Sashe 167
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Babu kawai dai na fahimci bata ra'ayi kin san shi so wani abu ne da yake gina kansa a zuciyar bawa, tana so zan iya fadar haka domin muna da kyakkyawar fahimta da ita, sai dai ba irin so na aureba kamar yadda ta fada, kuma na fahimce ta na mata uzuri”
Ummi ta ji wani iri a zuciyarta tausayinta danta ya kamata, sai dai kuma ya san bata isa ta saka Nuwaira son Ameer a dole ba kamar yadda bata isa ta cire wanda ke zuciyarta ba, ko ba a fada mata ba ta san ba zai wuce Maleek ba, domin Ummi ta ga irin kukan da ta sha lokacin da ta san da Maleek za a tafi, and duk gaisawar da zata yi da Ummi idan ta tambaye Ummi yaushe zata dawo sai ta ce Ya Maleek yaushe zaka dawo, shi kansa Maleek din tana lura da irin yadda yanayinsa yake canjawa idan yana video call da ita a gaban Ummi.
“Ameer dan Allah kar wannan ya saka ka a damuwa, komai nufi ne na Allah kuma so da yawa mukan so abu ya zama ba alheri ba ne a garemu, wani lokacin kuma sai mu ki abu ya zama alheri a garemu”
“Yeah shiyasa na daga mata kafa ai, a yanzu dai ina nan ina ta addu'a Allah ya yaye min duk wani abu da nake ji a zuciyata akan son Nuwaira”
“Ni ma zan taya ka da addu'a, amman kuma a cikin wannan halin kake zancen yin aure wa zaka aura?”
“Ban gama yanke hukunci ba, domin a yanzu bana jin sonta a raina kamar yadda nake jin Nuwaira, bana son na aureta na cutar da ita, wata kila kuma zan iya koya har na fara, ina jin zan iya zama da ita na bata kulawar da ya kamata amman ba zan ji sonta kamar Nuwaira ba, sai dai idan har ta tabbata abun da Hajiya ta fada min cewar ita din tana sona sosai kuma a haka take kokarin ganin na samu abun da nake so, ni kuma ba zan bari zuciyarta ta karaya ba”
“Humairah ce?”
“Ita ce Ummi, Hajiya ta nuna min tana son na aureta tun kamin Nuwaira ta amsa cewar bata so na, Daddy ma shi kuma saboda alakar dake tsakaninki da su ta yi karfi, i hope idan har abun da nake hasashe ya kasance zaki yarda da ita”
“Ameer ni ai ko yar tsana zaka kawo min matukar kana kaunarta ni ma ina sonta, amman karka cilastawa kanka sonta karka tirsasa kanka sonta ka bari son ya shiga zuciyarka da kansa”
Ya amsa mata da kai. Kwatantawa yayi da lokacin sallah sannan ya fita daga dakin, duk yadda Ummi ta so ya je gidan Dr Zainab ya zauna sai ya ki, shi dai ya fi ra'ayin ya zauna gidan mahaifinsa, ya fita daga asibitin texi ya dauka zuwa cath sai dai kamin ya isa gari ya fara haske kasancewar tafiya ce mai tazara daga inda gidan yake zuwa asibitin da Ummi take kwance.
