Sashe 95
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummi ta kalli Motar sannan ta sake kallon Ameer cikin wani yanayi mai kamar na tsoro ko fargabar zuciyar Ameer ta ce.
“Akwai abubuwa da yawa da ya kamata ka sani, ka ba ni dama na bude maka komai Ameer”
Ya tari numfashinta.
“Bana bukatar sanin komai”
Ya juya sai kuma ya juyo.
“Sorry for the lost na ďana daga cikin yayan da kika fi kauna, Allah ya mata rahma”
Ya sake juyawa zai shiga cikin gidan, sai Waira ta bi bayansa.
“Ke”
Maleek ya kirata, ta juyo kamar a razane.
“Ina son zan tambaye shi wani abu ne”
Ta fada muryarta na rawa. Maleek ya bude mata ido.
“Shiga mota”
Ta kalli Ameer kamar zata fashe da kuka ta zagaya gurin motar da Maleek ya bude ta shiga.
“Sai anjima Ameer, na gode”
Ummi ta fada sannan ta shiga motar, sai gashi ya juyo yana kallonta har ta shoga motar Maleek yaja suka bar gurin. Kansa ya daga sama hawaye suka zubo masa ta gefen ido.
[7/7, 10:21 PM] My S Line: 49
“Ummi magana kawai zan yi da shi, wani abu zan tambaye shi”
Waira ta fada tana girgiza hannun Ummi, so take Ummi ta cilasta Maleek komawa gidansu Ameer ta yi masa tambayoyi abubuwan da take son sani da kuma wadanda suka shige mata duhu.
“Ummi ki ce ya koma”
Duk magiyar da take Ummi, Maleek be ce komai ba har sai da suka faka compound din gidan.
“Ummi please ki ce Ya Maleek”
Juyowa yayi ya watsa mata harara sannan ya bude motar ya fita, ya budewa Ummi ta fito tare da Waira. Abun ka da mai na ci sai ta sake rokon Ummi ba Maleek umarni komawa gidansu Ameer, ko kuma ya kaita ya barta a can har sai ta gama abun da take sannan ya daukota. A nan ya daka mata tsawa daman ransa a ɓacen yake.
“Ba zan koma ba, babu wanda zai koma gidan nan, ko sunansa na sake ji a bakinki sai na miki dukan tsiya, Ummi that's enough ba zaki sake zuwa ganin yaron nan ba, ko da ba ni zan kai ki ba zaki sake saka kafa da sunan ganin Ameer ba, ba zan jire yadda yake amsa miki magana son ransa ba i won't tolerate that”
Ummi ta yi murmushi cikin tattausan lafazi ta ce.
“Shi ma ďana ne, banbancin ka da shi kai Aliyu ne ya haifeka, Shi kuma Zaharadeen, kai sunanka Maleek shi kuma Ameer, amman a cikin uwa ďaya kuka fito, a mahaifa ďaya kuka zauna, a yanzu ya fika bukatata, domin ban samu rayuwa da shi a lokacin da yafi bukatata ba, kai ma lokacin da kake kyamata ma jure zama da kai, da duk wani abu da kake yi min har zuwa yau da komai ya yaye maka, miyasa shi ba zamu ba shi damar yin fushi har ya fahimci manufata ya sauka ba?”
“Ummi yaron nan ba shi da tarbiya idan ba haka ba, ai ko wace uwa a bar girmamawa ce a gurin ko wane ďan halak, amman daman can shi ne matar kirki a cikin abokanmu, kalli abun da yayi ma Nimra”
“Mutuwa ma tana kunyar idon mahaifiya, ya kamata ka tausasa kalamanka kuma maganar Nimra! Ni ya kamata ka dorawa laifin, ba wanda be san komai ba. Ya fahimci Ameer ďan uwanka ne na jini”
“That's the most painful part”
Ya fada ya rufe motar ta karfi ya nufi cikin gidan da wani irin fushi da Ummi bata saba ganin Maleek a cikinsa ba.
