Sashe 89
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Amman taya Ummi zata haifi da ace bata bashi kulawa ba kuma be girma a tare da mu ba, ko sau daya bata taba fada mana labarinsa ba? Kuma shi Ameer mutanen da yake kallon a matsayin iyayensa ya alakarsu take da su kenan? Taya ma duk haka ta faru idan ma da gaske ne? Kuma shi Ameer ya san da haka ko kuma yaya? Kuma ďan ma na waye? Na mahaifinmu ne ko na wani”
“Nima ina son na sani sosai, sai dai bana son mu zurfafa tunani kar mu tunanin abun da be kamata ba, mu jira kawai mu ji ta bakinta zai fi, for now dai dole zata fada mana tun da gaskiyar ta bayyana”
Maleek ya gyada kai mamakin ya cika kansa har ya rasa ta ina zai fara tunani, abun sam be kama kanshi ba.
“If ma da gaske ne miyasa Ummi bata fada ba lokacin da muka samu matsala da shi? Karka manta fa har fada ta rika yi saboda ba a kama wanda yayi min aika aikar ba”
Maleek ya fada yana ciro wayar dake aljihunsa ya duba kiran Namra, he pick up the call ya kara a kunnensa kukan da ya ji tana rerawa har ya hana maganarta fita shi ya fara daga masa hankali.
“Namra are you alright?”
“Ciw...ciwo... Ciwon... Nimra ya tashi and.... She... Couldn't survive.... ”
“What do you mean?”
Ya tambaya da karfi. Sai ta amsa masa da ihu tana fashe da wani kalar kuka mai karfin gaske
“We lost her...”
“Innalillahi
Innalillahi
Innalillahi.... Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Haka ya rika furtawa sai a karshen ya samu hada kalmomin gaban dayansu, ya mike tsaye rike da wayar try to control himself.
“Lafiya?”
Mahmood ya tambaya shi ma yana mikewa tsaye ganin hankalin ďan'uwansa a tashe.
“Nimra ce we lost her...”
Maleek ya fada hawaye na zubo masa. Mahmood ya duke da sauri a gurin yana buga hannayensa a teburin dake gabansu har sai da hankalin mutane ya dawo kansu. Maleek ya yi following call din Namra amman bata daga ba ya sake kira bata daga ba sai ya nufi Waiters ya biya kudin ruwan da aka kawo musu ya fice da gudu, ya saka key din motarsa kusa da sau uku sannan ya shiga daidai ya shiga motar ya murza key da irin sifar da be taba tashin mota a haka ba. Kamar ya sato motar haka yake tukin yana ratsa motoci har ya iso gida, be tsaya danna horn asan da zuwansa har a bude masa gate ba a wajem gate din ya bar motar ya fito da gudu ya bar motar a kunne ya tura karamar kofar gate din da karfi, jin ta a rufe ya buga mai gadin ya bude masa, kamar an korasho haka ya shigo cikin gidan da gudu su kansu ma'aikatan gidan sai da suka tsorata, ta gudu ya shiga falon kitchen ya fara nufa ya leka sai ya tararda Hanne a ciki da Yesmin suna hira suna aiki, ya fito da gudu ya haura stairs din kamar zai zame, ta tura kofar dakin Ummi da sauri ya shiga.
“Ina wayarki Ummi ara min zan kira wani?”
Ummi ta juyo ta kalleshi hawaye na kwaranya a idonta.
“Mun rasa Nimra ko ba haka ba?”
Tsaye yayi cak ya rasa me zai ce mata eh haka ne, ko kuma aa ba haka ba ne? Tausayinta ya zame masa biyu. Daker ya cira kafarsa ya isa gurin da take tsaye ya rumgume mahaifiyarsa abun da be sani ba shi ma hawayen yake kamar ita, sai dai shi yana kokarin ya fita karfin hali ne saboda ta samu kwarin guiwa kar ita ma su rasa ta daman ba lafiya ce ya wadece ba.
“Ki yi hakuri Ummi mutuwa bata da magani”
Sai ta dago kamar jira take ta bashi amsa tana hakki tana kuka
“Haka ne Maleek, mutuwa bata da magani, na rasa mijina na farko a lokacin da nake da kurciya, na rasa mahaifina tun kamin girmana na rasa mahaifiyata a lokacin da girma ya fara kamani, yanzu kuma na rasa yata, bana fatar na sake rasa kowa kuma.. Bana fatar na sake ganin gawar kowa”
Ya saka hannayensa ya rike fuska yana kuka naman fuskarsa na rawa.
