← Book details Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 176

Sashe 63

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gudun kar ya rikata su fita tare mahaifiyarta ta gani ranta ya bace sai ya nemi Humaira ta rika masa ita suka fito yana gaba Nimra dake dafe da Humaira tana bayansa, sai da suka iso gurin motarsa da yayi parking sannan Ummi ta bude motar da facing din ta su ta fito tana kallonsa kamanin da ta gani a fuskarsa da jikinsa sun matukar daga mata hankali zuciyarta sai rawa, ita kadai take masa kallon tausayi da kauna, Abiey da Maleek kuma suna matsa kallon tsana daga cikin motar kamin su bude su fito. Nimra na ganin iyayenta sai hankalinta ya tashi ta fashe da kuka.

“Ameer kaika kira su?”

Ya juyo ya kalleta.

“Ba zan iya bari ki aikata kuskure nan ba Nimra”

“Ba kai ka fada min zaka iya mutuwa a kaina ba?”

“Hakan baya nufin na cutar da ke a yanzu, ba ki san abun da yake kasa ba”

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un ”

Ta fada tana runtse ido. Maleek da Abiey suka iso gurin da suke tsaye Ummi kuma ta kasa karaso sao kallon Ameer take. Abiey ya kai hannu ya fisgo Nimra daga hannun Humaira ya tsinka mata mari sai da wutar kanta ta yi daukewar wucin gadi. Sannan ya kalli Ameer cikin bakar fuska ya ce.

“Babu kai babu jinina, babu kai babu zuri'ata, babu kai babu iyalina...”

Ya juya ya nufi motarsa yana jan hannun Nimra da karfi, ita kuma da yake bata da kunya sai kiran sunan Ameer take, har mutane suka fara lura da abun da ke faruwa. Allah ne kadai ya tsare Ameer be fadawa Abiey bakar magana ba, domin babu mai fada masa magana marar dadi be rama ba, sai dai tausayin Nimra da son nema mata sassauci ya saka be furta ma Abiey komai ba, sai kallon Ummi dake tsaye tana hawaye yayi daga inda yake yake fadar.

“Wata kila kin taba yin so a lokacin da kike da kurciya, ban sani ba ko kin san yadda yake da zafi da rikita zuciya, CIWON SO yana da wahala da dimauta mai yinsa, mutum kan fita hayyacinsa ya aikata abun da be dace ba, dan Allah ki dubi Nimra da idon rahma, wanda be taba so ba idan ya samu ba zai fita ďakin son da sauki ba, karki bari mijinki ya cutarta da ita dan Allah. Bata watsar da tarbiyar da kuka mata ba, duk abun da ya faru ba laifinta ba ne laifina ne...”

Each and every words da ya furtawa Ummi sai ta ji kamar magana yake jefa mata, gaba daya duniyar ta juye mata upside down. Maleek ya tabe baki yana kallon Ameer da tsarki.

“Nice one Ameer kai kake furtawa Ummi wannan maganar saboda da baka da kunya kuma baka da mutumci?”

Ameer ya matsa kusa da Maleek yana furzar masa da numfashi da karfi tare da saka hannayensa aljihu yana kallon cikin idonsa.

“Saboda bana da uwa a raye ba shi yake nufin van san darajar uwa ba, kai kuma baka san miye soyayya ba, baka san CIWON SO ba, saboda haka be kamata ka tsoma rubabben bakinka ba, baka san komai akan masoya ba dan haka karka sake karanbanin shiga a abun da ka zahilta, zan raga maka ne kawai saboda Uwa...”

Ameer ya daga hannunsa ya nuna Ummi dake tsaye, suna kallon kallo akuya kallon kura shi da Maleek. Maleek yayi kamar ya fada masa magana sai kuma wata zuciyar ta hana shi ya juya yana huci da jin ďacin maganar da Ameer ya fada masa ya nufi motarsu.

“Wayyo Allah zuciyata...”

Ummi ta fada tana kai hannu ta dafe zuciyarta, Maleek ya rikata da sauri ya saka a back seat inda Nimra take zaune ya rufe motar sannan ya bude front seat ya shiga domin Abiey ne yake tuka motar. Daga Humaira har Ameer tsaye suka yi suna kallon motar har ta fice daga gurin sannan Humaira ta cire hannayenta biyu da suke dafe a fuskarta tun a lokacin da Abiey ya mari Nimra ta ji kamar ita aka mara ta dafe kumatunta bata dauke ba sai da suka wuce. Sannan ta kalli Ameer tana hawaye ta ce.

“Baka kyauta ba, kalli yadda ka saka ƴa da uwa kuka saboda selfishness dinka, ka san yadda uwa take ji idan aka lalata tarbiyar ƴarta? Wallahi kana da hakki da yawa akanka”

Ya juya zata koma ciki, ya saka hannunsa ya rika dantsen hannunta ya fisgota ya dawo da ita daf da shi har tana iya iya jiyo numfashinsa ya kalli cikin kwayar idonta ita ma ta kalli tasa...

©Khadeeja Candy
©®Copyright
2023
[6/17, 10:49 PM] My S Line: 𝐖𝐀𝐍𝐈 𝐆𝐀𝐑𝐈

33

Sun dauki tsawon lokaci a haka ya kasa ce mata komai.

“It hurt...”

Ta fada slowly, sai ya kalli hannun nata ya sake.