“Idan aka samu rashin hadin kai a tsakaninku, wani sabon ciwo ne a gareni, Allah ka hada min kan ƴaƴana”
Ta kama hannu Waira suka shiga ciki. A falo Ummi ta samu Dr Zaune zaune Namra na cinyarta kwance daga ita har Namra sharar kwalla suke. Namra na ganin Ummi ta tashi zaune
“Ummi ya jikin na ki?”
“Jiki Alhamdulillah”
“Me likita ya ce”
Ummi ta kalli yayar mijinta wato Dr Zainab sannan ta kalli Namra ta ce.
“Ya ce jiki da sauki babu wata matsala”
“Ummi Allah ya baki lafiya, dan Allah ki yarda da maganar Abiey ya ce zai fitar da ke waje a duba lafiyarki”
Ummi ta saki hannu Waira ta zauna tana kallonsu.
“Daga ina kuma wannan ya fito?”
“Ummi ba zaki iya boye mana komai ba a yanzu, Dr ta fada min Abiey be dade da tashi anan ba, ya fada mana komai”
Namra na fada tana nufar inda take, sai ta rumgumeta tana kuka. Ummi ta shafa bayanta.
“Da sauko fa karki daga hankalinki, babu abun da zai faru, komai ai sai Allah ya kaddara yake faruwa”
“Allah ya barki cikin zuri'arki Zahra”
Dr Zainab ta roka tana jin tausayin Ummi, sai dai karfin hali irin na uwa dake kokarin kwantar da hankalin kowa ya hana Ummi zubar da kwalla ko daya, sai murmushin da take.
Bayan sallah la'asar Waira ta sauko rike da jakarta ta nufi dinning sai da ta kauce duk abu da zai takura mata a kam dinning table din sannan ta dora jakarta ta cire littafanta tare da abun rubutu ta aje ta fara bude textbook dinta tana kallo.
“Yau kuma nan ake karatun Waira? Ba akwai dakin karatu ba? Kuma a dakin ki ma an saka miki kujerar zama da teburin karatu ko?”
Cewar Ummi tana dire flask din ruwan zafi a dinning din.
“Na tafi can?”
Ummi ta yi murmushi ta shafa kanta, sai idonta ya cika da hawaye tana tunawa da Nimra.
“Aa zauna a nan, amman dai kar wani yayi miki wani abu ki ce an miki ba daidai ba, nan gurin cin abinci ne ba gurin karatu ba”
Da kai Waira ta amsa mata ta cigaba abun da take har sai da ta ga Ummi ta bar falon ta koma kitchen saboda shigowar Hanne. Sannan ta tashi da kamar sanda ta nufi upstairs ta hau, bangaren da dakinta yake ta nufa kamar zata shiga sai kuma ta wuce dakinta ta tsaya bakin kofar dakin Maleek, har yanzu zuciyarta da kwadayin son zuwa gurin Ameer dan haka take jin kamar idan ta yi ma Maleek magiya zai yarda ya kaita. A hankali ta murda kofar dakin ta bude ta leka, sai ta hango shi zaune kan kujera yana fuskanta windows din dakinsa dake bude, bata san abun da yake ba domin kansa a kasa yake yana ta rare karatun Al'qur'ane, baya ta yi kadan ta yadda ba zai hango ta ta tsaya rike da kofar tana sauraren yadda muryarsa take da dadin gurin karatun, yadda yake jan aya ya direta ya dauki wata ya tafibda tunaninta, zakin muryarsa da kuma dadin abun da yake karantawarta ya saka ta tsayuwa jikin kofar har ta kai zaune ta tsanu tana jin ayayoyin da bata san akan me suke magana ba, wani yare ne mai dadin sauraro da saukar da natsuwa,ba wannan ne karon karfo da ta ji karatun a gidan ba, sai dai bata taba maida hankali ta saurara da natsuwa ba irin yau, kuma wani be tana karatu da murya mai zaki ba irin ta Maleek, wannan ne karon farko da taba jin Maleek yana karatun, a yanzu kam ta tabbatar wannan yaren ya fi nata da na su Ummi da kuma wanda aka koya mata wato turanci dadi nesa ba kusa ba. Shi yake karatun ita tsigar jikinta yake tashi ji take bata taba jin wani abu mai dadi saurarowa irin wannan!
