Sashe 130
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali ta fara bude idonta tana ganin dishe-dishe kamar wadda ta dade a sume, ta maida idon ta rufe ta sake budewa still the same thing, ta dago hannunta ta murda idon ta sake budewa wannan karon da dan sauki tana iya kallo da shi saidai ba kallo irin na mai gani normal ba, haka dai ta daure ta tashi zaune ta kai hannu ta dafa kanta ta shafa goshinta ya rufe idon na wasu mintuna sannan ta sake budewa tana kokarin tuna abun da ya faru sai ta kasa, ita dai abun da ta sani Ummi ta fada mata Malamimta na kiranta after ta fito ta ga malamin ya bata baya, bata sake sanin me ya faru ba, sai a yanzu da ta ganta a kasa kwance. Mikewa ta yi tsaye tana jin wani abu mai kamar jiri yana dibanta tana daga kafar daker tana takawa idonta na wanyewa a hankali har suka koma daidai, sai dai jirin be daina daukarta ba har ta tura kofar falon ta shiga. Bakin kofar falon ta tsaya tana kallon cikin falon kamar wata bakuwa sannan ta cira kafa ta taka a hankali zuwa kitchen, hannu ta mika zata dauki cup har ta riko cup din ya subuce a hannunta ya fadi kasa ya fashe, ta sake mika hannu ta janyo wani shi ma ya sake faduwa sai ta rike sink din da kyau jin tana rawa kamar zata fadi.
“Are you okay”
So take ta juyo ta kalli mai mata magana amman ta kasa. Maleek ya karasa cikin kitchen din ya tsaya daidai ita yana kallonta ba abun ya taba ta ya san haramcin yin haka sai dai yadda take ta juya ido ya nuna kamar bata cikin hayyacinta. A maimakon ya dauko wani kofin zuba mata ruwa ta sha sai ya kunna tab ya tara hannunsa ya ciko shi da ruwa ya kai mata saitin bakinta, sainta fara sha da sauri kamar wadda ta kwana bakwai bata ga ruwa ba, ya sake tara mata hannunsa ta sake sha, haka yayi mata har sau hudu sannan ta zauna a kasa gurin tana sauke numfashi jirin na sakinta kamar daman can ruwan ne maganin jiri.
“Me ya same ki?”
“Haka nan kawai nake ganin jiri”
“Okay maybe ruwan jikinki ne yayi kasa, tashi ki koma falo zan duba ki”
Ta mike tsaye tana fadin
“Lafiyata kalau maybe ina son zuwa gida ne”
Da mamaki Maleek ya kalleta.
“Gida kuma? Wane gida?”
“Garin mu inda iyalina suke, ina son na koma garinmu”
“Ssboda me? Bayan kin ce baki son zuwa kuma kina tsoron karki je su kasheki?”
“A da ne, yanzu duk wannan ya kau, bana bukatar ko'ina sai garinmu”
“Ummi ta matsa miki sai kin tafi gida ne?”
“Aa kawai dai ina son na tafi gida ne”
“Saboda muna fada da Ameer ne?”
“Aa kawai dai ina son na koma garinmu ne, lokaci yayi da ya kamata mu yi bakwana”
Fada take hawaye na sauko mata muryar na karkarwa, ita dai har a ranta ta san bata son tafiyar, sai dai tana jin ana kiranta an cire mata duk wata natsuwa da zata samu a zama garin da ba na su ba. Ji take kamar akwai wani aiki da ya kamata ta tafi ta karasa a garinsu. Maleek ya ji wani iri a kamar wanda aka cewa mutuwa zata yi ta bar shi duk inda jindadi da walwala suke a zuciyarsa sai ya neme su ya rasa.
“Kin ga zauna”
Ya kai kasa tun kamin ita din da ya bawa umarni ta zauna, damuwar bijiro da maganar tana son zuwa gida da ta yi ya saka shi manta a kitchen suke ya mike kafafuwansa ba tare da fargaba ko tsoron wani ya shigo ba. Ganin haka ya saka ita zauna a kasa tana kallon wani bangare na kitchen din zuciyarta cike da abubuwa marasa dadi.
