← Book details Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 72 OF 176

Sashe 72

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Subhanallahi barazana da makami Ameer? Kar zuciya ta dauke ka ka aikata kuskure, ka zo ka same ni gida yanzu nan, sai mu ji idan akwai matakin dauka kamata a adauka akan yarinyar kuma na ji abun da ta yi maka”

“Ba wata babbar matsala ba ce Daddy karka damu”

“Na ce ka zo mu tattauna, kuma karka tana yar mutane Ameer dan Allah”

“Okay Daddy gani nan zuwa”

Ya sauke wayar ya nufi motar ya cire key ya shiga ya zauna, tun da suka kama hanya suna tafiya bata ce masa uffan ba sai share hawaye take gabanta na zillo tana ta tunanin inda zai kaita zuciyarta sai sake sake take mata. Tafiya mai nisa suka yi sannan ya shigo umguwar manyan mutane ya fama gaban wani katon gida da gate din gidan ma ya isa bakauye kallo. Wani karamin littafi ya dauko ya fara rubutu, yana yi tana leko har ya gama ya nade takardar ya mika mata sannan ya bude gurin daya aje wayar Nimra ya dauko ya mika mata.

“Shiga gidan nan ki kai wannan wayar tare da takardar nan, amman idan kin shiga ki ce ke kawar Nimra ce kin zo ganinta, sai idan kun kebe zaki bata”

“Wallahi ba wata Nimra yanke min kai za'ayi wannan katon gidan na yan mafiya ne”

“Kwarai kin san mahaifina kudin tsafi yake da su”

Ta lake kafada tana kuka.

“Ni ba zan shiga ba, Allah ya fika”

“Ke look babu abun da za'ayi da katon kan nan naki, yarinyar da kika rika zagina kwanakin baya saboda ita, to gidansu nan, so nake ki shiga ciki ki kai mata wayar nan da wannan takardar, daga nan sai ki duba lafiyarta daman na ga kin damu da ita ai”

“Idan aka kashe ni hakkina yana kanka”

“Idan baki shiga ba, zan saka wukar nan na yanka ki, ko kuma na dauke ki na kaiwa abokaina su yi miki wulakanci son raina, dan haka ki zabi ďaya”

“Ameer me yasa kake mugu ne? Kana ta daukar hakkin mutane da basu maka komai ba”

“Toh bari na zabar miki a cikin ukun”

“Zan tafi, ka bude min motar”

“Idan na bude miki motar kuma ki gudu, na biki da wukar nan ko kuma na aika har gidanku a daukoki ai kin san dai na san gidanku ko?”

Ta daga kai, ta zabi shiga ne saboda shi ne mai sauki a cikin hukuncin abubuwan uku da ya shar'anta mata ta zaba, ta san ko da masu fille kai ne zata musu addu'a, idan kuma abun da ya fada ne a ciki idan ta aikata ga huta. Ta karbi wayar da takardar ta saka a jakarta sannan ya bude motar ya fita ya zagaya bangarenta ya bude mata ta fito.

“Kina yin wani abu kin san sauran”

“Me yasa kai ba zaka shiga da kanka ka bata ba, idan har da gaske gurinta ka zo”

“Ki kwankwasa kofa a bude miki”

Ya koma cikin motarsa ya zauna yana kallonta tana kallonsa, yana ganin ta matsa jikin gate din ya danna mata horn ta koma. Cikin tsoro ta kai hannu ta kwankwasa kofar gidan dake rufe sai da ta yi haka sau uku sannan aka bude kofar ganin mutumen daya fito yana sanye da uniform din police ya saka ta dan ji sanyi a ranta, ta juya ta kalli motar Ameer yayi reverse da ita zat tafi ya barta a gurin.

“Na zo gurin Nimara ne”

Ta fadi sunan a birkice tsabar tsoro da rashin rike sunan da ta yi.

“Ke wacece?”

“Kawarta ce”

Police din ya kalleta kasa da sama, shi dai be san yaran gidan na da kawayen da basa da motoci ba, yanayin mu'alamarsu ya saka ba kasafai suke zuwa gidan kawaye ko kawaye su zo nemansu ba, idan ma sun zo suka zo da manyan motoci ne, sai dai Humarai a kasa ta zo duk kuwa da ya hango motar da ke kokarin juyawa wacce yake kyautata zaton a ciki aka kawota.

“Kun yi da ita zaki zo?”

“Eh ga ma wayarta a hannuna tace na zo mata da shi”

Ta saka hannu a jaka ta dauko wayar tana nuna masa.

“Toh jira a nan ina zuwa, wa a ce mata?”

“Ka ce... Ka ce... Ka ce.. Aisha Humaira ce Ameer”

“Aisha Humaira Ameer?”

Ya maimaita sunan sai ta daga masa shi.

“Yeah”

“Okay shigo sai ki jira nan”

Ya matsa jikin kofar ya samu shiga sai ya rufe gate din ita kuma ta tsaya kusa da inda ya nuna mata jikinta na rawa gabanta na faduwa. Kamin yau idan wani ya zo yace yana son ganin masu gidan kai tsaye masu gadin suke ba shi damar ya shiga domin haka Ummi tace musu, sai dai Umarnin da Abiey ya bada na cewar kar a sake Nimra ta fita gidan ya aaka suka tsaurara tsoro gudun kar wani abun ya faru a dora laifin a kansu.
[6/18, 7:54 PM] My S Line: *Littafin WANI GARI na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*

38

MALEEK POV.

