Sashe 124
Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta mike tsaye tana nade carpet din.
“Kullum zan dinga yin Sallah”
“Hakan yana da kyau, amman ba za a amsa miki ba har sai kin musulumta”
“Me kenan?”
“Kin bar addininki kin shiga na mu”
Ta yi shiru for some minutes sannan ta zauna a kan kujera tana fadin.
“Zan yi tunani”
“Kina da wannan yancin, babu mai miki dole”
Maleek ya amsa mata da murmushi sannan ta kalli stairs ya kalleta.
“Dare yayi ki shiga ki kwanta so that ki tashi da wuri, gobe akwai school”
Ya rausayar da kai shagwabe ta ce.
“Ummi nake jira ta zo ta hada min tea sai na sha zan kwanta”
“Ba ta ce ki rika hadawa da kanki ba?”
Ta bata fuska tana zuba shagwaba ta ce.
“Da dai ayi min”
Ya tabe baki kadan ya mike tsaye.
“Let me help”
Ya nufi kitchen din ya shiga ya hada mata tea ta dauko mata cake ya dawo falon tana zaune saman kujera ya mika mata.
“Karki ci cake din da yawa saboda zaki kwanta karya saka ki ciwon ciki”
Ta karba.
“Thank you”
Ta sauko kasa ta zauna ta fara ci, a kokarinsa na hana idonsa abun da suke son kallo ya ciro wayarsa ya shiga dannawa. Waira sai kallonsa take tana tuna furucinsa na dazun da ya fada nata cewar tana burge shi, kuma gashi a yanzu ya hada mata tea, ba wannan karon farko da ya taba hada mata tea ba amman this one is special ita kanta tana jin haka, ko dan hado mata da cake da yayi kuma ya kawo mata har inda take zaune, kana ya fada mata kar ta ci da yawa saboda kar cikinta yayi ciwo.
“Ya Maleek”
Ta kira sunansa a hankali tana cin cake din, sai ya amsa mata ba tare da ya kalleta ba.
“Huhmm mmn”
“Me yasa yau kake min kirki?”
Ya kalleta sai yayi murmushi.
“I already told you saboda na ganki kina sallah ne”
“Haka ma Ameer ya ce he can't wait ya gan ni ina Sallah”
Ba tare da tunanin komai ba ta fadi haka tana dariya, sai ta ga murmushi dake fuskarsa ya gushe fuskarsa ta zama kamar wanda be taba murmushi ba. Ganin hakan ya saka ta mike tsaye sai kuma hakan yayi daidai da shigowar Ummi a bangaren tana tafiya kamar wanda bata son zuwa. Waira ta mikawa Maleek cup din tea din.
“Gashi thank you”
Ya kalleta kamar yace ki aje a kasa mana ko ki kai kitchen sai kuma ya ji ba zai iya fada mata ko daya ba, ya samu kansa da mika hannu ya karba ya sunkuya ya aje juyowar da zai yi ya kalli inda Waira take kallo sai ga Ummi ta iso gurin tana kallonsa Waira kuma na fada mata, Maleek ya hada mata tea kuma ta yi sallah, halin da Ummi take ciki ya saka bata maida hankali akan abun da Waira take fada mata ba.
“Yayi kyau, shiga ciki ki kwanta dare yayi”
“Okay good night”
Ummi ta kai hannu ta shafa kanta ta tsayar da hannunta daidai fuskarta tana shafawa fuskarta dauke da murmushi mai wuyar fasssara. Maleek ma mamakin yadda Ummi take kallon Waira yake, at first yayi zaton ko saboda ta yi sallah ne, sai dai jin bata yi magana ba ya saka shi kawar da wannan tunanin ga kuma idanuwan mahaifiyarsa da ya gani da alamar kuka, damuwa ma ta kasa boyuwa a fuskarsa.
“Good night sweetheart, sleep tight”
Waira ta dan yi murmushi sannan ta kalli Maleek ta ce.
“Good Night Ya Maleek”
“Good night”
Ya amsa mata sannan ta nufi stairs rike da dankwalin Ummi da carpet da kuma carjin da ta dauko bata ja ba. Maleek ya bita da kallo har ta haye sama, Ummi kuma ta ke ta kallon Maleek tana karantar abun da Abiey ya fada mata a fuskarsa ta ce.
“Ban taba tsayawa na lura da abun da ya kamata ace na gani ba, shiyasa zuciyata bata tana ayyana min kana son Waira ba....”