“I know baki son tashin hankali you're too young for that, amman ba ina rigima da Ameer ba ne saboda wani abu, sai dai ina kokarin baki kariya, tsoro nake kar ya lalata rayuwarki kamar yadda ya lalata rayuwar sauran mata, ciki har da kanwata, yayi sanadiyar mutuwarta, har a bada ba zan manta ba, mutumen da tausayin da imani suka fice a zuciyarsa saboda son rai, yayi wasa da zuciya da rayuwa har sai da muka rasa ta”
Waira ta juyo ta kalleshi.
“Ba irin wannan soyayyar Ameer yake min ba, baka gane ba, shi yana sona ne kamar yadda nake son sa nake son Ya Nimra da Mahmood, yana son yayi min kirki ne”
“Aa ke ce dai baki gane ba, amman so yake miki irin wanda yake yi ma Nimra, domin ya fadawa Ummi cewa yana sonki, sai dai ke ya ce Aurenki zai yi ba kamar ita ba”
Ta girgiza kai ko bata san miye soyayya ba ta san minene aure wata igiya dake hada mutum biyu suke a karkashin inuwa daya.
“Aa ba aure ba, ni bana son aure bana son Ameer da aure”
“Why? Ko da ace ke ba zai cutar da ke ba? But ban yarda da hakan ba, na yi magana Ummi ta ga laifina, dazun ya fito yana fada mana magana son ransa saboda Namra ta yi magana Ummi ta mareta ni ma na yi magana ta mareni, tun da nake a rayuwata Ummi bata taba dukana ba tun ina karami har girma sai a yanzu, and all because of you”
Kallonsa take tana jin wani abu na rashin jindadi a sakamakon fada mata da yayi Ummi ta mare shi. Ita ma zata iya shaidar cewar Ummi bata taba maaa wani hukunci mai karfi irin wannan ba.
Ta bude baki zata bashi amsa Mahmood ya shigo kitchen, tsaye yayi yana kallonsu with full of surprise domin be taba ganin Maleek a kitchen din zaune ba ko da kuwa ace Ummi ce a ciki tana girki, amman sai gashi ya ganshi zaune kuma a kasa tare da Waira ita ma Waira tana zaune kasa.
“Abu zan dauka”
Ya fada da Murmushi a fuskarsa yana kallon Maleek. Shi ma murmushin yayi ya daga masa kafadunsa, shi dai ya san ba son Waira yake ba, dan haka ba abun kunya ko mamaki ba ne dan ganshi tare da ita a zaune, a ganinsa ba wani abun ba ne. Mahmood ya shiga cikin kitchen din ya bude fridge be dauki energy drink din ba sai da ya juyo ya kalli Maleek yayi murmushi sannan ya dauka ya rufe fridge din, haka nan ya samu kansa da tsayuwa yana shan lemun a gurin kawai yadda suke zaune ne abun yayi matukar burgeshi, tun da yake a rayuwarsa be taba ganin ďan'uwansa a haka ba, kuma ba zaka ran chanwarsa saboda Waira ba, amma kalli yadda yake a yanzu ba ya kunya ko tsoron wani ya shigo ma, ji yake kamar ya ciro wayarsa ya dauke shi hoto ya aje ko dan tarihi.
“What?”
Maleek ya tambaya ganin kamar kallon da Mahmood yake masa yayi yawa har ya soma tsarguwa.
“Ya aka yi?”
“Murmushi na ga kana yi?”
Mahmood ya yi dariya yana kora drinks dinsa.
“Toh kuka zan yi? Abun farinciki ne ai, wish you all the best”
Maleek yayi saurin mikewa tsaye.
“No no noooo ba abun da kake tunani ba ne, kai baka da zuciya mai kyau sai tunanin abun da be dace ba? Akwai abun da nake son sani daga gareta that's why ta gan ni a nan”
“Okay Maa Shaa Allah”
Ya fada tare da daga hannunsa kana ya sa kai ya fice daga kitchen din still yana murmushi. Maleek ma samun kansa yayi da yin murmushi ya kalli Waira dake musu kallon rashin fahimta domin bata fahimci zaren yaren da suke ba.