“Ban yafe ba”

Ta fada da muryar da zai iya ji bayan ta wuce shi, yawu kawai ya hade ya nufi motarsa, ya bude ya shiga sai a lokacin ya kalli wayar Nimra dake hannunsa, samun kasan yayi da rashin sukunin abun da ya aikata, ya daga kujerar ta daya kwantar a dazun yana kallon gurin kamar tana nan, kamin ya kwantar da tashi kujerar ya kwanta a gurin gaba daya ya rasa ta inda zai dafa ya wanke Nimra, halin da ya jefata a yanzu ya matukar daga masa hankali, yana kwance cikin motar har la'asar sannan yaja motar ya fita daga gurin ya faka a gurin wani masallaci dake bakin hanya yayi sallah la'asar nesa da mamu.

*** *** ***

Har suka isa gida Nimra bata daina kuka ba, Abiey na faka motar ya fita ya nufi gurin masu gadi yayi musu gargadin cewar kar wanda ya kuskura ya bar Nimra ta sake fita daga gidan. Sannan ya dawo ya bude gefen da Nimra take ya fito da ita ya jefar a kasa kamar wanda be san inda ta fito ba, Ummi ta juyo da sauri ta kalleta sai dai bata da kuzarin da zata iso gurin domin zuciyarta a rike take. Abiey ya sake rika hannunta ya nufi cikin gidan da ita kamin ya isa falon Namra da Mahmood sun fito Waira ma tana bayansu, sai kowa ya kasa bawa Abiey hakuri ganin yadda fuskarsa take a hade kamar bakin hadari, tun da suke a rayuwarsu Abiey be taba saka hannu ya dakesu ba kuma ba taba yardar wani ya taba masa yara ba domin yana matukar kaunar yayansa, sai dai a yau shi da kansa yake yi ma Nimra hukunci. Sama ya hau da ita ta saka ta cikin dakinta ya janyo kofar da karfi.

“Kar wanda ya bari ta sake fita a gidan nan”

Waira na ganin zai saukowa ta yi saurin guduwa ta boya bayan kujera jikinta na rawa gani take kamar ita aka yi ma jina jina a jiki, a zatonta Abiey ne yayi ma Nimra wannan dukan daya canja mata kammanin. Tsoron kar ya hukuntata da laifin data aikata a dazun ya saka ta fashe da kuka tana rufe bakinta, dazun ma ba karamin fada yayi mata ba balle kuma yanzu da ya doki yarsa ita ma zai iya dukanta. Namra ta rika Ummi ta karasa shigowa falon ta zaunar da ita saman kujera.

“Ummi are you okay? Please kar ki saka abun da Nimra ta aikata a ranki”

Ummi ta juyo ta kalli Mahmood dake maganar tana kallonta cike da kulawa. Ta lumshe ido ta bude so take ta cika rokon da ďanta yayi mata na ganin ta bawa Nimra kariya.

“Je ka fito min da Nimra”

“Amman Ummi ba zaki hakura har zuwa anjima ba?”

Ta girgiza masa kai. Sai ya mike tsaye ya nufi upstairs ya tura kofar dakin Nimra ya shiga, kwance ya same ta a kasa tana kuka kamar ranta zai fita.

“Ta so Ummi tana kiranki ita ma kin saka ta kuka idan haka shi ne burinki, sakamakon da zaki yi mata kenan”

Nimra ta dago ta kalli Mahmood ta koma ta kwanta ita kadai ta san abun da take ji a zuciyarta, ganin ba zata tashi ba ya saka ya iso gurin ya rika hannunta yana janta da karfi domin shi ma a yanzu haushinta yake ji, sanin zata wahala ya saka ta fara rarrafe tana bin bayansa daker da sauko downstairs din, sai dai wani abu mai kama da kunya da jin nauyi ya hanata karasa inda Ummi take zaune, Maleek ya gurin dinning tsaye ya rumgume hannayensa yana harararta kamar zai cire.

“ƴa ta taso mana”

Ummi ta fada kamar ba komai tana kallon Nimra, kalaman da Ameer yayi mata a dazun ya dawo mata da tunanin rayuwarta ta baya, a yanzu tana iya fahimtar halin da Nimra take ciki. Bacin rai ya saka Maleek da Mahmood bari falon, sai Namra ce ta tashi ta riko hannun yar'uwarta tana kuka ta kawo ta gurin Ummi, Ummi ta rika kanta ta kwantar a kan cinyarta.

“Ya isa haka, wannan kuka ya isa Nimra ki kwantar da hankalinki ki saka ranki a inuwa, komai zai wuce kin ji? Karki sake kokarin guduwa ki bar ni saboda wani, kina tunanin uwa zata rayu idan babu yayanta a kusa? Ke kika da saurayi kika kasa jurewa balle ni da na haife ki? Kamin ki aikata wani abu ki rika tunawa da Umminki, kuma kin ga da acw guduwa abun kirki ne da wannan saurayin na ki be barki kin dawo ba, bude baki ki yi ta Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, ki yi sallah ki fadawa Allah damuwarki ki roki sasauci da zabi na alheri, Abiey zai sauko amman dole ne a yanzu sai yayi fushi sosai kin ji”

A hankali ta daga kai tana jin kaunar Ummi a ranta da kuma tausayin kanta.
Chapter 63 · 0% Book details