Dum-dum-dum yaji wani irin bugawar zuciya da karfi, kamar wanda aka jefowa aradu haka ya ji saukar maganar a kunnensa, ya juyo da fuskarsa daga barin kallon Stairs ya kalli Ummi dake kallonsa with emotional, shi dai ya san be fadawa Abiey yana son Waira ba, kuma be shi ba sonta yake ba to how comes Ummi ta fahimci abun a baibai? Abiey ya fadi haka ne saboda ya toshe duk wata hanya da Ameer zai bi ko kuma shi ma ya masa tsabanin fahimta ne? Sai dai abun da ya kasa yi shi ne karyata cewar baya sonta, ba dan saboda kar ya karyata Abiey dinsa ba, kawai sai dan baya da kuzarin karyata haka ko da kuwa Abiey ne a gabansa a tsaye yake shimfida masa fahimtarsa. Bashi da wannan kwarin guiwar na karyata cewa baya son Waira, kuma ba dan yana sonta din ba, kawai dai yana ganin kamar idan yayi haka ya rage mata kima da daraja.
“ Tsawon rayuwata wannan ranar nake jira, ranar da zaka gabatar min da wata mace a matsayin wadda kake so, ko kuma ni na gabatar maka ka karba, ba tare da ka musa min ba, sai dai abun ya zo min da inda ban zata ba, a wani yanayi da ban yi tsammani ba, ba zan ga laifinka ba, haka ma Ameer ba shi da laifina ne da ban maida hankali na kula da abun da idonka yake a kai ba”
Sai a lokacin Maleek ya samu baki magana domin a dazu jin yayi kamar Ummi ta daure shi da tsarkoki.
“Ba komai ne laifinki ba Ummi, ki daina dorawa kanki laifi babu abun da kika yi a nan”
“Da ace na zama Jarumar uwa kamar sauran iyaye mata, da na dade da lura da haka, da komai ya zo da sauki”
Maleek ya matsa daf da ita sai ta kwanto saman jikinta.
“Mahaifinka ya fada min abun da kake ta boyewa, ban yi zaton abun zai zo da wuri haka ba, kullum addu'a da buri na ga ranar da zaka canja, i wish i could...”
Sai kuka ya ci karfinta. Wani abu ya ji na rashin dadi, irin wanda ki wane dan kwarai yake ji idan uwarsa tana kuka. Sai yayi unkurin fada mata shi ba son Waira yake ba sai kuma ya ji ya kasa, wata kila farinciki take da hakan din ma da Abiey ya fada mata, sai dai shi ya san baya son kowa a ransa. Dan haka ya rumgume yana jin wani sanyi irin na wadda uwarsa take raye da kuma kaunarta a zuciyarsa da tausayinsa. A yanzu ya tabbatar hi miss alot na rashin samun damar rabar jikin mahaifiyarsa da sanin danuwarta tun da dadewa.
“Dare yayi Ummi ya kamata ki samu wutawa”
Ta dago daga jikinsa ta kalleshi sannan ta sauke kai ta nufi hanyar stairs jiki babu kwari. Da kallo ya bita har ta haye sannan ya zauna yana tunanin maganar, a sirance ya yi murmushi ya shafa kansa, be san me yasa abun yake saka shi nishadi ba, saboda Abiey yayi amfani da shi ne ko kuma saboda za a hanawa Ameer ita ne? Abun dai is just funny to him kuma be san dalili ya mike yana murmushin da ya kusan komawa dariya ransa fes kamar an masa albishir da wani abun farinciki. Wayarsa ya ciro ya rika ta da hannu biyu ya shiga message dinsa ya turawa Abiey sako.
“Abiey ban ce ina son yarinyar nan ba fa, me yasa ka fadawa Ummi haka zata yi zaton saboda Ameer ya ce yana sonta ne”
Silly Emoji Abiey yayi masa reply da shi ba tare da yace komai ba, a nan ma Maleek murmushi yayi ya nufi kofar fita daga falon, harabar gidan ya fito gurin motoci ya tsaya yana ta kallon taurarin dake samaniya, yana jin kamar bashi da damuwa ko daya. Can kuma ya sauke kai yana tuna sallah da ya tarar Waira na yi a dazun abu ne mai kyau domin haka na nuna sha'awarta ga addinin musulumci ne. Wayarsa dake hannunsa ya taba ya shiga sashen hotuna ya kama hotonta da ya dauke ta tana bachi yayi ta kallo kamar ba gobe.
A daren Ummi kasa bachi ta yi saboda tunanin da ya zame mata biyu ta rasa ina zata bullo, wane zata dauka wanne zata aje. Sai kusan asuba ta samu runtsawa asuba na yi kuma ta farka ta yi sallah ta fito dakinta kamin ta kawo kasa ta hango mijinta dake kokarin hauro stairs din.
“Na san baki yi bachi ba yau, zaki takura kanki da tunani ne kawai na raya haka saboda ba zo kin kwanta a bangarena ba”
Kamin ta karaso inda yake har hawaye ya cika idonta.