“Tashi ki tafi falo ko daki ki kwanta”
“Bana jin bachi?”
“Me yasa kike tangadi a dazun?”
“Ban sani ba, jiri nake ji, zaka iya rika ni na tafi dakina”
“No”
Ya amsa mata kai tsaye. Sai ta sauke idonta kasa da muryar da ta san ba zai ji ba ta furta.
“I thought you change”
Hakan kuma be hana shi ji ba.
“I change Waira, ni san na canja kawai ba zan rika ki ba ne saboda addinin musulunci ya hana taba macen da ma muharramankar ba”
Ta dago tana kallonshi a wani yanayi mai kamar fushi kamar shagwaba.
“Amman Ameer yana yi”
“Ameer is different from me, shi yana aikata abubuwa da musulunci ya hana, be damu da zunubin ba, ni kuma tsorona zunubin ne”
Hannu ta kai ta rika sink din ta mike tsaye ta fara tafiya har ta fice daga kitchen din.
Around 9pm babu kowa a dinning sai ita kadai plate din shimkafa da wake da Ummi ta saka aka girka yana gabanta sai kuma empty plate da take zuba waken da ta cire a cikin shimkafa domin bata jindadinsu a hade saboda bata saba ci ba, kara ma shimkafa ta san da ita tun a garinsu domin ana nomata kasancewar suna da ruwa suna sarrafata su ci, sai dai ita bata taba gwada ci ba, ta fi sha'awar yayan itatuwa. Hanne kuma na zaune a falon saman carpet tare da bakuwarta sun kurawa plasma dake kunne ido suna kallon drama da gabatarwa. Door bell din yayi kara Hanne ta zabura ta nufi kofar ta bude ganin Ameer ya saka ta matsa ta bashi hanya tana gaishe shi, ya amsa mata fuska sake domin ya shigo gidan da labari mai dadi da zai gabatarwa Waira. Tun da aka danna door bell din Waira take ta dago tana kallon kofar har Ameer ya shigo bata dauke idonta ba har ya karaso inda take zaune, abun ka da masoyi sai ya ji ba zai iya zama a kujerar dake nesa da ita ba, dan haka ya ja kujerar dake kusa ya zauna yana mata murmushi, sai ta samu kanta da kasa mayar masa da murmushin kuma ta kasa dauke idonta daga barin kallonsa.
“Hey Beauty”
Ya kai hannu ya shafa fuskarsa sai ta lumshe ido ta bude ta kawar da fuskar.
“Ya kike?”
Ya tambaya yana damuwa da tashin ganin murmushin da ya saba gani a fuskarta a duk lokacin da ya zo gurinta.
“Lafiya kalau”
“Are you okay”
So take ta juyo ta kalli mai mata magana amman ta kasa. Maleek ya karasa cikin kitchen din ya tsaya daidai ita yana kallonta ba abun ya taba ta ya san haramcin yin haka sai dai yadda take ta juya ido ya nuna kamar bata cikin hayyacinta. A maimakon ya dauko wani kofin zuba mata ruwa ta sha sai ya kunna tab ya tara hannunsa ya ciko shi da ruwa ya kai mata saitin bakinta, sainta fara sha da sauri kamar wadda ta kwana bakwai bata ga ruwa ba, ya sake tara mata hannunsa ta sake sha, haka yayi mata har sau hudu sannan ta zauna a kasa gurin tana sauke numfashi jirin na sakinta kamar daman can ruwan ne maganin jiri.
“Me ya same ki?”
“Haka nan kawai nake ganin jiri”
“Okay maybe ruwan jikinki ne yayi kasa, tashi ki koma falo zan duba ki”
Ta mike tsaye tana fadin
“Lafiyata kalau maybe ina son zuwa gida ne”
Da mamaki Maleek ya kalleta.
“Gida kuma? Wane gida?”
“Garin mu inda iyalina suke, ina son na koma garinmu”
“Ssboda me? Bayan kin ce baki son zuwa kuma kina tsoron karki je su kasheki?”
