Sashe 61
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya karashe tare da kwafa sannan ya juya ya nufi kofar ďakin ya bude, sai yayi arba da Waira, ita ma ta yi arba da shi da bulalar wayar dake hannunsa, hannunsa dake rike da bulalar ta fara kallo sannan ta kalli fuskarsa dake hade kamar bakin hadari, a zatonta ya gama dukan Nimra ne ya fito ita ma yayi mata nata, sai ta kwala kara iya karfinta har sai da ya dafe kunnensa ya kauce daga gurin ya sauka kasa da sauri zuwa ya nufi bangaren mahaifinsa yana jin kansa na mugun sarawa, domin tana da ƙyaƙyar muryar irin wannan mai shiga har can cikin amon kunne. Ummi ta fito da sauri tana share hawayenta ganin Waira tsaye a kofar ďakin Nimra ya saka ta karaso da sauri, ganin Ummi ya saka Waira ta yi shiru domin a yanzu ta gama fahimtar babu lafiya a gidan, ganin Ummi ma tana kuka.
“Lafiya? Waya taba ki?”
“Ya Maleek ya dauki bulala zai daki Waira”
Ummi ta rika hannunta taja ta suka nufi ďakinta, hakan ya bata damar rumgume Ummi ta sauraren dalilinta na kuka.
NIMRA POV.
Maleek na fita daga dakin ta ji ihun Waira da kuma Isowar Ummi taja hannunta suka bar gurin ta san, Ummi ta ajeta a gefe kenan, ba dan haka ba da yanzu ta iso da gudunta a lokacin fa Maleek yake dukanta ta tare mata dukan har ma ta yi fada da Maleek din, amman gashi bata zo ba, sai da Waira ta yi ihu, furucin da Maleek yayi mata da kuma bacin ran da ta gani a fuskar mahaifinta, ya matukar daga hankalinta ya kuma tabbatar mata da cewar ba za su taba yarda ta auri Ameer ba, ita kuma a yanzu tana jin ta shiryawa mutuwa akansa, bata taba so ba sai akan Ameer wani namiji be taba shiga zuciyarta ta juyawa yadda yake so ba sai Ameer, dabam wanda be saba ba idan ya samu ba shi ma so da sauki, iyakar gaskiyarta tana nufin mutuwa idan har aka rabata da love of her life, bata ta inda zata rayu ba idan har iyayenta suka zabi raba soyayyar da Ameer. Daker ta tashi ta tsaye ta nufi inda ta nefar da key din mota da wayarta ta dauka idonta daya a rufe saboda dukan da Maleek yayi mata ya same ta a dayar idonta ne, bakinta na a kumbure yake har lokacin yana jinin naushin da Abiey ya kai mata a baki, bata ko iya taka kafarta da kyau sai dingishi take, ko'ina na jikinta tsami yake duk inda Maleek ya same ta da bulalar ya kumbura mata jiki, yayi mata ja. Idonta har ya canja kala saboda kuka har wani jiri take gani. Sai da ta fara lekowa ta ga babu kowa a saman sannan ta sauko nufo downstairs tana tafiya dake tana sauri ta sauka, kanta babu ďankwali balle ayi maganar mayafi, haka ta sauko falon ta nufi kofa ta fita babu talkami da faduwar gaba ta fito falon ta nufi gurin motar da Ummi ta bar mata tana hawa tun bayan da Ameer ya ci uban tata motar. Ta bude ta shiga ta yi mata key kamin ta yi reverse kamar zuciyarta zata fado ta ji, masu gadi na ganin ta kunna mota sai suka fara kokarin bude mata gate, kamin ta iso har sun gama budewar ta nan ta samu sa'ar ficewa da sauri tana wani irin gudu. Fita ta yi daga unguwar amman hankalinta be kwanta ba har sai da ta ganta a bakin gate din gidan Ameer, tana faka motar bata tsaya kashewa ba ta bude ta fito ba dan tana da tabbacin Ameer yana cikin gidan ba ta nufi kofar falonsa ta tura kofar tana budewa sai ta fadi cikin falon saboda babu kuzari a jikinta kanta ma kamar zai tsage gida biyu take jinsa saboda ciwon da yake. Ameer dake rike da gorar ruwa da waya a kunne yayi saurin yanke wayar ya aje ruwan ya nufota.