“Mu kuma ba ma fatar ganin gawarki Ummi, ba ku fata kar Allah ya nuna mana wannan ranar”
Ya maida ita kirjinsa ya rumgume ita kuka shi kuka aka rasa mai rarrashin wani....
“Ummi...”
Muryar Waira ta saka suka juyo gaba dayansu suka kalleta tana tsaye bakin kofa kanta ba dankwali kamar kullum sai kallonsa take idonta a waje daman can sarki tsoro ce balle ta ga suna kuka. Maleek ya saki Ummi ya saka gefen rigarsa ya share hawayensa ya nufo kofar da Waira take tsaye da niyar ficewa sai suka jiyo karar Yesmin dake kitchen hakan yayi daidai da tsayawar motar Jabir, Umar daki daki ma ya fito da gudu domin Namra ta rike kowa kira take tana fada masa yar'uwarta ta mutu har da wadanda be kamata ta kira ba. Kan kace kwabo gidan ya karade da kuka kana ji kasan an rasa rayuwa mai tsada, Waira ta gudu a inda ta saba boya ta boye tana kuka sosai kamar ranta zai fita, domin tana matukar son Nimra, Ummi da Nimra su ne mutane da ta fi kauna bayan Shuraim da Eid..
Wani tashin hankali be bayyana ba sai da aka iso da gawarta a falon Ummi, gata kwance cikin karaga an daure babban dan yatsan kafarta da dan'uwansa, an daure hannunta ba ta motsi an lullube da babban zane. Kowa kuka yake a gidan domin ba su taba dandana zafin rasa rai ba sai a yau, ba ma kamar Namra dake ta kara tana fisge-fisge ji take kamar ace tana da ikon bada kyautar rai da sai ta bawa yar'uwarta.
“Ni kam na yi bakar tafiya, tun da na iso gidan nan bakaken abubuwa kawai suke faruwa, da nasani ban zo ba”
Shi ne abun da Dr Zainab ta fada tana kuka. Maleek ya kalleta yana istijara.
“A'uzubillahi minal shaidanin rajin, Mommy ki daina fadar haka be dace ba, mu fa musulmai ne ko kuka da kuka duk be dace na ba a son ana tsare gawa ana mata kuka”
“Allahu Akbar, yau yata ta canja suna daga Nimra zuwa gawa kaico mai rai”
Ummi ta fada tana kara fashewa da kuka sosai. Maleek da Jabir da Umar ne suka rika gawar aka maida ita a wani empty daki dake kasa saboda idan an haura da ita stairs zai zama aiki, idan kuma aka barta a falon za su tsareta da kuka ne duk da kasancewar falon babba ne mai kamar wata karamar fada. Tun da aka shigo da gawar Nimra a gidan Abiey be fito daga dakinsa ba, kuma ba kuka yake ba sai dai yayi shiru wani abu ya tsaya masa a kahon zuciya... Hoton gawarta da ya gani a asibitin bayan Namra ta kira shi ta fada masa ya rasa yarsa ya doshi asibitin ya ganta a lokacin da aka fito da ita daga dakin da aka shiga da ita domin bata taimakon gaggawa, sai dai ina mai ajiya ya karbi abarsa, mai kira yayi kira babu tsaya, tarin kwararin likotoci ko kayan aikin basa hana mutuwa ko karin wa'adi.
