Sashe 94
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Sai dai idan zai yiyu ki yi hakuri ganin Ameer ba zai samu a yanzu ba, ba dan ina nufi gina wani abu a tsakaninku ba, domin kin min komai kin rufa min asiri a lokacin da makiya za su min dariya, gaskiya kika fada bayyanar cewar Ameer ba ďana ba ne a yanzu babu wanda zai ji sai idan mun so ya sani, amman a wacan lokacin da hakan ya faru da na sha kunya da kunci matuka, kin min kyautar ďa sukutun da ya hana ni kewar rashin haihuwa, ko a haka kadai kin cancanci na yi miki komai a yanzu, kin aikata abun da kika aikata saboda ki ceto rayuwar mijinka na farko, sai dai hakan ya gagara saboda rai baya tsayawa dan wata rai, kuma kin hakura kika danne abun da kike ji ranki saboda farincikin mijin da kike aure a yanzu, maddallah da ke Zahra hakika ke mata ce ta gari”
Ummi ta sauke ajiyar zuciya tana sanyi a ranta na saurin fahimtarta da Mr Bashir yayi domin ba ta yi tsammanin zata same shi haka cikin ruwan sanyi ba.
“Na gode, amman me yasa ba zaka bar ni na ga Ameer ba?”
“Saboda ni mahaifinsa be, duk wani abu da zai jefa Ameer a damuwa bana sonsa, kwanansa biyu babu lafiya, abincin kirki baya iya ci, ko aiki baya fita kuma ina tunanin duk saboda faruwar wannan abun ne ya haifar masa da damuwa, yau ne muka samu ya dan sake har ya fita harabar gida yana dan hutawa, ina tsoron kar ganinki ya dawo masa da damuwa ko ya haifar masa da wata matsalar domin har yanzu be gama fahimtar rayuwar da kika bijiro masa da ita ba”
Ummi ta yi shiru, bata son takurawa domin ita ma din kamar shi take bata son damuwar Ameer idan har ganinta zai haifar masa da damuwa yo zata iya hakura.
“Daman dai na zo na duba lafiyarsa ne, ssboda zuciyata ta kwadaitu da son ganinsa, tun da na ji lafiyarsa Alhamdulillah wannan ma kadai abun farinciki ne a gurina”
Ta mike tsaye ta dauki jakarta.
“Ka taimaka min gurin shawo kan yaron nan dan Allah, ya yafe min abun da na yi masa”
“Ba zamu iya cilasta shi ba, amman a hannu zai fahimta mu bashi lokaci”
Ta amsa masa kai sannan ta ce.
“Na barka lafiya”
Binta yayi da kallo har ta fice sannan ya girgiza kai ya sauke ajiyar zuciya.
AMEER POV.
Tun a safiyar da ya raka gawar Nimra makabarta ya dawo gida zazzabi ya rufe shi, be sake lafiya ba sai yau shi ma kuma ba wadatarsa ta yi ba, ya dai samu kuzari ba kamar kwana biyu da yake wuni da zama a daki ba, har sai da Daddy ya kira Family Doctor su ya duba shi ya rubuta magani aka siyo masa ya sha, abinci sai Mommy ta matsa masa ya ke dan ci, ko kuma Daddy ya saka a kira shi bangarensa su ci abincin a tare duk yadda Daddy yake jans ada hirar duniya saboda ya sake ya kasa yin haka, idan kuma ya dauko masa zancen Ummi sai kawai ya tashi ya fice ya bar Daddy. Sai dai ya tashi jikinsa da dan sauki bama kamar da yamma nan da ya sha energy drink. Kewar Nimra da tunanin rayuwarsa da yayi ta baya kamin komai ya lalace ya saka shi fitowa yana ta yawo a compound din gidan, kamin daga karshe ya tare a garden da yar sarewarsa yana busar dake deba masa kewa da kadaici. Vest ce a jikinsa sai Jean baki da talkamin da suka fi kama da silifas. A tsaye yake yana busar a tsakanin ruwa swimming pool da kujerun da aka ware na kwanciya a huta. Be sararba ya ji an rumgume shi a baya ana kuka. Cak ya tsaya da busar yana sauraren yadda zuciyarsa ke bugawa da mugun karfi, bugawar da be taba jin irinta ba, bugawar da ta wuce kima, har take neman danne numfashinsa. Da sauri ya juyo sai yayi arba da kyakkyawar fuskar da zuciyarsa ke raya masa be ga wata macen da ta fita kyau ba on earth, hawaye ke mata zuba jikinta rawa yake bakinta na motsi kamar ta yi masa magana kuma ta kasa furta komai, kanta a sama tana kallonsa domin yayi mata tsawo sosai kamar yadda Maleek yake mata kasancewar ba wata mai tsayi sosai ba sai dai kuma ba zaka kirata gajera ba.