“A da ne, yanzu duk wannan ya kau, bana bukatar ko'ina sai garinmu”
“Ummi ta matsa miki sai kin tafi gida ne?”
“Aa kawai dai ina son na tafi gida ne”
“Saboda muna fada da Ameer ne?”
“Aa kawai dai ina son na koma garinmu ne, lokaci yayi da ya kamata mu yi bakwana”
Fada take hawaye na sauko mata muryar na karkarwa, ita dai har a ranta ta san bata son tafiyar, sai dai tana jin ana kiranta an cire mata duk wata natsuwa da zata samu a zama garin da ba na su ba. Ji take kamar akwai wani aiki da ya kamata ta tafi ta karasa a garinsu. Maleek ya ji wani iri a kamar wanda aka cewa mutuwa zata yi ta bar shi duk inda jindadi da walwala suke a zuciyarsa sai ya neme su ya rasa.
“Kin ga zauna”
Ya kai kasa tun kamin ita din da ya bawa umarni ta zauna, damuwar bijiro da maganar tana son zuwa gida da ta yi ya saka shi manta a kitchen suke ya mike kafafuwansa ba tare da fargaba ko tsoron wani ya shigo ba. Ganin haka ya saka ita zauna a kasa tana kallon wani bangare na kitchen din zuciyarta cike da abubuwa marasa dadi.
“I know baki son tashin hankali you're too young for that, amman ba ina rigima da Ameer ba ne saboda wani abu, sai dai ina kokarin baki kariya, tsoro nake kar ya lalata rayuwarki kamar yadda ya lalata rayuwar sauran mata, ciki har da kanwata, yayi sanadiyar mutuwarta, har a bada ba zan manta ba, mutumen da tausayin da imani suka fice a zuciyarsa saboda son rai, yayi wasa da zuciya da rayuwa har sai da muka rasa ta”
Waira ta juyo ta kalleshi.
“Ba irin wannan soyayyar Ameer yake min ba, baka gane ba, shi yana sona ne kamar yadda nake son sa nake son Ya Nimra da Mahmood, yana son yayi min kirki ne”
“Aa ke ce dai baki gane ba, amman so yake miki irin wanda yake yi ma Nimra, domin ya fadawa Ummi cewa yana sonki, sai dai ke ya ce Aurenki zai yi ba kamar ita ba”
Ta girgiza kai ko bata san miye soyayya ba ta san minene aure wata igiya dake hada mutum biyu suke a karkashin inuwa daya.
“Aa ba aure ba, ni bana son aure bana son Ameer da aure”
“Why? Ko da ace ke ba zai cutar da ke ba? But ban yarda da hakan ba, na yi magana Ummi ta ga laifina, dazun ya fito yana fada mana magana son ransa saboda Namra ta yi magana Ummi ta mareta ni ma na yi magana ta mareni, tun da nake a rayuwata Ummi bata taba dukana ba tun ina karami har girma sai a yanzu, and all because of you”
Kallonsa take tana jin wani abu na rashin jindadi a sakamakon fada mata da yayi Ummi ta mare shi. Ita ma zata iya shaidar cewar Ummi bata taba maaa wani hukunci mai karfi irin wannan ba.
Ta bude baki zata bashi amsa Mahmood ya shigo kitchen, tsaye yayi yana kallonsu with full of surprise domin be taba ganin Maleek a kitchen din zaune ba ko da kuwa ace Ummi ce a ciki tana girki, amman sai gashi ya ganshi zaune kuma a kasa tare da Waira ita ma Waira tana zaune kasa.
