Sashe 78
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya amsa yana picking calls din da Hajiya Jamila take masa.
“Hello Ammy”
“My Son lafiya kake?”
“Lafiya kalau I'm with...”
Yanayin yadda Daddy yayi masa da fuska ne ya saka shi fadar cewar yana tare da Daddy.
“With who?”
“With nobody”
“Mr Bashir yana kusa ne hala?”
“Yeah”
“To ka gaishe shi, na ga ka kira ni dazun zan daga sai kuma ka yanke kira, daman ina aiki shiyasa ban kira na sai yanzu”
“Daman wani abu na so na tambayeki, sai kuma na fahimci wahala ce kawai zan yi kuma ban san yadda zan fara miki bayanin ba”
“Akwai wata matsala ne?”
“No ba matsala ba ce, wata mata ce...”
Ganin Daddy na kusa kar ya masa fada yace ya sake shiga rigima da Maleek bayan duk abun da ya faru da kuma ja na kunne da yayi masa, ya saka shi yanke maganar.
“I will call you back”
Ya yanke kiran, Daddy ya girgiza kai.
“Zaka iya fada mata magana amman ba zaka iya fadawa mahaifinka ba?”
Ameer yayi dariya.
“Daddy ba fa wani abun ba ne, kasan za a iya sirrin da kai ban da kowa ba, zan kuma iya yi da ita ban yi da kai ba, kuma wannan ba wata magana ba ce”
“Then tell me, daman ban gamsu da zancen sakon nan ba”
Ameer yayi dariya.
“Wata mata ce, bari dai na fada maka gaskiya mahaifiyar Maleek ce, na hadu da ita a yau shi ne take fada min magana anyhow”
“Allah yasa ba Maleek din da kuka samu matsala da shi can baya ba”
“Miya hada ka da mahaifiyarsa Ameer baka jin magana ko”
“Ina ji mana Daddy”
“Ai dai na san ba zata hadu da kai haka nan kawai ta fada maka magana ba tare ka mata wani abu ba”
“Daddy ban mata komai ba, kawai ta dai na dan tana yarta ne kadan, shi ne ta fara fada min magana ba dan mun sha nono daya ba da sai ta cilasta ni aureta i think dai ko ciwon da yarta take ne ua saka ta fita hayyacinta, har da wani cewar mahaifiyarka da ake cewa ta mutu bata mutu ba ni ce ina raye, Alhaji Bashir ba mahaifinka ba ne, but Daddy ka san abun da ya ba ni mamaki har nake son na tambayi Ammy? Ce min ta yi na bincike Hajiya Jamila idan tana raye, toh ya aka yi ta san Hajiya Jamila?”
Ameer na kai aya Daddy ya mike tsaye ba tare da ya sani ba, counter dake hannunsa ta subuce ta fadi kasa. Ameer ya daga kai yana kallonsa.
“Wace ce wannan Ameer? A ina ka hadu da ita?”
“Mahaifiyar Maleek ce yaron da muka yi fada da shi, har tana cewa wai dan'uwana ne nake yaka, ina tunanin bata cikin hayyacinta ne shiyasa take fada hakan, saboda na taba yarta?”
“Me ka yi ma yarta?”
Ya sosa kansa yana jin kunyar Daddy dan ya san zai ce baya jin maganarsa.
“Soyayya na yi da ita, kuma sai na ji bana sonta shi ne na rabu da ita”
Daddy ya aje numfashi da karfi.
“Ta fada maka haka ne kawai saboda ta rikita maka tunani, amman wannan ai ba magana ba ce, zan yi kararta akan haka, bana daukar wannan ganganci, kai ma kuma rashin jin maganata zai haifar maka da matsala Ameer duk bayan abun da ya faru sai kuma ka sake bibiyar yaron nan?”
“Ba shi na bibiya ba, kanwarsa ce, kuma ita ta nuna min tana so na, Allah ne kawai ya tsare amman har son ta yi ta lalata ni, yanzu ai mun rabu babu ruwana da ita”
“Kar ma ka dauki zancenta, karka yarda da abun da take fada maka, kawai ta yi hakan ne saboda abun da ka yi mata, maganar sanin Hajiya Jamila kuma wata kila ka taba fadawa yarta ka santa ne, ko kuma ta san Hajiya Jamila can sani na dabam, dan haka karka ma fadawa Jamila wannan maganar ka saka hankalinta ya tashi, ka san dai yadda take sonka ba zata bar wannan maganar ba ni kuma bana son tashin hankali a yanzu”
Daddy ya nufi hanyar stairs kamar zai haura sai kuma ya fasa ya juyo ya nufi kofar fita, can kuma ya sake juyowa ya kalli Ameer dake kallonsa.