Two Weeks Ameer yayi tare da Ummi within days din nan babu ranar da baya waya da Humairah, da safe kamin ta tafi school zata yi waya da shi da dare ma idan zai kwanta sai ya kira ta, duk wani attention da take bukata yana bata not because of yana son ya so ta sai dan yana da bukatar duk wani abu da zai dauke masa hankali daga Nuwaira for now kwanciyar hankali yake bukata kamin yayi tunanin abun da ya kamata yayi next. Two days da zuwan Abiey tare da Namra da Mahmood har ma da Maleek dukansu a gidan Dr Zainab suka sauka domin gida ne a gurinsu ko a lokacin da take aiki balle kuma yanzu da yayanta ne suke aiki nan bayan ita ta yi retired. After two days da zuwansu ya shirya ya koma gida Nigeria. Sanin yadda Humairah take daukin ganinsa da yadda ta kwallafa rai na cewar sai ta tafi airport ta tarbe shi ya saka tun kamin ya isa ya fadawa direban gidansu lokacin da zai je ya dauke ta ya kaita airport din bayan ya sanar da ita lokacin da za su sauka. Dan haka ta shirya da wuri ba shiri kawai ta yi ba har da shirya masa abincin da ta san zai iya ci ta gyara dakinsa kamar wata mai aure da mijinta zai dawo. Misalin karfe daya jirginsu ya sauka Lagos, daga Lagos ya shiga wani jirgin zuwa Abuja. Tun kamin ya karasa fitowa Airport din ya hangota a gurin da aka tanada domin aje motoci, tana tsaye jikin motar tana ta rabon ido, murmushi ne ya kawata fuskarsa sai a yanzu yake jin marmarinta har ganin yayi kamar ta kara kyau saboda yar ramar da ta yi. Tana hangoshi ta doso inda yake da saurinta shi ma ya kara hanzari ya iso inda take sai ta yi tsaye tana kallonsa da wani irin dauki da murmushi a kumatunta.
“I thought rumgume ni zaki yi duk matsuwar nan da kika yi na dawo”
“Ba kyau ni ba muharramankar ba ce kuma akwai mutane sosai a nan”
Ya juya ya kalli gurin.
“Kowa sha'aninsa yake indai har da gaske kike yi kin yi missing dina hug me”
“Akwai mutane Ameer”
“I don't care hug me Humairah show me that you miss me”
“Ameer... Ba kyau fa”
“This will be the last one till we get married....!”
Wani dummnn ta ji maganar a kunnenta sai ta ji kamar ba daga bakinsa ta fito ba, tsaye tayi kamar hoto tana kallonsa ko motsi bata yi. Murmushi yayi irin murmushin da ya kara masa kyau ya warware jacket dinsa dake hannunsa ya dora mata saman abayar da ke jikinta ya rumgume ta.
“I miss you so much Humairah i never thought mun sabu haka ba sai a yanzu da na ganki”
Hawaye ya sauko idonta sai ya saketa ya dube ta, ganin hawayen ya saka hannunsa biyu ya share mata hawayen.
“Mu tafi”
Ya fara tafiya ita kuma ta kasa juyowa ta kasa tafiyar ta kasa komai har lokacin, baya baya yayi ya riko hannunta ya juyo da ita.
“Wasa nake miki kar ke ma ki yi breaking heart dina kamar Nuwaira i can see that you don't love me...”
Yana rufe baki sai ya rumgume shi ba tare da ta sani ba ta fashe da kuka. Murmushi yayi ya daga hannayensa ya daga ta jikinsa ya sumbanci goshinta sannan ya rika hannunta suka nufi gurin motar. Kamin ya isa direban ya bude masa baya, sai da ya fara sakata sannan ya shiga driver yaja motar.
“Ina zamu je?”
“Gidan Hajiya”
Ta fada cikin wata murya mai ban tausayi, kallonta yayi yana murmushi sai ya ga shi take kallo hawaye na sauko mata, a hankali ya kai hannunsa ya rika yatsunta ya murza a hankali yana kara yarda da maganar Hajiyar.
“Me kika shirya min?”
Ta kasa cewa komai shi kuma be fasa tambayarta ba har suka isa gidan, ita ta fara fita motar sannan ya fito yana fadin.
“Ya kamata a samu mai gadi, ko dan ku samu mai kula muku da gidan”
Ya fadi hakan ne kasancewar da za su shiga sai da direban ya fita ya bude gate ya shigo da motar, ita dai har lokacin ta kasa cewa komai gaba daya jikinta a mace yake, bata jin sautin komai sai maganar da Ameer yayi mata a airport, domin ya furta mata ita a lokacin da bata yi zato ba, ba ta ma yi tsammanin ya fahimci yaren soyayyarta ba. Wata tambaya ce ta zo mata a rai a lokacin da yake ta hira da Hajiya yana cin abinci, da gaske yana jin wani abu a zuciyarsa gema da ita ko kuma dai saboda zai cika burin Ummi ne? Har ya ci ya sude beta tofa komai a maganarsa da Hajiya ba. Sai da zai tashi ya shiga dakinsa yayi mata alama da abincinta yayi dadi. Bata hakaro ba ta ji shi a kusa da ita yana mata magana.
