yanzu zamu iya shiga da motar?”
Eid ya watsa ma Maleek wani mugun kallo ya kai hannunsa ya rika hannun Nuwaira sai ta fisge hannunta.
“Karka sake taba ni, ni a yanzu musulma ce haramun wanda ba dan'uwana ko uba ko mijina ya rike ni, na canja addini a yanzu ba addinina daya da kai ba, kamar yadda ba zuciyarmu ta banbanta”
Daga Maleek har Eid din kallonta suke babu wanda ya ce mat uffan. Eid ya juya ya fara tafiya sai kuma ya juyo ya kalli Maleek daga sama zuwa kasa ya dauke kai ya cigaba da tafiyarsa. Sai da ya ba su tazara mai yawa sannan Maleek da Nuwaira suka bi bayansa, kamin su iso an bude kofar garin mutanen dake jiranta suka matsa suka bata kofa ta wuce tare da Maleek, ban da mamaki da kallon ikon Allah babu abun da Maleek yake, shi ko a mafarki be taba ganin mutane masu kalar tufafin da ke sanye a jikin jama'ar garin ba, daga maza har mata babu wanda yake sanye da rigar da ta sauko masa har masa, kuma babu wanda ya saka tufafin da suka suturta jikinsu kamar yadda shi yayi ko kuma Nuwaira. Tun daga kan gine ginen garin zuwa abubuwan amfaninsu gaba daya Maleek be taba ganinsu ba, domin bw rayu a kauye ba balle ya san wasu abubuwa, haka ma ba dan da ba ne balle ya ce ya taba ganin yadda rayuwar baya take. Sai dai wani abun da ya bashi mamaki ganinsu tsab tsab ba kamar yadda ya fara atba da Nuwaira ba da kazanta, yayi zaton zai tararda kusan rabin garin da kazanta amman be ga haka ba. Duk gurin da suka ratsa kallonsu ake wasu na mamakin dawowar Nuwaira tare da wani, bayan an yi shelar ta gudu, wasu kuma na mamakin yadda ta sauya tufafin jikinta take tare da wanda ya aaka tufafin da suka banbanta da na su, ga kuma fatar jikinta dake sheki farinta ta fita fess kamar wadda aka sauyawa mata.
A madadin ta bi hanyar gidan Sarki sai ta zabi dauke hanyar da dakinta yake, bangaren da take rayuwa a gurin da ta girma, kuma gurin da ta gudu ta bari, tna tafiya tana tunanin yadda rayuwa zata kasance mata ita da Maleek domin abu ne mai wahala ace Sarki ya yafe mata ita kanta da take yar garin balle kuma Maleek da ya karya dokar garin bayab yayi hayayya d Eid, idan ma sarkin ya yafe mata to zai tabbatar da mata da kudirinsa na bata sarauta ne, abun da take ta fargaba tun farkon tashinta, saboda ta san idan ta haihu mutuwa zata yi kamar yadda aka kashe iyayenta bayan haihuwarta, kuma addinin da ta sauya a yanzu ba zata iya aje shi ba, tufafin ba zata daina sakawa ba, haka ma abincin garin Garuk bata jin zata iya cinsa a yanzu, rayuwa a dakin kasa da babu wuta babu ac babu kujera babu babban gado, babu mai damuwa da tashinta ko bachinta anya zata iya a yanzu?
“Ina ne?”
Tambayar Maleek ce ta dawo da ita daga dogon tunanin da ya kwashe ta har ta iso gurin ba tare da ta sani ba. Gaba dakin ya kara lalacewa wani bangare na dakin ya rufga ciki, datti ciki ya karu daga ciki har wajen dakin kamar gurin zuba shara haka yake, sharar ma ta kazamai masu bari bola ba tare da sun tsabta ce ba.
“A nan na yi rayuwa, a cikin dakin nan na girma a nan makwancina yake, ci da sha na duk a nan suke abincina yayan itatuwa ne, zakaru da beraye ne abokaina”
Kusan mutuwar tsaye yayi yana kallonta, how come zata ce masa ta yi rayuwa a nan?
“Nuwaira ko dabobi ba za su iya rayuwa a nan ba balle mutum, ina danginki suke?”