The death of Nimra hit every one of them, domin ba su saka mata ran mutuwa, even though likitan yace za su iya rasa ta, kuma numfashinta ya gagara sauka normal kamar yadda yake. Sai just like yadda mafi yawa mutane suna daukar bugun zuciya kamar baya saurin kisa, but ana haduwa da ajali kuma kowa da silar mutuwarsa. Waya kan waya aka rika kiran Abiey tun daga familynsa na bangaren Ammy har zuwa na Mai Martaba, da na Yesmin amman ya kasa amsa kiran kowa sai na amininsa Sauban. A lokacin da Abiey ya amsa wayar, Sauban ya fara shimfida masa kalaman hakuri da juriya da kuma yadda da kaddara, Sauban ya tunatar da shi abubuwa da dama daga rayuwarsu da baya yayi masa kalamai na kwantar da hankali da saukar da natsuwa. Duk da haka idon Abiey ko kwalla be yi ba balle hawaye. Bayan ya tabbatar masa da gobe zai yi sammakon biyo jirgin safe daga Dubai to Nigeria sannan suka yi sallama. Abiey ya aje wayar ya mike tsaye ya taka yana jin kafarsa kamar ba tashi ba gaba daya jikinsa ma ya sauya as well as zuciyarsa. Ya fito daga bangaren yana jin yadda yanayin gidan ya canja gaba daya saboda rashin yarsa, Nimra ce ta biyu da yafi kauna a cikin yayansa bayan Maleek, domin ita ba kamar Namra take ba da girman kai ko ji da kai, she's very friendly tana zama ta yi hira da shi kamar yadda Maleek ya dauke shi aboki ko ma fiye da haka. Ta kofar baya ya shigo bangaren Ummi ya daga kai yana kallon yan'uwa da suke kusa na garin Abuja da suka cika falon duk kuwa da kasancewar dare ne. Dr Zainab ta fi kowa fahimtar ďan'uwanta tana ganinsa ta san abun da ya kawo shi sai ta fada masa inda gawar yarsa take. Ya taka da kafarsa ya murda kofar dakin ya shiga, sai yayi arba da ita tana kwance a cikin karaga slowly ya karasa kusa da gawar ya sunkuya ya saka hannu ya yaye zanen da aka rufa mata, fuskarta ta bayyana gata kwance kamar ta yi magana amman ba dama, hannu ya saka ya shafa fuskarta yana tuna maganarsa ta karshe da ita a asibiti, ya risina ya sumbance ta sai a lokacin hawaye suka cika idonsa har suka diga a jikin gawar. Yana kokarin mikewa tsaye sai ga Maleek ya shigo da sauri daman baya falon a lokacin da Abiey ya shigo da ba zai bar shi ba.
“Abiey haba me zaka yi a nan kuma?”
Abiey ya juyo ya kalleshi hawaye na masa zuba idonsa yayi ja sosai kamar wan watsa masa yaji a ciki.
“I'm here to tell na yafe mata duk wani hakki nawa da yake kanta kuma na nema mata gafara”
“Ganinta a haka zai haifar maka da damuwa, damuwarka kai da Ummi matsala ce a garemu”
“Nima ina son na sani sosai, sai dai bana son mu zurfafa tunani kar mu tunanin abun da be kamata ba, mu jira kawai mu ji ta bakinta zai fi, for now dai dole zata fada mana tun da gaskiyar ta bayyana”
Maleek ya gyada kai mamakin ya cika kansa har ya rasa ta ina zai fara tunani, abun sam be kama kanshi ba.
“If ma da gaske ne miyasa Ummi bata fada ba lokacin da muka samu matsala da shi? Karka manta fa har fada ta rika yi saboda ba a kama wanda yayi min aika aikar ba”
Maleek ya fada yana ciro wayar dake aljihunsa ya duba kiran Namra, he pick up the call ya kara a kunnensa kukan da ya ji tana rerawa har ya hana maganarta fita shi ya fara daga masa hankali.
“Namra are you alright?”
“Ciw...ciwo... Ciwon... Nimra ya tashi and.... She... Couldn't survive.... ”
“What do you mean?”
Ya tambaya da karfi. Sai ta amsa masa da ihu tana fashe da wani kalar kuka mai karfin gaske
“We lost her...”
“Innalillahi
Innalillahi
Innalillahi.... Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Haka ya rika furtawa sai a karshen ya samu hada kalmomin gaban dayansu, ya mike tsaye rike da wayar try to control himself.
“Lafiya?”
Mahmood ya tambaya shi ma yana mikewa tsaye ganin hankalin ďan'uwansa a tashe.
“Nimra ce we lost her...”
