← Book details Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 138 OF 176

Sashe 138

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Addu'ar da Mahmood yayi sai duk suka amsa da ameen. Duk a cikin kyautukan da suka mata babu wanda ta fi so kamar abun hannun da Ameer ya daura mata, da kuma alkur'anen da ya bata, domin ta dade tana sha'awar kur'ane yawan sauraren da take idan Maleek na karantawa da kuma abubuwan da Ameer yake fada mata sai yace akwai a ciki kur'ane sai dai bata san yadda zata yi ta karanta ba. Sai dai ta zuba masa ido ta yi ta kallo tana shafawa, Prayer mat din da Abiey ya bata kuma sai ta taimaka mata sosai gurin yin ibadarta yadda ya dace tana fadar duk abun da nau'urar dakw ciki take fada, kana kuma ta bi yadda take nunawa. A kowa ce Sallah. Abiey yayi magana da Cp dake Abuja ya fada musu tafiyar da Nuwaira zata yi har ma da dansa Maleek da zai rakata, sai aka basu police biyu da za su raka su, bayan sun zo har gida sun yi mata tambayoyi sai ta fadi iya inda zata iya ganewa a kofar garinsu, daga inda ta fito zuwa gurin da ta hadu da Ameer, domin nan kadai gurin da ta sani, sauran abubuwan da suka faru bata iya labarta ko daya, kasancewar bata cikin hayyacinta aka kawo ta asibiti, daga Katsina zuwa Abuja ma bata san komai akai ba domin ko da aka iso tana bachi. Police biyu aka basu daga Abuja bayan an sanar musu wasu police biyu za su tare su daga Katsina tare da wanda ya san hanyar garin har zuwa inda Nuwaira zata gane.

Tun cikin dare Ummi ta shiryawa Nuwaira komai nata, ta zaunar da ita ta yi mata nasiha ta karfafa mata guiwar cigaba da rike addininta konda kuwa danginta za su nuna basa son addinin nata. Namra na tsaye jikin kofar dakin rumgume da hannayenta tana kallon Nuwaira dake ta rutsar kuka kamar an mata mota, shigowar Ameer ne ya saka Namra ta hanye daga jikin kofar ta karasa cikin dakin kusa da Ummi ta tsaya daga tsaye yayin da Ummi take zaune Nuwaira na jikinta sai kuka take, bata son rabuwa da Ummi kuma bata san me zata je ta tararda a garin ba, zancen sarautar yana nan ko kuma kasheta za'ayi? Ya za su karbeta idan suka ji ta canja addini da al'ada? Yana daga cikin abubuwan da suke matukar daga mata hankali.

“Ummi Daddy ya ce na zo da ita, yana son su yi bankwana”

Maganar Ameer yake yana kallon sahibarsa yadda take kuka abun ba dadi yake masa ba, shi ma tafiyarta domin kawai ta zame masa dole ne amman baya son rabuwa da ita ko na minti daya, idan kuma ya tuna da Maleek zata tafi sai ya ji hankalinsa ya tashi domin ganin yake kamar shakuwa ce zata kara shiga tsakaninsu. Nuwaira ta dago daga jikin Ummi ta kalleshi da jajayen idonta, hakan ya bashi karfin guiwar karasowa ya risina inda take zaune yana kallon fuskarta.

“Daddy na yake son ganinki, na fada masa gobe zaki tafi shi ne ya ce na zo da ke yanzu”

Ta mike tsaye sai ya ja baya domin bata dama ta taka, bandaki ta shiga ta wanke fuskarta sannan ta fito ta dauki daya daga cikin hijab din da Ummi ta bata ta saka daya, sannan ta kalli Ummi alamar tana neman izinin fita, Ummi ta daga mata kai

“Tafi”

Ta juya ta wuce gaba Ameer ya bita baya, Namra da Ummi suka bi Ameer da kallo ganin ya zama kamar wani jela.

“Ameer ya ba ni mamaki Ummi, kamar ba shi ba”

“Ciwon So kenan Namra, mai haukatar da mutum mai tsutsuta bawa ya firgita kwakwalwarsa, mai rufe idon mai yinsa ya saka yin abubuwan da ba su dace ba, i was in his shoes before shi ya saka na aikata duk abun da na aikata a yanzu, Abiey ma hauka ne kawai be yi ba a lokacin da ya rasa ni, amman Ciwon So ciwo ne mai wahalar magani”

Ummi was talking from experience tana kallon kofar dakin har lokacin. Wani bangare na yarenta kawai Namra ke iya ganewa domin ita ma ta ga zahiri a abun da ya faru da yar'uwarta, kuma ita tana cikin dakin so.

AMEER POV.

“Zaki yi ta yin kuka ne har hawayenki su kare Nuwaira?”

Ta dago ta kalleshi.

“Baka san yadda nake ji ba, bana son rabuwa da kowa”

Yayi murmushi domin shi kan ya fita sani da jin duk wani abu da take ji na kewa da zata yi da mutane.