“Abu zan dauka”
Ya fada da Murmushi a fuskarsa yana kallon Maleek. Shi ma murmushin yayi ya daga masa kafadunsa, shi dai ya san ba son Waira yake ba, dan haka ba abun kunya ko mamaki ba ne dan ganshi tare da ita a zaune, a ganinsa ba wani abun ba ne. Mahmood ya shiga cikin kitchen din ya bude fridge be dauki energy drink din ba sai da ya juyo ya kalli Maleek yayi murmushi sannan ya dauka ya rufe fridge din, haka nan ya samu kansa da tsayuwa yana shan lemun a gurin kawai yadda suke zaune ne abun yayi matukar burgeshi, tun da yake a rayuwarsa be taba ganin ďan'uwansa a haka ba, kuma ba zaka ran chanwarsa saboda Waira ba, amma kalli yadda yake a yanzu ba ya kunya ko tsoron wani ya shigo ma, ji yake kamar ya ciro wayarsa ya dauke shi hoto ya aje ko dan tarihi.
“What?”
Maleek ya tambaya ganin kamar kallon da Mahmood yake masa yayi yawa har ya soma tsarguwa.
“Ya aka yi?”
“Murmushi na ga kana yi?”
Mahmood ya yi dariya yana kora drinks dinsa.
“Toh kuka zan yi? Abun farinciki ne ai, wish you all the best”
Maleek yayi saurin mikewa tsaye.
“No no noooo ba abun da kake tunani ba ne, kai baka da zuciya mai kyau sai tunanin abun da be dace ba? Akwai abun da nake son sani daga gareta that's why ta gan ni a nan”
“Okay Maa Shaa Allah”
Ya fada tare da daga hannunsa kana ya sa kai ya fice daga kitchen din still yana murmushi. Maleek ma samun kansa yayi da yin murmushi ya kalli Waira dake musu kallon rashin fahimta domin bata fahimci zaren yaren da suke ba.
“Tashi ki tafi falo ko daki ki kwanta”
“Bana jin bachi?”
“Me yasa kike tangadi a dazun?”
“Ban sani ba, jiri nake ji, zaka iya rika ni na tafi dakina”
“No”
Ya amsa mata kai tsaye. Sai ta sauke idonta kasa da muryar da ta san ba zai ji ba ta furta.
“I thought you change”
Hakan kuma be hana shi ji ba.
“I change Waira, ni san na canja kawai ba zan rika ki ba ne saboda addinin musulunci ya hana taba macen da ma muharramankar ba”
Ta dago tana kallonshi a wani yanayi mai kamar fushi kamar shagwaba.
“Amman Ameer yana yi”
“Ameer is different from me, shi yana aikata abubuwa da musulunci ya hana, be damu da zunubin ba, ni kuma tsorona zunubin ne”
Hannu ta kai ta rika sink din ta mike tsaye ta fara tafiya har ta fice daga kitchen din.
Around 9pm babu kowa a dinning sai ita kadai plate din shimkafa da wake da Ummi ta saka aka girka yana gabanta sai kuma empty plate da take zuba waken da ta cire a cikin shimkafa domin bata jindadinsu a hade saboda bata saba ci ba, kara ma shimkafa ta san da ita tun a garinsu domin ana nomata kasancewar suna da ruwa suna sarrafata su ci, sai dai ita bata taba gwada ci ba, ta fi sha'awar yayan itatuwa. Hanne kuma na zaune a falon saman carpet tare da bakuwarta sun kurawa plasma dake kunne ido suna kallon drama da gabatarwa. Door bell din yayi kara Hanne ta zabura ta nufi kofar ta bude ganin Ameer ya saka ta matsa ta bashi hanya tana gaishe shi, ya amsa mata fuska sake domin ya shigo gidan da labari mai dadi da zai gabatarwa Waira. Tun da aka danna door bell din Waira take ta dago tana kallon kofar har Ameer ya shigo bata dauke idonta ba har ya karaso inda take zaune, abun ka da masoyi sai ya ji ba zai iya zama a kujerar dake nesa da ita ba, dan haka ya ja kujerar dake kusa ya zauna yana mata murmushi, sai ta samu kanta da kasa mayar masa da murmushin kuma ta kasa dauke idonta daga barin kallonsa.
“Hey Beauty”
Ya kai hannu ya shafa fuskarsa sai ta lumshe ido ta bude ta kawar da fuskar.
“Ya kike?”
Ya tambaya yana damuwa da tashin ganin murmushin da ya saba gani a fuskarta a duk lokacin da ya zo gurinta.
“Lafiya kalau”