A yanzu kam baya bukatar tuna inda ya santa ko ya ganta, ya fahimci wacece ita tun a karon farko da yayi arba da ita a gidan Ummi, sai dai siffarta gaba daya ta canja sam ba zaka ganta a yanzu ka ganta a can baya kuma ka ce mutum daya ne ba, sai dai kamanin da suka zo daya.
“Me kike so?”
Ya tambaya sai ta rumgume shi ta fashe da wani kukan, rayuwarta ta baya ta tuna mata, rumgumar da ta yi masa ta farko ta rumgume shi ne ba dan tasan waye ba, a yanzu ta gane Ameer ne hakan ya bata gwarin guiwar sake rumgumeshi domin a gurinta ba laifi ba ne, kasa motsi yayi har sai da ta gaji da kukan ta dago kanta.
“A ina ka iya wannan busar? Waya koya maka?”
Wannan ne karo na biyu ta ji yayi busar bayan busar da yayi a cikin dajin lokacin da take boye. Yawo yake da idonsa a fuskarta kamar mai kirga abu.
“Ya aka yi kike magana? Waya kawo ki nan?”
“Ka fara amsa min ni”
“Wani ne ya koya min”
“Wani wa?”
“Baki san shi ba, waya kawo ki nan?”
Amsa mata yake yana tambayarta idonsa akan kyakkyawar fuskarta mai daukar hankali ko kyabtawa ba yayi, wani irin kallonta yake kamar zai cinye ta, irin kallon nan dake tafiyar da hankalin mai yinsa ya mantar da shi a inda yake da duk wata damuwa da yake ciki.
“Ya aka yi kika zama haka? Ya aka yi kike iya magana yanzu?”
Ya kama hannunta yana dubawa, ko tabo babu balle alamar cizon maciji.
“I have so many questions for you Girl, you change alot, kamar dai bake ce yarinyar nan ba”
“Ni ma ina da tambayoyi da yawa”
Ta amsa tana fisge hannunta daga riko da yayi mata.
Ya dafa kansa ya daga sama.
“Oh my God”
Gani yake kamar ba ita ba ce, a lokacin da ta yi masa magana a gidan Ummi hankalinsa ba akanta yake ba dan haka be yi realize duk wani abu da ta fada ba, shi dai ya san ta rumgume a sa'ilin da kasa rabata da jikinsa kuma ya kasa ce mata komai har sai da Yesmin ta fisgeta a jikinsa.
“Ya Maleek ya kawo ni”
Ya dawo da kansa kasa ya kalleta.
“Fada min waya koya maka wannan busar?”
“Me yasa kike son ki sani?”
“Saboda mutum daya yake wannan busar, wani be isa ya ko yi yadda ake yi ba, kai ya aka yi kake yi? Ina Eid?”
“Eid..? How do you know him?”
Ya tambaya yana karin hancinta. Kamin ta amsa masa ya nufi hanyar fita Garden din tunawa da yayi ta fada masa Maleek ya kawo ta, me Maleek zai kawo ta yi me yasa ya kawo ta? Ta fada musu tana da alaka da shi ne.
“Ina Maleek din yake?”
“Yana can waje”
Ta nuna gate tana biyo bayansa, da sauri ya nufi gate din ya bude ya fita. Maleek na tsaye yana kallon wasu gidajen, zuciyarsa cike da haushin Ameer, saboda Ummi kawai ya tsaya nan ba dan ita ba da babu abun da zai tsayar da shi a kofar gidan.
“What now? Me ka zo yi?”
Ameer ya fada yana daga bayansa tsaye, Maleek na jin haka ya saka hannayensa aljihu ya cigaba da kallon da yake, sai yayi kamar be san da mutum bayansa ba.