“Are you okay?”
Wani irin faduwa gabanta yayi kwarjinsa ya cikata bata taba jin wani abu kunyarsa ba sai a lokacin, ta sauke ido kasa tana lekawa ta gani idan Hajiya bata gurin domin sosai ya matse har tana kusan jin numfashinsa.
“Hajiya bata nan”
Bata yarda da sai da ta duba da kanta bata ma san Hajiya ta bar falon ba sai lokacin.
“Zata iya fitowa ta ganmu a haka”
Ya kama hannunta ya rike yana murzawa a hankali.
“Humairah ina da banbanci da mutane yawanci abun da yake saka wasu kunya ko tsoron ni baya saka ni, nan ai gidanmu ne, dan anganmu a haka miye a ciki?”
Murmushi yayi mai sauti ya ce.
“Zaki iya tuna lokacin da kika fada min cewar idan na taba ki ko na rumgume ki sai ki min fadan hauka kin nuna min ke ba yar iska ba ce”
Ta fisge hannunta da sauri, sai kawai ya rumgume ta yana dariya sosai kamar ba shi ba.
“Go ahead idan na sake ki yanzu ki mare ni”
Ya fada sannan ya sake ta, abun mamaki duk masifarta sai ta daga ido ma ta kalleshi balle ta yi yunkurin aikata abun da ta furta.
“Ashe ni da ke duk marasa jin magana ne”
Ta kasa cewa komai har lokacin, da murmushi ya zagaye ya shige dakinsa kiran Daddy na shigowa wayarsa, sai da ya shige sannan ta juyo ya kalli bayansa tana murmushi ta kai hannunta ta dafe zuciyarta ta nufi dakinta da gudu tana shiga ta maida kofar ta rufe ta fada kan gadonta ta lumashe ido...
Ummi ta ji wani iri a zuciyarta tausayinta danta ya kamata, sai dai kuma ya san bata isa ta saka Nuwaira son Ameer a dole ba kamar yadda bata isa ta cire wanda ke zuciyarta ba, ko ba a fada mata ba ta san ba zai wuce Maleek ba, domin Ummi ta ga irin kukan da ta sha lokacin da ta san da Maleek za a tafi, and duk gaisawar da zata yi da Ummi idan ta tambaye Ummi yaushe zata dawo sai ta ce Ya Maleek yaushe zaka dawo, shi kansa Maleek din tana lura da irin yadda yanayinsa yake canjawa idan yana video call da ita a gaban Ummi.
“Ameer dan Allah kar wannan ya saka ka a damuwa, komai nufi ne na Allah kuma so da yawa mukan so abu ya zama ba alheri ba ne a garemu, wani lokacin kuma sai mu ki abu ya zama alheri a garemu”
“Yeah shiyasa na daga mata kafa ai, a yanzu dai ina nan ina ta addu'a Allah ya yaye min duk wani abu da nake ji a zuciyata akan son Nuwaira”
“Ni ma zan taya ka da addu'a, amman kuma a cikin wannan halin kake zancen yin aure wa zaka aura?”
“Ban gama yanke hukunci ba, domin a yanzu bana jin sonta a raina kamar yadda nake jin Nuwaira, bana son na aureta na cutar da ita, wata kila kuma zan iya koya har na fara, ina jin zan iya zama da ita na bata kulawar da ya kamata amman ba zan ji sonta kamar Nuwaira ba, sai dai idan har ta tabbata abun da Hajiya ta fada min cewar ita din tana sona sosai kuma a haka take kokarin ganin na samu abun da nake so, ni kuma ba zan bari zuciyarta ta karaya ba”
“Humairah ce?”