“Ba ni da sauran karfi a yanzu Abiey, dukansu yayana ne, ban san wa zan goyawa baya ba, a zan iya zaba a tsakaninsu ba, kuma na san hakan zai haifar da matsala da karin rashin fahimta ne a tsakaninsu, a maimakon a samu mafita sai abun ya kara lalacewa”
“Ina ganin kamata yayi ki fito fili ki fadawa Ameer gaskiya nima zan sanar da Maleek”
“Ba lallai ne ya fahimta ba, Ameer yana da wuyar sha'ani, yar alakar dake tsakaninmu zata yi tsami, da ma ace zan iya tankura Maleek wata kila shi zai iya hakura, domin Ameer yana son Waira sosai fiye da tunaninka, yadda kike ganin kamar cutar da ita zai yi ba zai yi haka ba, na ga kaunarta idonsa”
“Amman kuma kika kasa ganin hakan a idon Maleek karki zama selfish mana Zahra, ni ma ina son farinciki ďana fiye da yadda kike son Ameer, ina bin komai a hankalin ne saboda Matsalar da kike ciki... Dan haka ina ganin abun da ya dace kawai a fitar da yarinyar nan waje ta yi karatu kamin mu ga abun da Allah zai yi”
Ummi bata da karfin cewa komai a yanzu, ta san Abiey ba zai fahimce ta, haka ma Ameer ba fahimtar da zai yi ba.
“Allah ya zaba mana abun da ya fi zama alheri, bari na shiga kitchen”
“Kullum zan dinga yin Sallah”
“Hakan yana da kyau, amman ba za a amsa miki ba har sai kin musulumta”
“Me kenan?”
“Kin bar addininki kin shiga na mu”
Ta yi shiru for some minutes sannan ta zauna a kan kujera tana fadin.
“Zan yi tunani”
“Kina da wannan yancin, babu mai miki dole”
Maleek ya amsa mata da murmushi sannan ta kalli stairs ya kalleta.
“Dare yayi ki shiga ki kwanta so that ki tashi da wuri, gobe akwai school”
Ya rausayar da kai shagwabe ta ce.
“Ummi nake jira ta zo ta hada min tea sai na sha zan kwanta”
“Ba ta ce ki rika hadawa da kanki ba?”
Ta bata fuska tana zuba shagwaba ta ce.
“Da dai ayi min”
Ya tabe baki kadan ya mike tsaye.
“Let me help”
Ya nufi kitchen din ya shiga ya hada mata tea ta dauko mata cake ya dawo falon tana zaune saman kujera ya mika mata.
“Karki ci cake din da yawa saboda zaki kwanta karya saka ki ciwon ciki”
Ta karba.
“Thank you”
Ta sauko kasa ta zauna ta fara ci, a kokarinsa na hana idonsa abun da suke son kallo ya ciro wayarsa ya shiga dannawa. Waira sai kallonsa take tana tuna furucinsa na dazun da ya fada nata cewar tana burge shi, kuma gashi a yanzu ya hada mata tea, ba wannan karon farko da ya taba hada mata tea ba amman this one is special ita kanta tana jin haka, ko dan hado mata da cake da yayi kuma ya kawo mata har inda take zaune, kana ya fada mata kar ta ci da yawa saboda kar cikinta yayi ciwo.
“Ya Maleek”
Ta kira sunansa a hankali tana cin cake din, sai ya amsa mata ba tare da ya kalleta ba.
“Huhmm mmn”
“Me yasa yau kake min kirki?”
Ya kalleta sai yayi murmushi.
“I already told you saboda na ganki kina sallah ne”
“Haka ma Ameer ya ce he can't wait ya gan ni ina Sallah”
Ba tare da tunanin komai ba ta fadi haka tana dariya, sai ta ga murmushi dake fuskarsa ya gushe fuskarsa ta zama kamar wanda be taba murmushi ba. Ganin hakan ya saka ta mike tsaye sai kuma hakan yayi daidai da shigowar Ummi a bangaren tana tafiya kamar wanda bata son zuwa. Waira ta mikawa Maleek cup din tea din.
“Gashi thank you”
Ya kalleta kamar yace ki aje a kasa mana ko ki kai kitchen sai kuma ya ji ba zai iya fada mata ko daya ba, ya samu kansa da mika hannu ya karba ya sunkuya ya aje juyowar da zai yi ya kalli inda Waira take kallo sai ga Ummi ta iso gurin tana kallonsa Waira kuma na fada mata, Maleek ya hada mata tea kuma ta yi sallah, halin da Ummi take ciki ya saka bata maida hankali akan abun da Waira take fada mata ba.
“Yayi kyau, shiga ciki ki kwanta dare yayi”
“Okay good night”
Ummi ta kai hannu ta shafa kanta ta tsayar da hannunta daidai fuskarta tana shafawa fuskarta dauke da murmushi mai wuyar fasssara. Maleek ma mamakin yadda Ummi take kallon Waira yake, at first yayi zaton ko saboda ta yi sallah ne, sai dai jin bata yi magana ba ya saka shi kawar da wannan tunanin ga kuma idanuwan mahaifiyarsa da ya gani da alamar kuka, damuwa ma ta kasa boyuwa a fuskarsa.