“Nimra wooo what happened?”
Ta dago ta kalleshi tare da kai hannu ta taba fuskarsa.
“Ameer. Abiey, Ummi da Ya Maleek ba za su bari na aureka ba, ba za su bari mu zauna a tare ba, Ameer idan suka ba ni da kai mutuwa zan yi, ni kadai na san yadda nake ji a raina, Ameer guduwa zan yi, mu tafi wani gurin har sai iyayena sun sauka daga fushinsu, zan iya daukar komai amman ban da rabuwa da kai, ina sonka Ameer...”
Lokaci daya aka jefo masa digon tausayinta a ransa, yadda aka yi mata jina jina da jiki kuma har ta baro gidansu a irin wannan yanayin babu mayafi babu talkami hawayen da take zubar kawai sun isa su sosa masa zuciya.
“No Nimra ba zaki aikata haka ba”
“Ba zaman ban za zamu yi idan muka gudu ba Ameer aure zamu yi, mahaifina ba zai saurareni a yanzu ba, kalli yadda Ya Maleek yayi min da jiki”
Ta nuna masa jikinta, duk sai ya ji wani iri domin saboda shi komai ya faru, a kuma manufarsa ta daukar fansa ba dan yana sonta ko son aurenta da gaske ba. Ya saka hannunsa ya daga ta daga kasa ya zaunar da ita kan kujera ya rumgumeta.
“Ba zamu aikata hakan ba Nimra, ni ma da kika ga na gudu saboda Mahaifina ya kore ni da kansa ne, ke kuma mace ce hakan zai iya janyo miki matsala ba ga iyayenki kadai ba”
“Ameer ba ka ce kana kaunata ba? Zaka iya yin komai akaina?”
Yayi shiru kamar mai tunanin amsa mata, ba kansa yake ji ba, ita yake ji idan har ta aikata abun da zuciyarta ta raya mata zata jefa kanta a matsala ne kawai ne.
“Hakan ba yana nufin na sake jefaki a wata matsala a yanzu ba, Nimra I'm ever to fight for you now i can't let your family hurt you again, I'm serious this time”
“I think I'm losing my mind now, please don't let me down Ameer ina matukar kaunarka, dan Allah mu gudu idan mahaifina ya san na sake zuwa gurinka kashe ni zai yi”
Ta saki jikinsa ta mike tsaye jikinta na rawa. Sai yayi saurin mikewa shi ma ya rumgume ta.
“Shikenan zamu gudu, amman yanzu akwai wanda ya san kin zo nan?”
Ta girgiza masa kai alamar aa.
“Amman za su iya zuwa nema na a nan, Abiey zai iya kashe ni idan ya zo ya gan ni a nan”
Ya saketa ya nufi inda ya aje wayarsa ya dauka ya dauki key dinsa ya dauki wayarta ya rika hannunta ya fito da ita da sauri, a motarsa ya saka ta, sannan ya nufi motarta ya kashe ya dawo gurin motarsa ya shiga mazaunin direba ya tashi motar, ana bude masa gate ya fice da gudu, sai da yayi nisa sannan ya faka ya kwantar mata da kujerar motar yana kallon idonta dake rufe fuskarta har ta fara canja kammani. Tunanin inda za su je su boya ya fara yi kamin ya mike hannu ya rike hannunta shi dai ya san har ga Allah baya son ta a zuciyarsa sai dai kuma tausayinta ya cika masa zuciya a yanzu, domin ya fahimci ta gama haukacewa kansa.
[6/17, 10:49 PM] My S Line: 32
*W_G -it's not free, pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
Jin ya faka ya saka ta bude idonta daya domin ďayan ya rike ya rufe a yanzu ya like, tana kallon gurin ta dube shi.
“Me mike yi a nan?”
“Dole zamu zauna mu yi tunani inda zamu tafi mana, kuma kin ga muna bukatar kudi mai yawa da zai wadace mu a iya zaman da zamu yi, and dole mu tsara komai kamin mu tafi, kin ga babu wanda ya san muna zuwa nan balle ya saka mana ido ko a fada cewar an ganki”
Ta fashe da kuka.
