← Book details Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 88 OF 176

Sashe 88

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“A kowane dare ina bachi da bakincikin rashin haihu, sai dai saboda son kwanciyar hankalin Jamila a wacan lokacin na kan boye abun na barwa raina, daga lokacin da ta gabatar min da kai a matsayin ďa sai na ji kamar ba ni da sauran kunci a duniyar nan, bayan bayyanar gaskiya sai sonka ya karu, a lokacin ba ni da mafitar da ta wuce na mallaka ka ga mahaifiyarka, duk kuwa da irin kaunar da nake maka saboda na san ta fini bukatarka, domin ita dole ce ta saka ta rabuwa da kai, sai dai bana tunanin dole ce ta saka ta kyautar da kai a gareni, domin ban cilasta mata ba, ban kuma san wani ya cilasta mata ba, sai dai ina kallon abin a matsayin kyautar daban zata ba daga Allah, rahma Allah ce yayi min kyautarka, kuma tun daga lokacin da Zahra ta tabbatar min da kai a matsayin ďa, sai bakincikina ya yaye farinciki ya ninku, musamnan da na sake aure na haifi yaya mata, sai an fahimci hikimar Allah na bani kai kyauta da yayi. A yanzu ma ban san manufar sa, wata kila akwai abun da yake shirya mana, sai dai ina jin kamar ba zan iya jure kallonka a wannan halin ba, saboda ina matukar kaunarka, taso da wannan maganar da Zahra ta yi zata haifar min da damuwar da bata da magani”

Ameer ya sake shi ya fadi kasa ya fashe da kuka, gaskiyar da yake son sani ya santa amman ta haifar masa da karin bakinciki, damuwa da kunci suka bude masa sabon shafi, gaba daya komai ya zame masa ka rubutun littafi, wani abun kuma kamar mafarki. A cikin wuni daya duniyarsa ta juye, rayuwarsa ta sauya, mutanen da yake kallo a matsayin iyayen sun tashi daga iyayensa, wadanda be sani ba be taba mafarkin rayuwa da su ba, su ne iyayensa ta ina zai fara? Kiran wasu da suna da iyayensa? Da girmansa?e yasa wannan abun be same shi a lokacin da yake da kurciya ba? Sai yanzu da girmansa? Har ya mike tsaye ya juya ya fice daga dakin Daddy be juyo ba, Stairs ya sauko be kula da wadanda suke falon ba ya fice zuwa gurin motarsa. Ya shiga yayi mata key yayi reverse, kamin ya isa gate masu aikin kula da gate din sun bude masa. Sai da ya hau titi tunanin ina zai je ya zo masa? Wa zai fuskanta ya fadawa damuwarsa? Damuwace da ba a magani balle a magance masa this is reality. Tafiya mai nisa yayi sannan ya isa unguwar su Humaira, domin zuciyarsa bata raya masa ya je ko'ina ba sai can. Yana shiga unguwar ana kiran sallah Isha'i immediately yayi parking daidai inda Masallacin yake ya fito rike da ruwa ya wanke fuskarsa ya kuskure bakinsa sannan ya rufe motar ya nufi Mallasacin. Second time kenan da yayi sallah a cikin jam'i kafadarsa na taba ta wasu mutanen da be san inda suka fito ba. After gama Sallah ya sake daga hannunsa sai kuma ya rasa addu'ar da zai yi. Sai mikewa yayi tsaye ya fito daga Masallacin ya dawo ta saitin inda gidansu Humairah yake ya tsaya yana ta kallon corner.

Ya dade a haka sannan ya samu wanda ya aika ya fada masa sunanta kuma yayi masa kwatancen gidansu da taba shiga da shi, matashin saurayin ya ce ya gane ta. Takowa yayi ya dawo gurin motarsa ya jingina. Almost 30min sannan ya hango Humaira ta fito, kallonta yake har ta iso inda yake, hakan nan kawai ya ji kamar ya rumgume ta domin yana a cikin damuwar da yake bukatar hug, sai dai ya san Humaira bata cikin irin matan da zai yi ma wannan matukar yana son su kwashe lafiya.

“I thought na ce na aje aiki a gurinku? Miye na sallamo min kuma? Da na san kai ne Wallahi da ba zan fito ba”

Ya dauke idonsa daga barin kallonta ya kalli wani gurin dabam tare da rumgume hannayensa.

“Damuwata ta wuce ta kamfani ko wani gurin aiki, Humaira ban san inda zan je ba, na bata da yawa daga abokaina, some of them ma idan ma fada musu kallon marar hankali zasu min, bana ma son su sani, ban san me zan yi ba, na rufe kaina a daki na yi kuka kamar jariri ko na fito waje na yi ta ihu? Ko kuma na je gurin mutanen da ban sani ba, wadanda suka kira kansu a matsayin iyayena na yi fada da su? Or should I just died?”

Kalamsa sun sanya jikinta sanyi, domin a cikin lafazi mai rauni da neman mafita yake maganar. A wani yanayi na tsoron hantararsa da fadansa ta dago wayarta ta haska fuskarsa. Hawayen da ta gani a fuskarsa ya matukar daga mata hankali, domin duk wani abun da zai iya saka Ameer din data sani kuka to ita zai iya ma kasheta wata kila.

“Me ya faru Ameer?”

“I just need someone to talk to kuma na zo nan na ji kamar bana son magana akan damuwar anymore, I'm sorry for bothering you”

“No... No... No please don't, you need me just tell me me ke damunka?”