“Kar na sake jin maganar nan a bakinka, i will deal with her, domin wannan ba maganar da za kyale ba ce, akan me zaka ta kalli dana da hankalinta ta ce ďanta saboda kawai wani selfish interest nata, ba zan bar wannan ba”
“Okay”
Kawai Ameer ya fada sannan Daddy ya fice yana kokarin danne tashin hankalinsa. Sai da yayi nisa da fita sannan Ameer ya lura da counter sa data fadi kasa ya nufeta ya dauka ya bi bayan Daddy. Yana shiga part dinsa hullar kansa ce abar da ya fara cirea ya jefar a kasa, sannan ya daga wayarsa ya kira Hajiya Jamila da rabon da ya kirata tun da a lokacin da Ameer ya bata.
“Salamu alaikum”
Daddy be tsaya amsa mata sallama ba, bayan ta amsa kiran sai akwai ya kora mata da bayanin dalilin kiransa.
“Na ja masa kunne, amman na san ba ya jin magana zai iya kiranki ya tambaye wani abu akan wata mata ta ganshi tace shi danta ne, karki amsa masa?”
“Miya faru baka min bayanin komai ba, akwai ka fara da ba ni umarni? Sannan kuma ka saka hankalina tashi da jin wadannan kalaman naka”
Daker Daddy ya samu ya natsuwar fada mata abun da Ameer ya fada masa in brief.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Allah yasa ba Zahra ba ce, daman tana garin Abuja da zama?”
“Ba ni da wannan labarin, ko a lokacin Ameer ya samu matsala da abokinsa ban bibiya akan dole sai na san ko waye ko kuma dan waye ba, amman taya zata hadu da yaro a hanya ta fada masa wannan? Ameer ya girma a hannun tun yana karami har ya girma, karatunsa cinsa da shansa duk a hannuna yake, da dukiyata yake yadda yake so, shi yake kula min da wani bangare na kawancina, ina son Ameer shi yake maye min gurbin ďa namiji da Allah be bani ba, yadda nake son Ameer ko kaina bana so haka, taya zan yarda a raba ni da ďana, Ameer ďana ne that's”
“Mr Bashir kenan, ka ji kwatankwacin abun da na ji, a lokacin da ka raba ni da Ameer, kuma ka tsinke igiyar auren dake tsakaninmu”
Turo kofar dakin da Ameer yayi ya shigo yayi daidai ta lokacin da Daddy yake bawa Hajiya Jamila amsa.
“Ke aje wannan maganar a gafe, wacan da ne, wannan kuma yanzu ne babu wanda ya isa ya sauya yadda komai yake tafiya a yanzu, ba zan lamunta da wannan ba”
Daddy ya juyo yana ganin Ameer ne sai yayi saurin sauya maganar.
“Gidane na riga na siya an mallaka min, so zancen a maida kudi yanzu ba taso ba, sun san suna son gidan suka bari na siya? Akan me za su nemi daga ma kansu hankali har su daga min, su yi hakuri su bar ni na mutu a gida dan Allah...”
Ya yanke wayar Ameer kallonsa akwai yake domin be saba ganinsa a cikin irin wannan yanayin ba, yana waya yana fada.
“Ka bar carbinka a falon Mummy”
Ameer ya matso kusa da shi ya mika masa, Daddy ya karba tare da mika jikinsa ya rumgume ďanta.
“Allah ya maka albarka, ina matukar kaunarka Ameer, Allah ya kara shirya min kai”
“Ni ma ina kaunarka Daddy, Allah ya baka lafiya”
Ya sake shi yana sauke ajiyar zuciya, Ameer ya juya ya fice yana jin rashin natsuwa da halin da ya tararda mahaifinsa, da kuma wayar da yake.
