← Book details Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 77 OF 176

Sashe 77

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallonta kawai yayi ya dauke kai ya fice kamar ba da shi take magana. Yana isa gurin motar da key ta ke hannunsa ya bude ya shiga, masu tsaron gidan suka bude masa gate ya fita ya fara shimfida gudu a titi kamar shi ma na ubansa ne.
A lokacin da ya isa asbitin sai ya samu guri ya faka yana ta kalle kalle, can kuma ya fito yana tunanin ta ina zai fara, domin sunan asibitin kawai Abdull ya turo masa amman be fada masa inda take ba, sai dai tunaninshi na ba shi ba zata wuce Emergency ba, sai dai idan ya shiga ya gane dakin yayi me? Bayan ya fada mata gaskiya kuma abun kunya Maleek ya ganshi ya zo gurin ma, wata zuciyar ta katsi hanzarinsa. Sai kawai ya fasa yin abun da zai yi a asibitin ya juya da zimmar tafiya sai ya ji an kira shi da wata bakuwar murya.

“Ameer”

Ya juyo sai yayi arba da Ummi dake rike da coolar Mahmood na gefenta rike da key mota, da alama su ma kusa da inda ya aje motarsa suka aje ta su ko kuma sun hangoshi. Hannayensa ya saka aljihu yana kallonta sai wani sham kamshi yake.

“Me ka zo yi nan?”

Ya kalli Mahmood sannan ya amsawa Ummi.

“Na zo ganin likita na ne, ya jikin yarki ance bata jin dadi”

“Magana kake hankali kwance kamar baka aikata komai ba, kalli idona tun da muka kawo Nimra asibitin nake kuka har yanzu, bata iya numfashi sai da Oxygen, bugun zuciyarta ya kasa daidaituwa, ta kasa bachi kuma Likitoci suna tsoron su yi mata allurar bachi saboda kar ta ki farkawa, kasan abun da ya fi min ciwo? Da ta fada min cewar ka fada mata soyayyar da kake mata ta karya ce, idan yau Nimra ta mutu wannan furucin naka ne ya kasheta, Ameer yar'uwarka kake son ka kashe..... Nimra kamar yar'uwa take a gareka saboda Nono na ta sha bayan kai ka saki, na gaji da ajiyar kayan da ba zai kai ni ko'ina ba, lokaci yayi da ya kamata kowa ya san gaskiya”

“Excuse me kamar baki cikin hayyacinki”

Ya fada yana daga kafadunsa, a take Mahmood ya ware hannu zai kai masa mari sai Ameer yayi karaf ya rike.

“Kai yaro Maleek ma yayi kadan balle kai kanensa, bakin rijiya ba gurin wasan makaho ba ne”

Ya jefar da hannunsa ya juya sai Ummi ta saka hannu ta juyo da shi da karfi.

“Weather you believe me or not, mutumen da kake attacking dan'uwanka ne, saboda ďana ne ni na haife shi kamar yadda na tsuguna na haife ka, uwar da ake fada maka ta mutu ni ce, Alhaji Bashir ba mahaifinka ba ne, ka je ka tambayi Hajiya Jamila idan tana raye, Ameer kai ďana ne jininka yau idan aka tsaga sai anga nawa a ciki, ba dan nono ďaya da kuka sha da Nimra ba, babu abun da zai hana na cilasta maka aurenta saboda ina son rayuwarta da farincikinta....”

Cikin wani yanayin mai kama da fada Ummi take fadin haka hawaye na mata zuba.
Baya baya Ameer yayi yana jin wani jim akansa.

“And Now kuma you're not making any sense...”

Ya nufi motarsa ya bude da sauri ya shiga yaja ta ya bar gurin. Jinginawa ta yi jikin wata motar dake kusa da ita ta fashe da kuka tana jin kamar ba ta yi abun da ya dace ba, sai dai ba zata iya cigaba da aje abun a zuciyarta ba, domin ba san iya abun da zai biyon duk wadannan abubuwan da suka faru ba. Mahmood kam mutuwar tsaye yayi yana kallon mahaifiyarsa ya kasa cewa komai, shi ma dai ganin yake kamar ta zauce ba a hayyacinta ta fadi duk abun da ya fito bakinta ba.

___________

Masu karatu na ce ana wata ga wata me kuke tunanin zai faru a gaba?
Anya Ameer zai yarda?
Abiey zai karbi Ameer matsayin step son dinsa kuwa bayan duk abun da ya faru?
Ya kuke tunanin rayuwar Nimra zata kasance?
Ni fa ban yarda da Malamin nan na Waira ta ba ku fa kun yarda da shi?
Anya Maleek be fara fadawa ba?
Abiey zai yarda Namra ta auri Shuraim kuwa?
Wai ina labarin Eid?