Dan juyowa yayi kadan sai ya lura da kofar dakin dake bude kadan, ga kuma inuwar mutum a zaune, be tabbatar ba amman zuciyarsa ta raya masa cewar Waira, domin ita kadai zata yi masa haka, Namra ya san idan tana bukatar wani abu zata iya masa magana, balle ma dakinsa ba gurin shigowarta ba ne tun a lokacin baya hakan ya saka sai suka dauke kafarsu daga dakinsa gaba daya, Ummi ma dake shigowa ba zata masa labe ba. Yana kawai a karshe aya, ya rufe qur'ane ta aje ya tashi ya nufi kofar ya bude tana ganinsa sai ta mike tsaye da sauri ta daga kai tana kallonsa ta manta da hawaye a idonta har sai da ta ga yana kallon fuskarta.
“Cry???”
Ta saka hannu ta sauri ta share.
“Abun da kake yi ne?”
Ta fada a shagwabe, sai ya tsaya tunani domin be san wani abu da yake ba.
“Oh karatu?”
Ya tambaya tunawa da yayi. Sai ta daga kai masa.
“Shi me yasa baka koya min ba?”
“Shi ak karatu ne, wani bangare ne na ibadar mu, ke kuma ba Musulma ba ce”
“Ke ma ba kuna da ibadar ku ba?”
“Yes amman wannan karatun yana da dadi, na ji wani iri karatun akwai dadi”
He's not in the mood if not da sai yayi mata murmushi ko kwararran bayani, sai dai shi ma yana cikin bacin rai na abun da Ameer yayi da kuma bakinciki rashin kanwarsa Nimra, wannan ne silar karatun al'qur'anen da yake da yamman nan domin samun walwala.
“Why are you here?”
Bata san tana da wayon iya roko ba sai a lokacin, kamar wata almajira haka ta zube kasa ta hade hannayenta ta daga kai, daman sai da daga kai kam tana tsaye ma ta daga kai ta kalleshi balle ta zube kasa. Marairaice murya ta yi ta fara masa magiya.
“Please Ya Maleek i know you hate me, but please ka kai ni gurin Ameer, ina son magana da shi, please”
“Akwai abubuwa da yawa da ya kamata ka sani, ka ba ni dama na bude maka komai Ameer”
Ya tari numfashinta.
“Bana bukatar sanin komai”
Ya juya sai kuma ya juyo.
“Sorry for the lost na ďana daga cikin yayan da kika fi kauna, Allah ya mata rahma”
Ya sake juyawa zai shiga cikin gidan, sai Waira ta bi bayansa.
“Ke”
Maleek ya kirata, ta juyo kamar a razane.
“Ina son zan tambaye shi wani abu ne”
Ta fada muryarta na rawa. Maleek ya bude mata ido.
“Shiga mota”
Ta kalli Ameer kamar zata fashe da kuka ta zagaya gurin motar da Maleek ya bude ta shiga.
“Sai anjima Ameer, na gode”
Ummi ta fada sannan ta shiga motar, sai gashi ya juyo yana kallonta har ta shoga motar Maleek yaja suka bar gurin. Kansa ya daga sama hawaye suka zubo masa ta gefen ido.
[7/7, 10:21 PM] My S Line: 49
“Ummi magana kawai zan yi da shi, wani abu zan tambaye shi”
Waira ta fada tana girgiza hannun Ummi, so take Ummi ta cilasta Maleek komawa gidansu Ameer ta yi masa tambayoyi abubuwan da take son sani da kuma wadanda suka shige mata duhu.
“Ummi ki ce ya koma”
Duk magiyar da take Ummi, Maleek be ce komai ba har sai da suka faka compound din gidan.
“Ummi please ki ce Ya Maleek”
Juyowa yayi ya watsa mata harara sannan ya bude motar ya fita, ya budewa Ummi ta fito tare da Waira. Abun ka da mai na ci sai ta sake rokon Ummi ba Maleek umarni komawa gidansu Ameer, ko kuma ya kaita ya barta a can har sai ta gama abun da take sannan ya daukota. A nan ya daka mata tsawa daman ransa a ɓacen yake.