“Are you here to celebrate?”
Maleek ya bawa banza ajiyarsa, domin ya san idan har ya juyo yayi masa magana to ba zai fada masa mai dadi ba, shi a yanzu baya ma son ganin Ameer din da idonsa.
“All those years kana min kallon wani kalar mutum na dabam right? Saboda kansan gaskiya, boye gaskiyar me ya haifar? Da ace na san gaskiya da ban yi soyayyar karya da kanwarka ba”
Sai a lokacin Maleek ya juyo.
“Matsala ta da kai kenan, kai ba shaye shaye ba, sai surutai kala kala, ka san mun rasa Nimra kenan? Amman kake tsaye a nan kana fada min magana marar kan gado? Saboda ka zama ďan Ummi sai na yi celebration?”
Maleek ya kara takowa ya isa daf da Ameer.
“No na ji ba dadi ne saboda Ummi bata cancanci ďa kamar kai ba, arrogant, wanda be iya komai ba sai son kai da wulakanta mutane, Ameer har duniya ta nade ba zan manta cewar kai ka yi silar mutuwar Nimra ba, kuma ka gode Allah Ummi tana tare da kai, ka ci albarkacinta saboda ka zama daga tsatsonta, if not Wallahi da sai na saka nadamar da sai ka yi nadamar haihuwarka da aka yi”
Ameer yayi murmushi.
“Kai kasan waye ni Maleek ba yi wani wanda zai saka ni nadamar ba, sai dai idan na ga lokacin nadamar yayi na yi dan kaina, ka ce Ummi bata cancanci ďa kamar ni ba, sai kuma ga shi ta hada jini da ni? Ya aka yi?”
Fitowar Ummi ce ta saka duk suka kalleta, tana ganin yadda suka yi kirko kiro ta san ba lafiya ba, sai dai ganin Ameer da ta yi ya kawar mata da damuwar sanin dalilinsu na tsayuwa har suna fuskantar juna kamar abokan gaba.
“Ameer ďa na, i just come to check on you”
Ta kai hannu ta taba shi sai ya kauce ya matsa baya, ya dauke fuska.
“This should be the last time da zaki zo duba ni, ba ki ba ni kulawa a lokacin da nake bukatarta karki ce zaki yi kokari yi a yanzu”
Maleek ya watsa masa wata uwar harara yana jin kamar ya shaki wuyansa. Sai dai shi mutum ne dake kokarin danne abun a zuciyarsa dan haka ya budewa Ummi mota.
“Ummi shiga muje”
Ummi ta sauke ajiyar zuciya tana sanyi a ranta na saurin fahimtarta da Mr Bashir yayi domin ba ta yi tsammanin zata same shi haka cikin ruwan sanyi ba.
“Na gode, amman me yasa ba zaka bar ni na ga Ameer ba?”
“Saboda ni mahaifinsa be, duk wani abu da zai jefa Ameer a damuwa bana sonsa, kwanansa biyu babu lafiya, abincin kirki baya iya ci, ko aiki baya fita kuma ina tunanin duk saboda faruwar wannan abun ne ya haifar masa da damuwa, yau ne muka samu ya dan sake har ya fita harabar gida yana dan hutawa, ina tsoron kar ganinki ya dawo masa da damuwa ko ya haifar masa da wata matsalar domin har yanzu be gama fahimtar rayuwar da kika bijiro masa da ita ba”
Ummi ta yi shiru, bata son takurawa domin ita ma din kamar shi take bata son damuwar Ameer idan har ganinta zai haifar masa da damuwa yo zata iya hakura.
“Daman dai na zo na duba lafiyarsa ne, ssboda zuciyata ta kwadaitu da son ganinsa, tun da na ji lafiyarsa Alhamdulillah wannan ma kadai abun farinciki ne a gurina”
Ta mike tsaye ta dauki jakarta.
“Ka taimaka min gurin shawo kan yaron nan dan Allah, ya yafe min abun da na yi masa”
“Ba zamu iya cilasta shi ba, amman a hannu zai fahimta mu bashi lokaci”
Ta amsa masa kai sannan ta ce.