“Ban tana tunanin zan iya aikata haka ba Ameer dan Allah karka ci amanata, karka bar ni dan Allah”
Ya saka hannunsa ya rike fuskarta.
“Ni na janyo miki wannan abun Nimra, so i promise you ba zan kyale ki ki sake aikata kuskure ba, kuma ba zan kyale ki sha wahala ke kadai ba”
Ya sumbanci hannunta, tun da yake a rayuwarsa be taba jin tausayin wani mutum lokaci daya kamar yadda ya ji tausayinta a yanzu ba. Yarda da ta yi da shi ya saka ta amince da kalamansa har ya bude motar ya fita ya zagaya side dinta ya bude mota ta sauko sai yayi mata side hug domin bata iya tsayuwa da kyau kuma ba zai yiyu ya dauke ta a public guri kamar wannan ba, haka ya shiga da ita a gurin ya nufi gurin da suka saba zama ya zaunar da ita sannan ya koma ya dauko wayarsa da tata wayar ya dawo ya zauna, yana kallonta sai ta miko hannunta ta rika hannunta. Humairah dake gefe tana kula da wasu wata abokiyar aikinta ta tabo ta ta nuna mata shigowarsu domin kowa a gurin ya san Humaira ce kadai take kula da su idan sun zo gurin. Sai da ta gama da wandanda suke serving sannan ta nufo gurin da Ameer yake zaune tana rare wakar da ta tanadar musu. Kusan a yanzu ya haddace wakar dan haka tana fara rerawa sai ya tayata suka kare wakar a tare.
“Idan ka biye ta kan saurayi, sai ya kai ka ya baro, samarin yanzu yan shan minti ne, yar'uwa ki yi hankali 🎶 Duniya budurwar wawa yarinya ki yi hattara... 🎶 iyeee yaraye nanaye Humaira.... 🎶”
“Na haddace wannan wakar sai wace kuma?”
Ya tambaya a tsawa yana kallonta sai ta daga kafadunta tana kallonsa ita ma.
“Wakata ce kawai”
“Nice song”
“Thank You”
Ganin kamar tana kokarin raina masa da wayo ya saka ya daki teburin gabansa da karfi, har sai da ta zabura.
“Don't you ever singing that song again”
Ta hade yawu tana sauke ajiyar zuciya domin ta lura ba da wasa yake ba.
“Me za a kawo muku?”
“Ba ma bukata go back to your work”
“Lafiya? Waya taba ki?”
“Ya Maleek ya dauki bulala zai daki Waira”
Ummi ta rika hannunta taja ta suka nufi ďakinta, hakan ya bata damar rumgume Ummi ta sauraren dalilinta na kuka.
NIMRA POV.
Maleek na fita daga dakin ta ji ihun Waira da kuma Isowar Ummi taja hannunta suka bar gurin ta san, Ummi ta ajeta a gefe kenan, ba dan haka ba da yanzu ta iso da gudunta a lokacin fa Maleek yake dukanta ta tare mata dukan har ma ta yi fada da Maleek din, amman gashi bata zo ba, sai da Waira ta yi ihu, furucin da Maleek yayi mata da kuma bacin ran da ta gani a fuskar mahaifinta, ya matukar daga hankalinta ya kuma tabbatar mata da cewar ba za su taba yarda ta auri Ameer ba, ita kuma a yanzu tana jin ta shiryawa mutuwa akansa, bata taba so ba sai akan Ameer wani namiji be taba shiga zuciyarta ta juyawa yadda yake so ba sai Ameer, dabam wanda be saba ba idan ya samu ba shi ma so da sauki, iyakar gaskiyarta tana nufin mutuwa idan har aka rabata da love of her life, bata ta inda zata rayu ba idan har iyayenta suka zabi raba soyayyar da Ameer. Daker ta tashi ta tsaye ta nufi inda ta nefar da key din mota da wayarta ta dauka idonta daya a rufe saboda dukan da Maleek yayi mata ya same ta a dayar idonta ne, bakinta na a kumbure yake har lokacin yana jinin naushin da Abiey ya kai mata