Maleek ya fada hawaye na zubo masa. Mahmood ya duke da sauri a gurin yana buga hannayensa a teburin dake gabansu har sai da hankalin mutane ya dawo kansu. Maleek ya yi following call din Namra amman bata daga ba ya sake kira bata daga ba sai ya nufi Waiters ya biya kudin ruwan da aka kawo musu ya fice da gudu, ya saka key din motarsa kusa da sau uku sannan ya shiga daidai ya shiga motar ya murza key da irin sifar da be taba tashin mota a haka ba. Kamar ya sato motar haka yake tukin yana ratsa motoci har ya iso gida, be tsaya danna horn asan da zuwansa har a bude masa gate ba a wajem gate din ya bar motar ya fito da gudu ya bar motar a kunne ya tura karamar kofar gate din da karfi, jin ta a rufe ya buga mai gadin ya bude masa, kamar an korasho haka ya shigo cikin gidan da gudu su kansu ma'aikatan gidan sai da suka tsorata, ta gudu ya shiga falon kitchen ya fara nufa ya leka sai ya tararda Hanne a ciki da Yesmin suna hira suna aiki, ya fito da gudu ya haura stairs din kamar zai zame, ta tura kofar dakin Ummi da sauri ya shiga.
“Ina wayarki Ummi ara min zan kira wani?”
Ummi ta juyo ta kalleshi hawaye na kwaranya a idonta.
“Mun rasa Nimra ko ba haka ba?”
Tsaye yayi cak ya rasa me zai ce mata eh haka ne, ko kuma aa ba haka ba ne? Tausayinta ya zame masa biyu. Daker ya cira kafarsa ya isa gurin da take tsaye ya rumgume mahaifiyarsa abun da be sani ba shi ma hawayen yake kamar ita, sai dai shi yana kokarin ya fita karfin hali ne saboda ta samu kwarin guiwa kar ita ma su rasa ta daman ba lafiya ce ya wadece ba.
“Ki yi hakuri Ummi mutuwa bata da magani”
Sai ta dago kamar jira take ta bashi amsa tana hakki tana kuka
“Haka ne Maleek, mutuwa bata da magani, na rasa mijina na farko a lokacin da nake da kurciya, na rasa mahaifina tun kamin girmana na rasa mahaifiyata a lokacin da girma ya fara kamani, yanzu kuma na rasa yata, bana fatar na sake rasa kowa kuma.. Bana fatar na sake ganin gawar kowa”
Ya saka hannayensa ya rike fuska yana kuka naman fuskarsa na rawa.
“Mu kuma ba ma fatar ganin gawarki Ummi, ba ku fata kar Allah ya nuna mana wannan ranar”
Ya maida ita kirjinsa ya rumgume ita kuka shi kuka aka rasa mai rarrashin wani....
“Ummi...”
Muryar Waira ta saka suka juyo gaba dayansu suka kalleta tana tsaye bakin kofa kanta ba dankwali kamar kullum sai kallonsa take idonta a waje daman can sarki tsoro ce balle ta ga suna kuka. Maleek ya saki Ummi ya saka gefen rigarsa ya share hawayensa ya nufo kofar da Waira take tsaye da niyar ficewa sai suka jiyo karar Yesmin dake kitchen hakan yayi daidai da tsayawar motar Jabir, Umar daki daki ma ya fito da gudu domin Namra ta rike kowa kira take tana fada masa yar'uwarta ta mutu har da wadanda be kamata ta kira ba. Kan kace kwabo gidan ya karade da kuka kana ji kasan an rasa rayuwa mai tsada, Waira ta gudu a inda ta saba boya ta boye tana kuka sosai kamar ranta zai fita, domin tana matukar son Nimra, Ummi da Nimra su ne mutane da ta fi kauna bayan Shuraim da Eid..
Wani tashin hankali be bayyana ba sai da aka iso da gawarta a falon Ummi, gata kwance cikin karaga an daure babban dan yatsan kafarta da dan'uwansa, an daure hannunta ba ta motsi an lullube da babban zane. Kowa kuka yake a gidan domin ba su taba dandana zafin rasa rai ba sai a yau, ba ma kamar Namra dake ta kara tana fisge-fisge ji take kamar ace tana da ikon bada kyautar rai da sai ta bawa yar'uwarta.
“Ni kam na yi bakar tafiya, tun da na iso gidan nan bakaken abubuwa kawai suke faruwa, da nasani ban zo ba”
Shi ne abun da Dr Zainab ta fada tana kuka. Maleek ya kalleta yana istijara.