“Na barka lafiya”
Binta yayi da kallo har ta fice sannan ya girgiza kai ya sauke ajiyar zuciya.
AMEER POV.
Tun a safiyar da ya raka gawar Nimra makabarta ya dawo gida zazzabi ya rufe shi, be sake lafiya ba sai yau shi ma kuma ba wadatarsa ta yi ba, ya dai samu kuzari ba kamar kwana biyu da yake wuni da zama a daki ba, har sai da Daddy ya kira Family Doctor su ya duba shi ya rubuta magani aka siyo masa ya sha, abinci sai Mommy ta matsa masa ya ke dan ci, ko kuma Daddy ya saka a kira shi bangarensa su ci abincin a tare duk yadda Daddy yake jans ada hirar duniya saboda ya sake ya kasa yin haka, idan kuma ya dauko masa zancen Ummi sai kawai ya tashi ya fice ya bar Daddy. Sai dai ya tashi jikinsa da dan sauki bama kamar da yamma nan da ya sha energy drink. Kewar Nimra da tunanin rayuwarsa da yayi ta baya kamin komai ya lalace ya saka shi fitowa yana ta yawo a compound din gidan, kamin daga karshe ya tare a garden da yar sarewarsa yana busar dake deba masa kewa da kadaici. Vest ce a jikinsa sai Jean baki da talkamin da suka fi kama da silifas. A tsaye yake yana busar a tsakanin ruwa swimming pool da kujerun da aka ware na kwanciya a huta. Be sararba ya ji an rumgume shi a baya ana kuka. Cak ya tsaya da busar yana sauraren yadda zuciyarsa ke bugawa da mugun karfi, bugawar da be taba jin irinta ba, bugawar da ta wuce kima, har take neman danne numfashinsa. Da sauri ya juyo sai yayi arba da kyakkyawar fuskar da zuciyarsa ke raya masa be ga wata macen da ta fita kyau ba on earth, hawaye ke mata zuba jikinta rawa yake bakinta na motsi kamar ta yi masa magana kuma ta kasa furta komai, kanta a sama tana kallonsa domin yayi mata tsawo sosai kamar yadda Maleek yake mata kasancewar ba wata mai tsayi sosai ba sai dai kuma ba zaka kirata gajera ba.
A yanzu kam baya bukatar tuna inda ya santa ko ya ganta, ya fahimci wacece ita tun a karon farko da yayi arba da ita a gidan Ummi, sai dai siffarta gaba daya ta canja sam ba zaka ganta a yanzu ka ganta a can baya kuma ka ce mutum daya ne ba, sai dai kamanin da suka zo daya.
“Me kike so?”
Ya tambaya sai ta rumgume shi ta fashe da wani kukan, rayuwarta ta baya ta tuna mata, rumgumar da ta yi masa ta farko ta rumgume shi ne ba dan tasan waye ba, a yanzu ta gane Ameer ne hakan ya bata gwarin guiwar sake rumgumeshi domin a gurinta ba laifi ba ne, kasa motsi yayi har sai da ta gaji da kukan ta dago kanta.
“A ina ka iya wannan busar? Waya koya maka?”
Wannan ne karo na biyu ta ji yayi busar bayan busar da yayi a cikin dajin lokacin da take boye. Yawo yake da idonsa a fuskarta kamar mai kirga abu.
“Ya aka yi kike magana? Waya kawo ki nan?”
“Ka fara amsa min ni”
“Wani ne ya koya min”
“Wani wa?”
“Baki san shi ba, waya kawo ki nan?”
Amsa mata yake yana tambayarta idonsa akan kyakkyawar fuskarta mai daukar hankali ko kyabtawa ba yayi, wani irin kallonta yake kamar zai cinye ta, irin kallon nan dake tafiyar da hankalin mai yinsa ya mantar da shi a inda yake da duk wata damuwa da yake ciki.
“Ya aka yi kika zama haka? Ya aka yi kike iya magana yanzu?”
Ya kama hannunta yana dubawa, ko tabo babu balle alamar cizon maciji.
“I have so many questions for you Girl, you change alot, kamar dai bake ce yarinyar nan ba”
“Ni ma ina da tambayoyi da yawa”
Ta amsa tana fisge hannunta daga riko da yayi mata.