“Dole na canja maka friends da guraren da kake zama,”
Ya fada bayan Ameer ya fice daga dakin yaja masa kofar. Hannu ya saka ya dafe kirjinsa tunawa kawai da yayi cewar Ameer ba dansa ba ne, sai ya ji duniyar da jindadin dake cikinta ya juye masa zuwa bakinciki da ciwon kirji a take.
“Kin zaki bukata miyasa kika ba ni? Rayuwata kawai matar nan take son ta ruguza kuma ta zubar min da mutunci, ba ta tunanin halin da Ameer zai shiga? Ta sani ta yi haka ko kuma kuskure ne? Ita din ce ma ko wata? Allah ka amshi rayuwata kamin ranar Da Ameer zai san ba ni na haife shi ba, ba zan bar hakan ma ta faru ba...”
Ya zauna gefen gadon yana jin kirjinsa na masa mugun ciwo.
WAIRA POV.
Sai da aka gama darasin sannan Malamin ya ciro katon lollipop ya mika mata, ba tare da tsayawa tunani komai ba ta karba, ta bude ta fara sha tana dariya kamar ba ita ce ta gama kuka ba. Tsareta yayi sai da ta shanye sannan yayi mata sallama ya tafi, ita kuma ya dauki jakar karatunta da dayan hannunta yayinda dayan hannun ke rike da zomon da daukarsa da yawo da shi ya zame mata kamar ibada. Sai da ta fara aje jakarta ta bude kofar falon sannan ta dauka ta shiga tunawa Ummi bata cikin gidan sai ya saka jin babu dadi a take yanayinta ya sauya. Saman ta hau ta shiga dakinta ta aje jakar a inda ta saba ajewa sannan ta sauko kasa ta aje zomonta akan kujera ta nufi hanyar Kitchen ta duba idan Hanne na ciki ta hada mata tea idan kuma bata nan sai ta hada da kanta. Tana leka Kitchen din ta hango Maleek tsaye rike da gorar ruwa sai ta tsaya jikin kofar. Da ido ya tambaye ta lafiya sai ta turo baki a shagwabe ta fara magana idonta har wani ruwa ruwan kwalla suke yana ce mata tak zata fara amayar masa da hawayenta
“Zan sha tea, ko cake ko a soya min arish ina jin yunwa”
“Hello Ammy”
“My Son lafiya kake?”
“Lafiya kalau I'm with...”
Yanayin yadda Daddy yayi masa da fuska ne ya saka shi fadar cewar yana tare da Daddy.
“With who?”
“With nobody”
“Mr Bashir yana kusa ne hala?”
“Yeah”
“To ka gaishe shi, na ga ka kira ni dazun zan daga sai kuma ka yanke kira, daman ina aiki shiyasa ban kira na sai yanzu”
“Daman wani abu na so na tambayeki, sai kuma na fahimci wahala ce kawai zan yi kuma ban san yadda zan fara miki bayanin ba”
“Akwai wata matsala ne?”
“No ba matsala ba ce, wata mata ce...”
Ganin Daddy na kusa kar ya masa fada yace ya sake shiga rigima da Maleek bayan duk abun da ya faru da kuma ja na kunne da yayi masa, ya saka shi yanke maganar.
“I will call you back”
Ya yanke kiran, Daddy ya girgiza kai.
“Zaka iya fada mata magana amman ba zaka iya fadawa mahaifinka ba?”
Ameer yayi dariya.
“Daddy ba fa wani abun ba ne, kasan za a iya sirrin da kai ban da kowa ba, zan kuma iya yi da ita ban yi da kai ba, kuma wannan ba wata magana ba ce”
“Then tell me, daman ban gamsu da zancen sakon nan ba”
Ameer yayi dariya.
“Wata mata ce, bari dai na fada maka gaskiya mahaifiyar Maleek ce, na hadu da ita a yau shi ne take fada min magana anyhow”
“Allah yasa ba Maleek din da kuka samu matsala da shi can baya ba”
“Miya hada ka da mahaifiyarsa Ameer baka jin magana ko”
“Ina ji mana Daddy”
“Ai dai na san ba zata hadu da kai haka nan kawai ta fada maka magana ba tare ka mata wani abu ba”
“Daddy ban mata komai ba, kawai ta dai na dan tana yarta ne kadan, shi ne ta fara fada min magana ba dan mun sha nono daya ba da sai ta cilasta ni aureta i think dai ko ciwon da yarta take ne ua saka ta fita hayyacinta, har da wani cewar mahaifiyarka da ake cewa ta mutu bata mutu ba ni ce ina raye, Alhaji Bashir ba mahaifinka ba ne, but Daddy ka san abun da ya ba ni mamaki har nake son na tambayi Ammy? Ce min ta yi na bincike Hajiya Jamila idan tana raye, toh ya aka yi ta san Hajiya Jamila?”