#Team Maleek
#Team Ameer

Ni dai ina Team Shuraim da Humairah, kun san na fi son masu zafi zafin lol.
[6/21, 10:22 PM] My S Line: *Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*

40

Tukin motar yake zuciyarsa na raya masa cewar, mahaifiyar Nimra ta fita daga hayyacinta ne, wata kila kuma ta yi haka ne saboda ta haddasa masa fitina saboda abun da yayi ma ďanta da yarsa. Ya girgiza kai yana tabe baki domin sam maganarta bata kama kanshi ba, kuma ba zata kama ba. Da tunanin ya isa gida sai ya bude motarsa zai fita sannan wani furucinta ya fado masa a rai na cewar ya tambaye Hajiya Jamila idan tana raye, how comes ta san Hajiya Jamila? Bayan ba a Abuja take ba a Kano, kuma shi be taba yin maganarta da Nimra ba balle yace ita ta fada mata, then taya ta san Hajiya Jamila, to him Hajiya Jamila is just he's father's ex wacce take matukar nuna masa kauna da soyayya.
Fitowa yayi motar ya fara dialing number Ammynsa wato Hajiya Jamila, tunanin me zan tambayeta ko ya fada mata and taya zai fara mata kwatancen mahaifiyar Nimra da ko sunanta be sani ba bayan Ummi da yaji Nimra na kiranta, tana daf da dauka ya yanke kiran ya nufi hanyar falonsu. Daman kofar a bude take dan haka ya saka kai ciki, i think this is the first time da be tsaya canja talkamin shiga falo ba ya haura sama da su har dakinsa, domin hankalinsa ba a nan yake ba, sai da ya shiga kuma sai ya fara tunanin me zai kawo shi dakin? Me zai yi a dakin? Ya juyo ya fito yana jin ransa kamar ya dan bace, but why ransa zai bace? A take ya tuna daga hannu da Mahmood yayi zai mareshi, wai kamar shi Mahmood zai daga ma hannu da sunan mari, and then mahaifiyarsa ta fara fada masa magana anyhow.

“Revenge take son dauka, ita ma dai bata da banbanci da yayanta”

A falon ya zauna, sam sam maganar Ummi bata sake shiga kansa ba, shi kawai mamakin yadda take shiga lamarin yayanta yake, ta wani bangaren kuma baya ganin laifinta saboda ita macece akwai rauni a tare da ita, kuma shi ne mai laifi da ya sake bibiyar rayuwar yarsu. Be wuce awa daya da yawowa gidan ba Daddy ya shigo gidan kamin ya isa part dinsa ya kira Ameer a waya domin hankalinsa ya tashe da zancen wukar da aka ce masa ya dauka.

“Na ce ka same ni gida ko?”

“Ina gidan fa Daddy, tun dazun nake jiranka”

“Alright”

Daddy ya fada sai ya fasa shiga bangarensa ya jufo apartment dinsu yana sanye da jallabiyarsa yar Egypt mai tsada, sai shining take kamar an shafa mata mai, hannunsa rike da counter.
Ameer na ganin shigowarsa ya mike tsaye domin baya son yayi masa magana a gaban Mummu wato Step mother dinsa shi a kullum kallon makiyiyyarsa yake mata.

“Daddy yanzu zan tafi part din ka ba”

“Toh gani ni na zo ai, zauna”

Daddy ya nuna masa kujerar da ya tashi sannan shi ma ya zauna, Ameer be zauna ba kamar yadda mahaifinsa ya bukata sai ya cigaba da tsayuwar yana juyawa ya kalli stairs.

“Daddy can't we talk private”

Daddy ya karewa falon da babu kowa a ciki kallo sannan ya kalleshi.

“Akwai wani a nan ne?”

“Wani dai zai iya shigowa”

“Wani abu ka aikata”

Ya zauna yana fadin.

“Come on Daddy na girma a wannan babin kuma”

“Toh ka yi da wukar? Da bakinka kake fada min cewar wata ka tsorata fa, wata wa? Sannan an fada min akwai yarinyar da kake treating badly why? Kai yaushe zaka canja ne Ameer?”

“Daddy ka taimake ni dan girman Allah ka fada min waya fada maka wannan maganar?”

“Ba zan fada ba, shi ma kaje ka karta masa rashin mutuncin ko? Zauna ka fada min me ka aikata, kuma karka kuskura yi min karya”

Ya zauna ba dan ransa ya so ba.

“Yadda labarin yake, ita yarinyar nan tun da ta gan ni ta bi ta tsane ni, yadda kasa ni na hana ta arziki, shiyasa idan na dan shigo sai na yi mata barazana, and daddy bata Tsorona sam kai tsaye idan na yi mata abu take ramawa kuma bata shakkar fada min magana any how i hate her, kuma kar kace wata babba ce karamar yarinya ce fa yanzu ma take jami'a”

Daddy ya samu kansa da murmushi domin ya lura da yanayin da yadda yake bashi labari ba irin na kullum ba ne, har wani yamutsa fuska yake yana son gwada yadda take masa tsiwa ba tare da ya san yana yi ba.

“Toh me ka yi mata da wukar?”

Ya juyo ya kalli Daddy.

“Sako nake so ta kai min wani guri shiyasa na yi mata barazana na san idan ban mata haka ba, ba zata ji magana ba, dan bata Tsorona kuma bata jin maganata”

“Do we need to fired her?”

“No no no no no no”

Ya furta hakan kusan sau biyar, daman da biyu Daddy ya tambaye shi ba dan ya sallame ta ba ko da ya bukata.

“A barta ta zauna, ai son nake na azabtar da ita har sai ta yarda na fita zafin kai”

“Baka ba ni labarin inda ta kai maka sakon ba kuma sakon me ne?”

“Haba Daddy karka min haka mana, na fa girma sai ka rika daukata karamin yaro”

“Ba yaro nake daukarka ba, ina maka kallon abokina ne da zai fada min sirrinsa ni ma na fada masa nawa sirrin”

“Na ji, amman dai for now be kamata ka san inda na aiketa ba, ba wani abu mao muhimmanci ba ne”

“Yes I'm very sure”

“Allah ya maka albarka”

Daddy ya fada yana kallon ďansa cike da alfahari.

“Ameen”
Chapter 77 · 0% Book details