Ya sauke kai kasa.

“I'm so weak”

Ya juya ta bude masa motar.

“Shiga ka zauna”

Ya taka ya zauna cikin motar sai ta kwantar masa da seat din, ta rufe motar ta zagaya dayan side din ta shiga ta zauna ta bar nata bangaren a bude saboda idon mutane.

“Do you want water?”

Ya girgiza mata kai, sai ta kalli ruwan dake cikin motar.

“I'm sorry akwai ma ruwa a motar, to zaka ci wani abu?”

Ya girgirza mata kai.

“Ko kana son wani abu? Kana son zuwa wani gurin? Ko kana son shan magani?”

Murmushi ne ya zo masa a lokacin da be yi zato ba, domin ya fahimci so take ta dauke masa damuwa kuma bata san ta inda zata fara ba. Ya juyo yana kallonta sai ta wayarsa ta yi ringing, ya dago wayar yana dubawa sai number Ummi ya gani be hadace number ba amman ya fahimci number ta ne tun a lokacin da ya saka number daga wayar Nimra zuwa wayarsa. Rejected call din yayi a take mood dinsa ya canja.

“Na san bama shiri da juna, and ka tsane ni na sani, amman ganinka a cikin halin ya haifar min da damuwa a yanzu, please fada min meke damunka?”

“Humairah how would you feel idan wata uwar ta fito a matsayin mahaifiyarki, ta ce matar da kike kallon a yanzu ba mahaifiyarki ba ce ita ce mahaifiyarki, and mahaifinki da a kullum kike masa addu'a saboda ya rasu sai wani ya fito yace miki yana raye, yana can wata duniyar yana rayuwa da wasu iyalan da ya fi kauna fiye da ke, ke kuma ya barki duk da yasan shi mahaifinki ne be damu ya baki kulawa da kaunar da kike bukata, and abun da ya fi komai ciwo ya ce kyautar da ke yayi, kuma ya san kina raye amman ya ki baki kulawa saboda baya kaunarki, sai daga wasu kike samu kulawa da kauna, kuma saboda ya rusa farincikinki sai ya fito da rana tsaka ya rusa mafarkinki...”

Humairah ta yi fuskar mamaki jin wani abun banbara gwai, tana kokarin fahimtar hanyar da yake dorata, kamin ta zaro ido ta rufe baki da sauri tana kallonsa...

UMMI's POV.

Cikin rauni da fargabar zai dauko ko ba zai dauka ba ta zabura a lokacin da yanke kiran nata. Sai ta hade yawu da karfi ta zauna bakin gadonta, daman dai she wanted to know halin da yake ciki domin ta fahimci yana da saurin fushi da zuciya, kar ya jefa kansa a wani hali. Sakon kar ta kwana ta aika masa sannan ta aje wayar ta mike tsaye sai ga kira ya shigo, da sauri ta dawo ta dauki wayar a zatonta Ameer din ne ya kirata sai ta ga Namra. Lumshe ido ta yi ta sauke ajiyar zuciya sannan ta amsa kiran.

“Assalamu Alaikum Namra....”

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”

Shi ne ya biyo bayan sallamar da Ummi ta yi wayar dake kunneta ta subuce ta fadi kasa...
[7/2, 9:43 PM] My S Line: 46

Labarin da Mahmood ya bashi ya zama masa wani sabon lamari a cikin kai da be taba mafarkin faruwarsa ba. A tunaninsa Mahmood zai fada masa cewar Ummi tana dauke da cutar cancer su tattauna akan cutar, amman sai ya fada masa wani labarin na dabam da fi karfin tunaninsa ya firgita kwakwalwarsa.

“Ya za'ayi na yarda da wannan? Ummi bata taba auren wani kamin Abiey ba, da ma Abiey ka ce sai na ce yes saboda Mahaifiyarsu Namra, amman Ummi bata taba aure ba, kuma bana tunanin zata samu ďan ta hanyar da be dace ba, idan ma gaskiya ba ne me zai saka ta ta boye tsawon shekarun nan bata bayyana ma kowa ba? Kuma ko sau daya bata taba nuna cewar Ameer ďanta ba ne? Maybe dai Ameer ya shirya duk wannan ne?”

Mahmood ya kalleshi.

“Da wa zai shirya? Ummi zai hada kai da ita ta fadi karya saboda me? Kuma ba shi ya fada ba ita ta fada in her own mouth, babu wanda ya matse ta, shi kasan a yanayin yadda ya bar gidan bana tsammanin zai yarda domin daukar yake ma bata cikin hayyacinta”

“Taya wai Ameer zai zama ďan'uwan mu? Not just dan'uwa ma ace dan Ummi ne wai ita ta haife shi da kanta? Ai kai ma kasan ba zai yiyu ba, wannan ba abun da hankali zai kama ba ne”

“Then ask her”

“Baka ganin halin da take ciki? Ba ta a halin da ya kamata ayi mata wannan maganar, amman ai dole gaskiya zai fito saboda Abiey ba zai dauka ba”

“Yanzu baka fahimci labarin da na gama baka ba, kenan? Abiey ma ya san da wannan, shi da kansa ya zo yayi mata fada akan me yasa ta fadi wannan abun sai gashi na gabatar masa da ciwonta a dole ya bar zancen”
Chapter 88 · 0% Book details