Yana shiga dakinsa ya shiga closet dinsa ya aje jakar ya fito ya sauko downstairs ya zauna a dayan side din da kujeru suke, sosai ya maida hankalinsa gurin plasma dake kunne yana kallon film da MBC 2 suke hakawa. Sai da suka tafi talla tukuna hankalinsa ya kai gurin wayarsa dake kan ďayan set din kujerun tana ringing da hanzari ya isa gurin ya dauki wayar tare da amsa kiran da ya biyo bayan miss calls din dake bayyana a saman kiran.

“Maleek kana ina?”

“Ina cikin gida, bana kusa da wayar ne”

“Ka same ni bangarena zamu gaisa da mijin Namra, na kusa karasowa”

“Okay”

“Kuma ban ce ka zo min da kananan kaya ba”

Yayi murmushi kawai ya sauke wayar yana kallon kansa domin kananan kayan ne a jikinsa. Haurawa yayi sama ya canja tufafin jikinsa zuwa shadda ash color ya fesa turare ya saka kular Zanna bukar yar ubansu, ya canja talkamin kafarsa ya saka wandanda za su dace da shaddar jikinsa be damu da duba madubi ba domin ba yin kyau ko akasin haka ne a gabansa ba burinsa yayi shigar mutunci kamar yadda mahaifinsa ya bukata, be fice dakin ba sai da ya murza wani karamin turare a hannunta ya shafe hannunsa zuwa wuyansa, ya dauki wayarsa ya saka aljihu sannan ya sauko stairs din yana wani irin kamshi na tashin hankali kamar shi ne angon. Kofar fita falon ya nufa tana tafiya kamar mai tausayin kasa.  Entrance din bangaren Ummi ya tsaya yana kallon gate din gidansu, a hankali ya juyo yana kallon motar Shuraim sai ba motar yake kallo kai tsaye ba, kyakkyawar halittar Allah mai matukar burgewa da daukar hankali yake kallo, Waira ce tsaye jikin motar can side din da ace bata mike tsaye ba ba zai iya sanin tana gurin ba, ita ma bata mike tsaye dan sanin cewar shi ne tsaye a gurin ba, sai dan kamshin turaren da ya kaiwa hancinta hari ta kasa jurewa har ta leko a zatonta zata ga Sulem dinta ne sai ta yi arba da abokin fadanta.

Yayi kyau, kyau da ake kira da kyau irin kyaun dake fitar da asalin kyau da siffar kyau a jikin namijin, da haramun ne ka yi masa kallo daya ka dauke ido. Hular kansa ta zauna das kamar sai da aka sauna kalar zaren da girman aka zaka masa domin shi kadai kawai. Shaddar ta haska fatarsa ta kara masa kwarjini da cikar izza irin ta jinin sarauta, daga ita har shi sun dauki lokaci suna kallo junansu, ko wane na tantance kyaun dayan jinsinsa. Waira ce ta fara sulalewa kasa ta zauna tana rike da zomonta, a lokacin da idonshi suka daina ganin kyakkyawar fuskarta sai hayyacinsa ya dawo jikinsa ya dauke kai ya sake maidawa gurin gate din yana hade yawun bakinsa da suka tsinke...
Me kike yi a nan wa kike jira, duk baya bukatar amsarsu, yadda aka yi ta fito daga cikin falon ta zauna a gurin ne abun tambaya a gurinsa, jira ko me take yi a gurin ya san amsarsu, ko da ya tambaye ba zai wuce tace masa tana jiran Sulem ba, domin a gurin motarsu ta tsaya. Yana kokarin zuba hannayensa aljihu ta sake lekowa irin leken da be yi kama da gulma take ba, ta gefen ido yake kallonta rabin idonsa na kan gate din da aka buden ragowar kuma suna kan Waira dake kallonsa, tana ganin motar Abiey ta kunno kai cikin gidan sai ta mike tsaye gaba daya ta bar jikin motar ta nufo hanyar shiga falon inda Maleek yake tsaye. Tana doso inda yake tsaye gabansa ya tsanata faduwa na rashin dalili kuma ya kasa kallonta har ta iso gurin ta ratsa gefensa ta wuce. Sai da ya sauke numfashi mai nauyi sannan ya samu sukuni a zuciyarsa, tun da yake a rayuwarsa be tana jin abun da yaji a yau ba. After Abiey ya faka a compound din gidan ya sauko ya isa gurin motar yana masa sannu da zuwa.

“Maa Shaa Allah, haba ko kai fa yanzu da ban maka magana ba da kananan kayan zaka saka ka fito a matsayinka na yayan Namra”

Murmushi yayi as respond ya karbi jakar dake hannun driver mahaifinsa suka jera a tafe kamar ba uba da ďa ba, kamin su karasa apartment din Abiey yayi masa tambaya uku ya kasa bashi amsar ko daya.

“Ai tun kamin ya zo a matsayinka na dan'uwanta kuma namiji, wanda nake sa ran ko bana raye ko kuma nan gaba kadan zaka iya gudanar da komai ya kamata ace ka mata tambayoyi akansa”

“Abiey ka san ba wani sakewa nake da su sosai ba, so ban cika son shiga rayuwarsu ba”

“Amman ai na ga alakarka da su yanzu ba kamar da ba, ka samu lafiya inji Umminku kasan ita ce kullum take ganin baka da lafiya”
Chapter 72 · 0% Book details