Ameer na kai aya Daddy ya mike tsaye ba tare da ya sani ba, counter dake hannunsa ta subuce ta fadi kasa. Ameer ya daga kai yana kallonsa.
“Wace ce wannan Ameer? A ina ka hadu da ita?”
“Mahaifiyar Maleek ce yaron da muka yi fada da shi, har tana cewa wai dan'uwana ne nake yaka, ina tunanin bata cikin hayyacinta ne shiyasa take fada hakan, saboda na taba yarta?”
“Me ka yi ma yarta?”
Ya sosa kansa yana jin kunyar Daddy dan ya san zai ce baya jin maganarsa.
“Soyayya na yi da ita, kuma sai na ji bana sonta shi ne na rabu da ita”
Daddy ya aje numfashi da karfi.
“Ta fada maka haka ne kawai saboda ta rikita maka tunani, amman wannan ai ba magana ba ce, zan yi kararta akan haka, bana daukar wannan ganganci, kai ma kuma rashin jin maganata zai haifar maka da matsala Ameer duk bayan abun da ya faru sai kuma ka sake bibiyar yaron nan?”
“Ba shi na bibiya ba, kanwarsa ce, kuma ita ta nuna min tana so na, Allah ne kawai ya tsare amman har son ta yi ta lalata ni, yanzu ai mun rabu babu ruwana da ita”
“Kar ma ka dauki zancenta, karka yarda da abun da take fada maka, kawai ta yi hakan ne saboda abun da ka yi mata, maganar sanin Hajiya Jamila kuma wata kila ka taba fadawa yarta ka santa ne, ko kuma ta san Hajiya Jamila can sani na dabam, dan haka karka ma fadawa Jamila wannan maganar ka saka hankalinta ya tashi, ka san dai yadda take sonka ba zata bar wannan maganar ba ni kuma bana son tashin hankali a yanzu”
Daddy ya nufi hanyar stairs kamar zai haura sai kuma ya fasa ya juyo ya nufi kofar fita, can kuma ya sake juyowa ya kalli Ameer dake kallonsa.
“Kar na sake jin maganar nan a bakinka, i will deal with her, domin wannan ba maganar da za kyale ba ce, akan me zaka ta kalli dana da hankalinta ta ce ďanta saboda kawai wani selfish interest nata, ba zan bar wannan ba”
“Okay”
Kawai Ameer ya fada sannan Daddy ya fice yana kokarin danne tashin hankalinsa. Sai da yayi nisa da fita sannan Ameer ya lura da counter sa data fadi kasa ya nufeta ya dauka ya bi bayan Daddy. Yana shiga part dinsa hullar kansa ce abar da ya fara cirea ya jefar a kasa, sannan ya daga wayarsa ya kira Hajiya Jamila da rabon da ya kirata tun da a lokacin da Ameer ya bata.
“Salamu alaikum”
Daddy be tsaya amsa mata sallama ba, bayan ta amsa kiran sai akwai ya kora mata da bayanin dalilin kiransa.
“Na ja masa kunne, amman na san ba ya jin magana zai iya kiranki ya tambaye wani abu akan wata mata ta ganshi tace shi danta ne, karki amsa masa?”
“Miya faru baka min bayanin komai ba, akwai ka fara da ba ni umarni? Sannan kuma ka saka hankalina tashi da jin wadannan kalaman naka”
Daker Daddy ya samu ya natsuwar fada mata abun da Ameer ya fada masa in brief.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Allah yasa ba Zahra ba ce, daman tana garin Abuja da zama?”