a baki, bata ko iya taka kafarta da kyau sai dingishi take, ko'ina na jikinta tsami yake duk inda Maleek ya same ta da bulalar ya kumbura mata jiki, yayi mata ja. Idonta har ya canja kala saboda kuka har wani jiri take gani. Sai da ta fara lekowa ta ga babu kowa a saman sannan ta sauko nufo downstairs tana tafiya dake tana sauri ta sauka, kanta babu ďankwali balle ayi maganar mayafi, haka ta sauko falon ta nufi kofa ta fita babu talkami da faduwar gaba ta fito falon ta nufi gurin motar da Ummi ta bar mata tana hawa tun bayan da Ameer ya ci uban tata motar. Ta bude ta shiga ta yi mata key kamin ta yi reverse kamar zuciyarta zata fado ta ji, masu gadi na ganin ta kunna mota sai suka fara kokarin bude mata gate, kamin ta iso har sun gama budewar ta nan ta samu sa'ar ficewa da sauri tana wani irin gudu. Fita ta yi daga unguwar amman hankalinta be kwanta ba har sai da ta ganta a bakin gate din gidan Ameer, tana faka motar bata tsaya kashewa ba ta bude ta fito ba dan tana da tabbacin Ameer yana cikin gidan ba ta nufi kofar falonsa ta tura kofar tana budewa sai ta fadi cikin falon saboda babu kuzari a jikinta kanta ma kamar zai tsage gida biyu take jinsa saboda ciwon da yake. Ameer dake rike da gorar ruwa da waya a kunne yayi saurin yanke wayar ya aje ruwan ya nufota.
“Nimra wooo what happened?”
Ta dago ta kalleshi tare da kai hannu ta taba fuskarsa.
“Ameer. Abiey, Ummi da Ya Maleek ba za su bari na aureka ba, ba za su bari mu zauna a tare ba, Ameer idan suka ba ni da kai mutuwa zan yi, ni kadai na san yadda nake ji a raina, Ameer guduwa zan yi, mu tafi wani gurin har sai iyayena sun sauka daga fushinsu, zan iya daukar komai amman ban da rabuwa da kai, ina sonka Ameer...”
Lokaci daya aka jefo masa digon tausayinta a ransa, yadda aka yi mata jina jina da jiki kuma har ta baro gidansu a irin wannan yanayin babu mayafi babu talkami hawayen da take zubar kawai sun isa su sosa masa zuciya.
“No Nimra ba zaki aikata haka ba”
“Ba zaman ban za zamu yi idan muka gudu ba Ameer aure zamu yi, mahaifina ba zai saurareni a yanzu ba, kalli yadda Ya Maleek yayi min da jiki”
Ta nuna masa jikinta, duk sai ya ji wani iri domin saboda shi komai ya faru, a kuma manufarsa ta daukar fansa ba dan yana sonta ko son aurenta da gaske ba. Ya saka hannunsa ya daga ta daga kasa ya zaunar da ita kan kujera ya rumgumeta.
“Ba zamu aikata hakan ba Nimra, ni ma da kika ga na gudu saboda Mahaifina ya kore ni da kansa ne, ke kuma mace ce hakan zai iya janyo miki matsala ba ga iyayenki kadai ba”
“Ameer ba ka ce kana kaunata ba? Zaka iya yin komai akaina?”
Yayi shiru kamar mai tunanin amsa mata, ba kansa yake ji ba, ita yake ji idan har ta aikata abun da zuciyarta ta raya mata zata jefa kanta a matsala ne kawai ne.
“Hakan ba yana nufin na sake jefaki a wata matsala a yanzu ba, Nimra I'm ever to fight for you now i can't let your family hurt you again, I'm serious this time”
“I think I'm losing my mind now, please don't let me down Ameer ina matukar kaunarka, dan Allah mu gudu idan mahaifina ya san na sake zuwa gurinka kashe ni zai yi”
Ta saki jikinsa ta mike tsaye jikinta na rawa. Sai yayi saurin mikewa shi ma ya rumgume ta.