“Ita ce Ummi, Hajiya ta nuna min tana son na aureta tun kamin Nuwaira ta amsa cewar bata so na, Daddy ma shi kuma saboda alakar dake tsakaninki da su ta yi karfi, i hope idan har abun da nake hasashe ya kasance zaki yarda da ita”
“Ameer ni ai ko yar tsana zaka kawo min matukar kana kaunarta ni ma ina sonta, amman karka cilastawa kanka sonta karka tirsasa kanka sonta ka bari son ya shiga zuciyarka da kansa”
Ya amsa mata da kai. Kwatantawa yayi da lokacin sallah sannan ya fita daga dakin, duk yadda Ummi ta so ya je gidan Dr Zainab ya zauna sai ya ki, shi dai ya fi ra'ayin ya zauna gidan mahaifinsa, ya fita daga asibitin texi ya dauka zuwa cath sai dai kamin ya isa gari ya fara haske kasancewar tafiya ce mai tazara daga inda gidan yake zuwa asibitin da Ummi take kwance.
Two Weeks Ameer yayi tare da Ummi within days din nan babu ranar da baya waya da Humairah, da safe kamin ta tafi school zata yi waya da shi da dare ma idan zai kwanta sai ya kira ta, duk wani attention da take bukata yana bata not because of yana son ya so ta sai dan yana da bukatar duk wani abu da zai dauke masa hankali daga Nuwaira for now kwanciyar hankali yake bukata kamin yayi tunanin abun da ya kamata yayi next. Two days da zuwan Abiey tare da Namra da Mahmood har ma da Maleek dukansu a gidan Dr Zainab suka sauka domin gida ne a gurinsu ko a lokacin da take aiki balle kuma yanzu da yayanta ne suke aiki nan bayan ita ta yi retired. After two days da zuwansu ya shirya ya koma gida Nigeria. Sanin yadda Humairah take daukin ganinsa da yadda ta kwallafa rai na cewar sai ta tafi airport ta tarbe shi ya saka tun kamin ya isa ya fadawa direban gidansu lokacin da zai je ya dauke ta ya kaita airport din bayan ya sanar da ita lokacin da za su sauka. Dan haka ta shirya da wuri ba shiri kawai ta yi ba har da shirya masa abincin da ta san zai iya ci ta gyara dakinsa kamar wata mai aure da mijinta zai dawo. Misalin karfe daya jirginsu ya sauka Lagos, daga Lagos ya shiga wani jirgin zuwa Abuja. Tun kamin ya karasa fitowa Airport din ya hangota a gurin da aka tanada domin aje motoci, tana tsaye jikin motar tana ta rabon ido, murmushi ne ya kawata fuskarsa sai a yanzu yake jin marmarinta har ganin yayi kamar ta kara kyau saboda yar ramar da ta yi. Tana hangoshi ta doso inda yake da saurinta shi ma ya kara hanzari ya iso inda take sai ta yi tsaye tana kallonsa da wani irin dauki da murmushi a kumatunta.
“I thought rumgume ni zaki yi duk matsuwar nan da kika yi na dawo”
“Ba kyau ni ba muharramankar ba ce kuma akwai mutane sosai a nan”
Ya juya ya kalli gurin.
“Kowa sha'aninsa yake indai har da gaske kike yi kin yi missing dina hug me”
“Akwai mutane Ameer”
“I don't care hug me Humairah show me that you miss me”
“Ameer... Ba kyau fa”
“This will be the last one till we get married....!”
Wani dummnn ta ji maganar a kunnenta sai ta ji kamar ba daga bakinsa ta fito ba, tsaye tayi kamar hoto tana kallonsa ko motsi bata yi. Murmushi yayi irin murmushin da ya kara masa kyau ya warware jacket dinsa dake hannunsa ya dora mata saman abayar da ke jikinta ya rumgume ta.
“I miss you so much Humairah i never thought mun sabu haka ba sai a yanzu da na ganki”
Hawaye ya sauko idonta sai ya saketa ya dube ta, ganin hawayen ya saka hannunsa biyu ya share mata hawayen.