“Ba ni da wannan labarin, ko a lokacin Ameer ya samu matsala da abokinsa ban bibiya akan dole sai na san ko waye ko kuma dan waye ba, amman taya zata hadu da yaro a hanya ta fada masa wannan? Ameer ya girma a hannun tun yana karami har ya girma, karatunsa cinsa da shansa duk a hannuna yake, da dukiyata yake yadda yake so, shi yake kula min da wani bangare na kawancina, ina son Ameer shi yake maye min gurbin ďa namiji da Allah be bani ba, yadda nake son Ameer ko kaina bana so haka, taya zan yarda a raba ni da ďana, Ameer ďana ne that's”
“Mr Bashir kenan, ka ji kwatankwacin abun da na ji, a lokacin da ka raba ni da Ameer, kuma ka tsinke igiyar auren dake tsakaninmu”
Turo kofar dakin da Ameer yayi ya shigo yayi daidai ta lokacin da Daddy yake bawa Hajiya Jamila amsa.
“Ke aje wannan maganar a gafe, wacan da ne, wannan kuma yanzu ne babu wanda ya isa ya sauya yadda komai yake tafiya a yanzu, ba zan lamunta da wannan ba”
Daddy ya juyo yana ganin Ameer ne sai yayi saurin sauya maganar.
“Gidane na riga na siya an mallaka min, so zancen a maida kudi yanzu ba taso ba, sun san suna son gidan suka bari na siya? Akan me za su nemi daga ma kansu hankali har su daga min, su yi hakuri su bar ni na mutu a gida dan Allah...”
Ya yanke wayar Ameer kallonsa akwai yake domin be saba ganinsa a cikin irin wannan yanayin ba, yana waya yana fada.
“Ka bar carbinka a falon Mummy”
Ameer ya matso kusa da shi ya mika masa, Daddy ya karba tare da mika jikinsa ya rumgume ďanta.
“Allah ya maka albarka, ina matukar kaunarka Ameer, Allah ya kara shirya min kai”
“Ni ma ina kaunarka Daddy, Allah ya baka lafiya”
Ya sake shi yana sauke ajiyar zuciya, Ameer ya juya ya fice yana jin rashin natsuwa da halin da ya tararda mahaifinsa, da kuma wayar da yake.
“Dole na canja maka friends da guraren da kake zama,”
Ya fada bayan Ameer ya fice daga dakin yaja masa kofar. Hannu ya saka ya dafe kirjinsa tunawa kawai da yayi cewar Ameer ba dansa ba ne, sai ya ji duniyar da jindadin dake cikinta ya juye masa zuwa bakinciki da ciwon kirji a take.
“Kin zaki bukata miyasa kika ba ni? Rayuwata kawai matar nan take son ta ruguza kuma ta zubar min da mutunci, ba ta tunanin halin da Ameer zai shiga? Ta sani ta yi haka ko kuma kuskure ne? Ita din ce ma ko wata? Allah ka amshi rayuwata kamin ranar Da Ameer zai san ba ni na haife shi ba, ba zan bar hakan ma ta faru ba...”
Ya zauna gefen gadon yana jin kirjinsa na masa mugun ciwo.
WAIRA POV.
Sai da aka gama darasin sannan Malamin ya ciro katon lollipop ya mika mata, ba tare da tsayawa tunani komai ba ta karba, ta bude ta fara sha tana dariya kamar ba ita ce ta gama kuka ba. Tsareta yayi sai da ta shanye sannan yayi mata sallama ya tafi, ita kuma ya dauki jakar karatunta da dayan hannunta yayinda dayan hannun ke rike da zomon da daukarsa da yawo da shi ya zame mata kamar ibada. Sai da ta fara aje jakarta ta bude kofar falon sannan ta dauka ta shiga tunawa Ummi bata cikin gidan sai ya saka jin babu dadi a take yanayinta ya sauya. Saman ta hau ta shiga dakinta ta aje jakar a inda ta saba ajewa sannan ta sauko kasa ta aje zomonta akan kujera ta nufi hanyar Kitchen ta duba idan Hanne na ciki ta hada mata tea idan kuma bata nan sai ta hada da kanta. Tana leka Kitchen din ta hango Maleek tsaye rike da gorar ruwa sai ta tsaya jikin kofar. Da ido ya tambaye ta lafiya sai ta turo baki a shagwabe ta fara magana idonta har wani ruwa ruwan kwalla suke yana ce mata tak zata fara amayar masa da hawayenta
“Zan sha tea, ko cake ko a soya min arish ina jin yunwa”