“Ba zan koma ba, babu wanda zai koma gidan nan, ko sunansa na sake ji a bakinki sai na miki dukan tsiya, Ummi that's enough ba zaki sake zuwa ganin yaron nan ba, ko da ba ni zan kai ki ba zaki sake saka kafa da sunan ganin Ameer ba, ba zan jire yadda yake amsa miki magana son ransa ba i won't tolerate that”
Ummi ta yi murmushi cikin tattausan lafazi ta ce.
“Shi ma ďana ne, banbancin ka da shi kai Aliyu ne ya haifeka, Shi kuma Zaharadeen, kai sunanka Maleek shi kuma Ameer, amman a cikin uwa ďaya kuka fito, a mahaifa ďaya kuka zauna, a yanzu ya fika bukatata, domin ban samu rayuwa da shi a lokacin da yafi bukatata ba, kai ma lokacin da kake kyamata ma jure zama da kai, da duk wani abu da kake yi min har zuwa yau da komai ya yaye maka, miyasa shi ba zamu ba shi damar yin fushi har ya fahimci manufata ya sauka ba?”
“Ummi yaron nan ba shi da tarbiya idan ba haka ba, ai ko wace uwa a bar girmamawa ce a gurin ko wane ďan halak, amman daman can shi ne matar kirki a cikin abokanmu, kalli abun da yayi ma Nimra”
“Mutuwa ma tana kunyar idon mahaifiya, ya kamata ka tausasa kalamanka kuma maganar Nimra! Ni ya kamata ka dorawa laifin, ba wanda be san komai ba. Ya fahimci Ameer ďan uwanka ne na jini”
“That's the most painful part”
Ya fada ya rufe motar ta karfi ya nufi cikin gidan da wani irin fushi da Ummi bata saba ganin Maleek a cikinsa ba.
“Idan aka samu rashin hadin kai a tsakaninku, wani sabon ciwo ne a gareni, Allah ka hada min kan ƴaƴana”
Ta kama hannu Waira suka shiga ciki. A falo Ummi ta samu Dr Zaune zaune Namra na cinyarta kwance daga ita har Namra sharar kwalla suke. Namra na ganin Ummi ta tashi zaune
“Ummi ya jikin na ki?”
“Jiki Alhamdulillah”
“Me likita ya ce”
Ummi ta kalli yayar mijinta wato Dr Zainab sannan ta kalli Namra ta ce.
“Ya ce jiki da sauki babu wata matsala”
“Ummi Allah ya baki lafiya, dan Allah ki yarda da maganar Abiey ya ce zai fitar da ke waje a duba lafiyarki”
Ummi ta saki hannu Waira ta zauna tana kallonsu.
“Daga ina kuma wannan ya fito?”
“Ummi ba zaki iya boye mana komai ba a yanzu, Dr ta fada min Abiey be dade da tashi anan ba, ya fada mana komai”
Namra na fada tana nufar inda take, sai ta rumgumeta tana kuka. Ummi ta shafa bayanta.
“Da sauko fa karki daga hankalinki, babu abun da zai faru, komai ai sai Allah ya kaddara yake faruwa”
“Allah ya barki cikin zuri'arki Zahra”
Dr Zainab ta roka tana jin tausayin Ummi, sai dai karfin hali irin na uwa dake kokarin kwantar da hankalin kowa ya hana Ummi zubar da kwalla ko daya, sai murmushin da take.
Bayan sallah la'asar Waira ta sauko rike da jakarta ta nufi dinning sai da ta kauce duk abu da zai takura mata a kam dinning table din sannan ta dora jakarta ta cire littafanta tare da abun rubutu ta aje ta fara bude textbook dinta tana kallo.
“Yau kuma nan ake karatun Waira? Ba akwai dakin karatu ba? Kuma a dakin ki ma an saka miki kujerar zama da teburin karatu ko?”
Cewar Ummi tana dire flask din ruwan zafi a dinning din.
“Na tafi can?”
Ummi ta yi murmushi ta shafa kanta, sai idonta ya cika da hawaye tana tunawa da Nimra.