“A'uzubillahi minal shaidanin rajin, Mommy ki daina fadar haka be dace ba, mu fa musulmai ne ko kuka da kuka duk be dace na ba a son ana tsare gawa ana mata kuka”
“Allahu Akbar, yau yata ta canja suna daga Nimra zuwa gawa kaico mai rai”
Ummi ta fada tana kara fashewa da kuka sosai. Maleek da Jabir da Umar ne suka rika gawar aka maida ita a wani empty daki dake kasa saboda idan an haura da ita stairs zai zama aiki, idan kuma aka barta a falon za su tsareta da kuka ne duk da kasancewar falon babba ne mai kamar wata karamar fada. Tun da aka shigo da gawar Nimra a gidan Abiey be fito daga dakinsa ba, kuma ba kuka yake ba sai dai yayi shiru wani abu ya tsaya masa a kahon zuciya... Hoton gawarta da ya gani a asibitin bayan Namra ta kira shi ta fada masa ya rasa yarsa ya doshi asibitin ya ganta a lokacin da aka fito da ita daga dakin da aka shiga da ita domin bata taimakon gaggawa, sai dai ina mai ajiya ya karbi abarsa, mai kira yayi kira babu tsaya, tarin kwararin likotoci ko kayan aikin basa hana mutuwa ko karin wa'adi.
The death of Nimra hit every one of them, domin ba su saka mata ran mutuwa, even though likitan yace za su iya rasa ta, kuma numfashinta ya gagara sauka normal kamar yadda yake. Sai just like yadda mafi yawa mutane suna daukar bugun zuciya kamar baya saurin kisa, but ana haduwa da ajali kuma kowa da silar mutuwarsa. Waya kan waya aka rika kiran Abiey tun daga familynsa na bangaren Ammy har zuwa na Mai Martaba, da na Yesmin amman ya kasa amsa kiran kowa sai na amininsa Sauban. A lokacin da Abiey ya amsa wayar, Sauban ya fara shimfida masa kalaman hakuri da juriya da kuma yadda da kaddara, Sauban ya tunatar da shi abubuwa da dama daga rayuwarsu da baya yayi masa kalamai na kwantar da hankali da saukar da natsuwa. Duk da haka idon Abiey ko kwalla be yi ba balle hawaye. Bayan ya tabbatar masa da gobe zai yi sammakon biyo jirgin safe daga Dubai to Nigeria sannan suka yi sallama. Abiey ya aje wayar ya mike tsaye ya taka yana jin kafarsa kamar ba tashi ba gaba daya jikinsa ma ya sauya as well as zuciyarsa. Ya fito daga bangaren yana jin yadda yanayin gidan ya canja gaba daya saboda rashin yarsa, Nimra ce ta biyu da yafi kauna a cikin yayansa bayan Maleek, domin ita ba kamar Namra take ba da girman kai ko ji da kai, she's very friendly tana zama ta yi hira da shi kamar yadda Maleek ya dauke shi aboki ko ma fiye da haka. Ta kofar baya ya shigo bangaren Ummi ya daga kai yana kallon yan'uwa da suke kusa na garin Abuja da suka cika falon duk kuwa da kasancewar dare ne. Dr Zainab ta fi kowa fahimtar ďan'uwanta tana ganinsa ta san abun da ya kawo shi sai ta fada masa inda gawar yarsa take. Ya taka da kafarsa ya murda kofar dakin ya shiga, sai yayi arba da ita tana kwance a cikin karaga slowly ya karasa kusa da gawar ya sunkuya ya saka hannu ya yaye zanen da aka rufa mata, fuskarta ta bayyana gata kwance kamar ta yi magana amman ba dama, hannu ya saka ya shafa fuskarta yana tuna maganarsa ta karshe da ita a asibiti, ya risina ya sumbance ta sai a lokacin hawaye suka cika idonsa har suka diga a jikin gawar. Yana kokarin mikewa tsaye sai ga Maleek ya shigo da sauri daman baya falon a lokacin da Abiey ya shigo da ba zai bar shi ba.
“Abiey haba me zaka yi a nan kuma?”
Abiey ya juyo ya kalleshi hawaye na masa zuba idonsa yayi ja sosai kamar wan watsa masa yaji a ciki.
“I'm here to tell na yafe mata duk wani hakki nawa da yake kanta kuma na nema mata gafara”
“Ganinta a haka zai haifar maka da damuwa, damuwarka kai da Ummi matsala ce a garemu”