“Shikenan zamu gudu, amman yanzu akwai wanda ya san kin zo nan?”
Ta girgiza masa kai alamar aa.
“Amman za su iya zuwa nema na a nan, Abiey zai iya kashe ni idan ya zo ya gan ni a nan”
Ya saketa ya nufi inda ya aje wayarsa ya dauka ya dauki key dinsa ya dauki wayarta ya rika hannunta ya fito da ita da sauri, a motarsa ya saka ta, sannan ya nufi motarta ya kashe ya dawo gurin motarsa ya shiga mazaunin direba ya tashi motar, ana bude masa gate ya fice da gudu, sai da yayi nisa sannan ya faka ya kwantar mata da kujerar motar yana kallon idonta dake rufe fuskarta har ta fara canja kammani. Tunanin inda za su je su boya ya fara yi kamin ya mike hannu ya rike hannunta shi dai ya san har ga Allah baya son ta a zuciyarsa sai dai kuma tausayinta ya cika masa zuciya a yanzu, domin ya fahimci ta gama haukacewa kansa.
[6/17, 10:49 PM] My S Line: 32
*W_G -it's not free, pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660*
Jin ya faka ya saka ta bude idonta daya domin ďayan ya rike ya rufe a yanzu ya like, tana kallon gurin ta dube shi.
“Me mike yi a nan?”
“Dole zamu zauna mu yi tunani inda zamu tafi mana, kuma kin ga muna bukatar kudi mai yawa da zai wadace mu a iya zaman da zamu yi, and dole mu tsara komai kamin mu tafi, kin ga babu wanda ya san muna zuwa nan balle ya saka mana ido ko a fada cewar an ganki”
Ta fashe da kuka.
“Ban tana tunanin zan iya aikata haka ba Ameer dan Allah karka ci amanata, karka bar ni dan Allah”
Ya saka hannunsa ya rike fuskarta.
“Ni na janyo miki wannan abun Nimra, so i promise you ba zan kyale ki ki sake aikata kuskure ba, kuma ba zan kyale ki sha wahala ke kadai ba”
Ya sumbanci hannunta, tun da yake a rayuwarsa be taba jin tausayin wani mutum lokaci daya kamar yadda ya ji tausayinta a yanzu ba. Yarda da ta yi da shi ya saka ta amince da kalamansa har ya bude motar ya fita ya zagaya side dinta ya bude mota ta sauko sai yayi mata side hug domin bata iya tsayuwa da kyau kuma ba zai yiyu ya dauke ta a public guri kamar wannan ba, haka ya shiga da ita a gurin ya nufi gurin da suka saba zama ya zaunar da ita sannan ya koma ya dauko wayarsa da tata wayar ya dawo ya zauna, yana kallonta sai ta miko hannunta ta rika hannunta. Humairah dake gefe tana kula da wasu wata abokiyar aikinta ta tabo ta ta nuna mata shigowarsu domin kowa a gurin ya san Humaira ce kadai take kula da su idan sun zo gurin. Sai da ta gama da wandanda suke serving sannan ta nufo gurin da Ameer yake zaune tana rare wakar da ta tanadar musu. Kusan a yanzu ya haddace wakar dan haka tana fara rerawa sai ya tayata suka kare wakar a tare.
“Idan ka biye ta kan saurayi, sai ya kai ka ya baro, samarin yanzu yan shan minti ne, yar'uwa ki yi hankali 🎶 Duniya budurwar wawa yarinya ki yi hattara... 🎶 iyeee yaraye nanaye Humaira.... 🎶”
“Na haddace wannan wakar sai wace kuma?”
Ya tambaya a tsawa yana kallonta sai ta daga kafadunta tana kallonsa ita ma.
“Wakata ce kawai”
“Nice song”
“Thank You”
Ganin kamar tana kokarin raina masa da wayo ya saka ya daki teburin gabansa da karfi, har sai da ta zabura.
“Don't you ever singing that song again”
Ta hade yawu tana sauke ajiyar zuciya domin ta lura ba da wasa yake ba.
“Me za a kawo muku?”
“Ba ma bukata go back to your work”