“Aa zauna a nan, amman dai kar wani yayi miki wani abu ki ce an miki ba daidai ba, nan gurin cin abinci ne ba gurin karatu ba”
Da kai Waira ta amsa mata ta cigaba abun da take har sai da ta ga Ummi ta bar falon ta koma kitchen saboda shigowar Hanne. Sannan ta tashi da kamar sanda ta nufi upstairs ta hau, bangaren da dakinta yake ta nufa kamar zata shiga sai kuma ta wuce dakinta ta tsaya bakin kofar dakin Maleek, har yanzu zuciyarta da kwadayin son zuwa gurin Ameer dan haka take jin kamar idan ta yi ma Maleek magiya zai yarda ya kaita. A hankali ta murda kofar dakin ta bude ta leka, sai ta hango shi zaune kan kujera yana fuskanta windows din dakinsa dake bude, bata san abun da yake ba domin kansa a kasa yake yana ta rare karatun Al'qur'ane, baya ta yi kadan ta yadda ba zai hango ta ta tsaya rike da kofar tana sauraren yadda muryarsa take da dadin gurin karatun, yadda yake jan aya ya direta ya dauki wata ya tafibda tunaninta, zakin muryarsa da kuma dadin abun da yake karantawarta ya saka ta tsayuwa jikin kofar har ta kai zaune ta tsanu tana jin ayayoyin da bata san akan me suke magana ba, wani yare ne mai dadin sauraro da saukar da natsuwa,ba wannan ne karon karfo da ta ji karatun a gidan ba, sai dai bata taba maida hankali ta saurara da natsuwa ba irin yau, kuma wani be tana karatu da murya mai zaki ba irin ta Maleek, wannan ne karon farko da taba jin Maleek yana karatun, a yanzu kam ta tabbatar wannan yaren ya fi nata da na su Ummi da kuma wanda aka koya mata wato turanci dadi nesa ba kusa ba. Shi yake karatun ita tsigar jikinta yake tashi ji take bata taba jin wani abu mai dadi saurarowa irin wannan!
Dan juyowa yayi kadan sai ya lura da kofar dakin dake bude kadan, ga kuma inuwar mutum a zaune, be tabbatar ba amman zuciyarsa ta raya masa cewar Waira, domin ita kadai zata yi masa haka, Namra ya san idan tana bukatar wani abu zata iya masa magana, balle ma dakinsa ba gurin shigowarta ba ne tun a lokacin baya hakan ya saka sai suka dauke kafarsu daga dakinsa gaba daya, Ummi ma dake shigowa ba zata masa labe ba. Yana kawai a karshe aya, ya rufe qur'ane ta aje ya tashi ya nufi kofar ya bude tana ganinsa sai ta mike tsaye da sauri ta daga kai tana kallonsa ta manta da hawaye a idonta har sai da ta ga yana kallon fuskarta.
“Cry???”
Ta saka hannu ta sauri ta share.
“Abun da kake yi ne?”
Ta fada a shagwabe, sai ya tsaya tunani domin be san wani abu da yake ba.
“Oh karatu?”
Ya tambaya tunawa da yayi. Sai ta daga kai masa.
“Shi me yasa baka koya min ba?”
“Shi ak karatu ne, wani bangare ne na ibadar mu, ke kuma ba Musulma ba ce”
“Ke ma ba kuna da ibadar ku ba?”
“Yes amman wannan karatun yana da dadi, na ji wani iri karatun akwai dadi”
He's not in the mood if not da sai yayi mata murmushi ko kwararran bayani, sai dai shi ma yana cikin bacin rai na abun da Ameer yayi da kuma bakinciki rashin kanwarsa Nimra, wannan ne silar karatun al'qur'anen da yake da yamman nan domin samun walwala.
“Why are you here?”
Bata san tana da wayon iya roko ba sai a lokacin, kamar wata almajira haka ta zube kasa ta hade hannayenta ta daga kai, daman sai da daga kai kam tana tsaye ma ta daga kai ta kalleshi balle ta zube kasa. Marairaice murya ta yi ta fara masa magiya.
“Please Ya Maleek i know you hate me, but please ka kai ni gurin Ameer, ina son magana da shi, please”