Ya dafa kansa ya daga sama.
“Oh my God”
Gani yake kamar ba ita ba ce, a lokacin da ta yi masa magana a gidan Ummi hankalinsa ba akanta yake ba dan haka be yi realize duk wani abu da ta fada ba, shi dai ya san ta rumgume a sa'ilin da kasa rabata da jikinsa kuma ya kasa ce mata komai har sai da Yesmin ta fisgeta a jikinsa.
“Ya Maleek ya kawo ni”
Ya dawo da kansa kasa ya kalleta.
“Fada min waya koya maka wannan busar?”
“Me yasa kike son ki sani?”
“Saboda mutum daya yake wannan busar, wani be isa ya ko yi yadda ake yi ba, kai ya aka yi kake yi? Ina Eid?”
“Eid..? How do you know him?”
Ya tambaya yana karin hancinta. Kamin ta amsa masa ya nufi hanyar fita Garden din tunawa da yayi ta fada masa Maleek ya kawo ta, me Maleek zai kawo ta yi me yasa ya kawo ta? Ta fada musu tana da alaka da shi ne.
“Ina Maleek din yake?”
“Yana can waje”
Ta nuna gate tana biyo bayansa, da sauri ya nufi gate din ya bude ya fita. Maleek na tsaye yana kallon wasu gidajen, zuciyarsa cike da haushin Ameer, saboda Ummi kawai ya tsaya nan ba dan ita ba da babu abun da zai tsayar da shi a kofar gidan.
“What now? Me ka zo yi?”
Ameer ya fada yana daga bayansa tsaye, Maleek na jin haka ya saka hannayensa aljihu ya cigaba da kallon da yake, sai yayi kamar be san da mutum bayansa ba.
“Are you here to celebrate?”
Maleek ya bawa banza ajiyarsa, domin ya san idan har ya juyo yayi masa magana to ba zai fada masa mai dadi ba, shi a yanzu baya ma son ganin Ameer din da idonsa.
“All those years kana min kallon wani kalar mutum na dabam right? Saboda kansan gaskiya, boye gaskiyar me ya haifar? Da ace na san gaskiya da ban yi soyayyar karya da kanwarka ba”
Sai a lokacin Maleek ya juyo.
“Matsala ta da kai kenan, kai ba shaye shaye ba, sai surutai kala kala, ka san mun rasa Nimra kenan? Amman kake tsaye a nan kana fada min magana marar kan gado? Saboda ka zama ďan Ummi sai na yi celebration?”
Maleek ya kara takowa ya isa daf da Ameer.
“No na ji ba dadi ne saboda Ummi bata cancanci ďa kamar kai ba, arrogant, wanda be iya komai ba sai son kai da wulakanta mutane, Ameer har duniya ta nade ba zan manta cewar kai ka yi silar mutuwar Nimra ba, kuma ka gode Allah Ummi tana tare da kai, ka ci albarkacinta saboda ka zama daga tsatsonta, if not Wallahi da sai na saka nadamar da sai ka yi nadamar haihuwarka da aka yi”
Ameer yayi murmushi.
“Kai kasan waye ni Maleek ba yi wani wanda zai saka ni nadamar ba, sai dai idan na ga lokacin nadamar yayi na yi dan kaina, ka ce Ummi bata cancanci ďa kamar ni ba, sai kuma ga shi ta hada jini da ni? Ya aka yi?”
Fitowar Ummi ce ta saka duk suka kalleta, tana ganin yadda suka yi kirko kiro ta san ba lafiya ba, sai dai ganin Ameer da ta yi ya kawar mata da damuwar sanin dalilinsu na tsayuwa har suna fuskantar juna kamar abokan gaba.
“Ameer ďa na, i just come to check on you”
Ta kai hannu ta taba shi sai ya kauce ya matsa baya, ya dauke fuska.
“This should be the last time da zaki zo duba ni, ba ki ba ni kulawa a lokacin da nake bukatarta karki ce zaki yi kokari yi a yanzu”
Maleek ya watsa masa wata uwar harara yana jin kamar ya shaki wuyansa. Sai dai shi mutum ne dake kokarin danne abun a zuciyarsa dan haka ya budewa Ummi mota.
“Ummi shiga muje”