“Mu tafi”
Ya fara tafiya ita kuma ta kasa juyowa ta kasa tafiyar ta kasa komai har lokacin, baya baya yayi ya riko hannunta ya juyo da ita.
“Wasa nake miki kar ke ma ki yi breaking heart dina kamar Nuwaira i can see that you don't love me...”
Yana rufe baki sai ya rumgume shi ba tare da ta sani ba ta fashe da kuka. Murmushi yayi ya daga hannayensa ya daga ta jikinsa ya sumbanci goshinta sannan ya rika hannunta suka nufi gurin motar. Kamin ya isa direban ya bude masa baya, sai da ya fara sakata sannan ya shiga driver yaja motar.
“Ina zamu je?”
“Gidan Hajiya”
Ta fada cikin wata murya mai ban tausayi, kallonta yayi yana murmushi sai ya ga shi take kallo hawaye na sauko mata, a hankali ya kai hannunsa ya rika yatsunta ya murza a hankali yana kara yarda da maganar Hajiyar.
“Me kika shirya min?”
Ta kasa cewa komai shi kuma be fasa tambayarta ba har suka isa gidan, ita ta fara fita motar sannan ya fito yana fadin.
“Ya kamata a samu mai gadi, ko dan ku samu mai kula muku da gidan”
Ya fadi hakan ne kasancewar da za su shiga sai da direban ya fita ya bude gate ya shigo da motar, ita dai har lokacin ta kasa cewa komai gaba daya jikinta a mace yake, bata jin sautin komai sai maganar da Ameer yayi mata a airport, domin ya furta mata ita a lokacin da bata yi zato ba, ba ta ma yi tsammanin ya fahimci yaren soyayyarta ba. Wata tambaya ce ta zo mata a rai a lokacin da yake ta hira da Hajiya yana cin abinci, da gaske yana jin wani abu a zuciyarsa gema da ita ko kuma dai saboda zai cika burin Ummi ne? Har ya ci ya sude beta tofa komai a maganarsa da Hajiya ba. Sai da zai tashi ya shiga dakinsa yayi mata alama da abincinta yayi dadi. Bata hakaro ba ta ji shi a kusa da ita yana mata magana.
“Are you okay?”
Wani irin faduwa gabanta yayi kwarjinsa ya cikata bata taba jin wani abu kunyarsa ba sai a lokacin, ta sauke ido kasa tana lekawa ta gani idan Hajiya bata gurin domin sosai ya matse har tana kusan jin numfashinsa.
“Hajiya bata nan”
Bata yarda da sai da ta duba da kanta bata ma san Hajiya ta bar falon ba sai lokacin.
“Zata iya fitowa ta ganmu a haka”
Ya kama hannunta ya rike yana murzawa a hankali.
“Humairah ina da banbanci da mutane yawanci abun da yake saka wasu kunya ko tsoron ni baya saka ni, nan ai gidanmu ne, dan anganmu a haka miye a ciki?”
Murmushi yayi mai sauti ya ce.
“Zaki iya tuna lokacin da kika fada min cewar idan na taba ki ko na rumgume ki sai ki min fadan hauka kin nuna min ke ba yar iska ba ce”
Ta fisge hannunta da sauri, sai kawai ya rumgume ta yana dariya sosai kamar ba shi ba.
“Go ahead idan na sake ki yanzu ki mare ni”
Ya fada sannan ya sake ta, abun mamaki duk masifarta sai ta daga ido ma ta kalleshi balle ta yi yunkurin aikata abun da ta furta.
“Ashe ni da ke duk marasa jin magana ne”
Ta kasa cewa komai har lokacin, da murmushi ya zagaye ya shige dakinsa kiran Daddy na shigowa wayarsa, sai da ya shige sannan ta juyo ya kalli bayansa tana murmushi ta kai hannunta ta dafe zuciyarta ta nufi dakinta da gudu tana shiga ta maida kofar ta rufe ta fada kan gadonta ta lumashe ido...