“Duk yadda kike ji, na fiki jin haka ke kewa ce kawai kike ji a ranki, ni kuma wata kalar azaba da radadi nake ji, saboda zaki tafi ne da ruhina na zuciyata, ban san ya zan kasance ba idan kika tafi, hauka zan yi? Ko kuma zan iya jurewa na yi hakuri na cigaba da rayuwa da tabon da kika min a zuciya, duk yadda zan misalta ba zaki taba ganewa ba, amman dai Daddy ya dora ni akan shawara, ta addu'a da neman zabin Allah kuma na dage da haka, wata kila babu alheri a tarayya ta dake shiyasa ma kika dage sai kin tafi, sannu sannu komai zai yaye har na manta da ke”

Yana maganar tana kallonsa har ya gama be kalleta ba, ita kuma bata fasa kallonsa ba har suka isa gidan, sai a sannan ya cire tissue ya mika mata. Ta karba ta share hawayenta ya fita motar ya zagaya ya bude mata ta fito ya rufe motar suka jekara suna tafiya har suka shiga cikin falon Mummy ta fara yi musu lale marbabun fuska a sake baki har kunne.

“Sannu da zuwa Marhabun lale”

Mummy da yayanta suka tarbi Nuwaira da farinciki da jindadi, Ameer da kansa ya shiga ya sanar da Daddy zuwan Nuwaira suka jero a tare suka fito daga bangaren, Daddy kamar ya hade Nuwaira ba saboda Ameer yana sonta kawai ba, sai dan addinin musulunci da ta shiga ya kara mata kwarjini da farinciki a gurin kowa. Liyafa Mummy ta shirya mata, sai dai ita kasa cin komai ta yi saboda tunanin gaba da take. Bayan sun gama cin abincin Daddy ya aika yarsa ta dauko masa ajiyar da yayi a dakinsa, ya gabatarwa da Nuwaira, sarka zinari ce mai matukar ktau da tsada irin mai cika wuya wadda ke hade da abun hannu da agogo.

“Wannan duka na ki ne, ina fatar idan kin tafi ba zaki manta da mu ba, musamman ma ďana Ameer, yana yawan maganarki kusan ya zama kamar wani soko akanki, ki rika tunawa da shi kina masa addu'a ko dan silar shigar da yayi miki a addinin Allah mai tsabta da natsuwa”

Ta saka hannu biyu ta karba, ba lallai ta fahimci minene ba saboda a garensu ba haka ake sarrafa zinariya a yi ado da shi a garinsu ba. Amman ta san abu ne mai kyau da tsada ganin yadda yake daukar ido.

“Zinari ne wannan, yana da kyau sosai”

Ta girgiza kai da sauri.

“Ba zan iya karbar wannan ba yayi yawa”

“No ba a maida kyauta karki ce haka ki karba mana”

Mummy ta fada tana kallonsu da murmushi. Godiya sosai Nuwaira ta yi ma Daddy har ta rasa kalaman hadawa ta nuna masa farincikinta. Mummy ma ta yi mata kyautar turaruka da earring masu kyau na GL da lace mai kyau. Suka rakota har gurin mota ta shiga suna daga mata hannu.
[8/6, 7:07 PM] 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲: 72

A tunaninta gida Ameer zai nufa da ita kai tsaye bayan ya bar gidan Daddy. Sai ganin ganin ya faka a gaban wani gate ya fita ta bude gate din ya shiga da motar ya sauya tuninaninta.

“Ina ne?”

Ta tambaya a lokacin da ya bude mata motar take kokarin fitowa.

“Kakata yau suka tare, na fada mata zan kawo ki, ki musu bankwana”

Kamin ya rufe motar Humaira ta fito rike da waya a kunnenta amman hakan be hanata yin welcoming din Nuwaira ba, cikin kyakkyawar tarba fuska a sake. Ameer ya wuce gaba Nuwaira ta bi bayansa har suka shiga cikin falon da ba a gama sakawa kaya ba, shi ya fara yi mata nuni da inda zata zauna sannan ya shiga dakin farko dake cikin falon. Humaira ta shigo after minutes da zaman Nuwaira a falon tana sake mata maraba da zuwa.

“Sannu da zuwa, Ameer yana yawan ba mu labarinki, kusan kowa ya san ki tun farko fara haduwarku ya fada kin yadda ya rikice akanki, bari na baki abun sha kar na cika ci da surutu”

Ta tashi ta shiga dakin da ke nuna madafa ce ta dauko mata ruwa da taliyar da ta girka, domin su ne kadai abubuwan da zata iya samu for now a gidan, kasancewar tarewar ta wuri ce kuma hankali Ameer ba kwance ba, be gabatar musu da komai ba, arzikinsu daya Daddy be manta da su ba, shi yayi musu komai a gidan. Nuwaira ta kai hannu ta dauki ruwan ta rike kamar wadda bata san abun da zata yi da shi ba. Can kuma ta daga kai tana kallon Ameer davya fito dakin Hajiya na bayansa tana takawa a hankali da sandar guragu, Bahijja na bayanta sai leken Nuwaira take kamar ba zata karaso kusa da ita ta kalleta ba.

“Sannu da zuwa yau bakuwar Ameer ce a gidan mu”

Nuwaira ta mike tsaye tana kallonsu, sai wani irin take ji, ta bakuncin mutanen da suka san da labarinta ita kuma bata san su ba. Hajiya ta karaso ta zauna tana kallon Nuwaira ita dai zuciyarta bata gamsu da yarinyar ba, ba dan tarbiyarta ko wani abun ba, sai dan ganin take ta fito daga bangaren Ummi ne, ganin take idan ya aureta Ummi zata sake dauke mata shi ne bayan duk abun da ta yi da farko, hakan na nufin ta ci nasara kenan. Cikin rashin natsuwa da sakin jiki Nuwaira ta gaisa da su, sannan ta yi musu sallama suka fito ita da Humaira ganin kamar Ameer ba zai fito yanzu ba.

“Da alama kin matsu ki bar gidan nan”
Chapter 138 · 0% Book details