“Good night sweetheart, sleep tight”
Waira ta dan yi murmushi sannan ta kalli Maleek ta ce.
“Good Night Ya Maleek”
“Good night”
Ya amsa mata sannan ta nufi stairs rike da dankwalin Ummi da carpet da kuma carjin da ta dauko bata ja ba. Maleek ya bita da kallo har ta haye sama, Ummi kuma ta ke ta kallon Maleek tana karantar abun da Abiey ya fada mata a fuskarsa ta ce.
“Ban taba tsayawa na lura da abun da ya kamata ace na gani ba, shiyasa zuciyata bata tana ayyana min kana son Waira ba....”
Dum-dum-dum yaji wani irin bugawar zuciya da karfi, kamar wanda aka jefowa aradu haka ya ji saukar maganar a kunnensa, ya juyo da fuskarsa daga barin kallon Stairs ya kalli Ummi dake kallonsa with emotional, shi dai ya san be fadawa Abiey yana son Waira ba, kuma be shi ba sonta yake ba to how comes Ummi ta fahimci abun a baibai? Abiey ya fadi haka ne saboda ya toshe duk wata hanya da Ameer zai bi ko kuma shi ma ya masa tsabanin fahimta ne? Sai dai abun da ya kasa yi shi ne karyata cewar baya sonta, ba dan saboda kar ya karyata Abiey dinsa ba, kawai sai dan baya da kuzarin karyata haka ko da kuwa Abiey ne a gabansa a tsaye yake shimfida masa fahimtarsa. Bashi da wannan kwarin guiwar na karyata cewa baya son Waira, kuma ba dan yana sonta din ba, kawai dai yana ganin kamar idan yayi haka ya rage mata kima da daraja.
“ Tsawon rayuwata wannan ranar nake jira, ranar da zaka gabatar min da wata mace a matsayin wadda kake so, ko kuma ni na gabatar maka ka karba, ba tare da ka musa min ba, sai dai abun ya zo min da inda ban zata ba, a wani yanayi da ban yi tsammani ba, ba zan ga laifinka ba, haka ma Ameer ba shi da laifina ne da ban maida hankali na kula da abun da idonka yake a kai ba”
Sai a lokacin Maleek ya samu baki magana domin a dazu jin yayi kamar Ummi ta daure shi da tsarkoki.
“Ba komai ne laifinki ba Ummi, ki daina dorawa kanki laifi babu abun da kika yi a nan”
“Da ace na zama Jarumar uwa kamar sauran iyaye mata, da na dade da lura da haka, da komai ya zo da sauki”
Maleek ya matsa daf da ita sai ta kwanto saman jikinta.
“Mahaifinka ya fada min abun da kake ta boyewa, ban yi zaton abun zai zo da wuri haka ba, kullum addu'a da buri na ga ranar da zaka canja, i wish i could...”
Sai kuka ya ci karfinta. Wani abu ya ji na rashin dadi, irin wanda ki wane dan kwarai yake ji idan uwarsa tana kuka. Sai yayi unkurin fada mata shi ba son Waira yake ba sai kuma ya ji ya kasa, wata kila farinciki take da hakan din ma da Abiey ya fada mata, sai dai shi ya san baya son kowa a ransa. Dan haka ya rumgume yana jin wani sanyi irin na wadda uwarsa take raye da kuma kaunarta a zuciyarsa da tausayinsa. A yanzu ya tabbatar hi miss alot na rashin samun damar rabar jikin mahaifiyarsa da sanin danuwarta tun da dadewa.
“Dare yayi Ummi ya kamata ki samu wutawa”
Ta dago daga jikinsa ta kalleshi sannan ta sauke kai ta nufi hanyar stairs jiki babu kwari. Da kallo ya bita har ta haye sannan ya zauna yana tunanin maganar, a sirance ya yi murmushi ya shafa kansa, be san me yasa abun yake saka shi nishadi ba, saboda Abiey yayi amfani da shi ne ko kuma saboda za a hanawa Ameer ita ne? Abun dai is just funny to him kuma be san dalili ya mike yana murmushin da ya kusan komawa dariya ransa fes kamar an masa albishir da wani abun farinciki. Wayarsa ya ciro ya rika ta da hannu biyu ya shiga message dinsa ya turawa Abiey sako.
“Abiey ban ce ina son yarinyar nan ba fa, me yasa ka fadawa Ummi haka zata yi zaton saboda Ameer ya ce yana sonta ne”
Silly Emoji Abiey yayi masa reply da shi ba tare da yace komai ba, a nan ma Maleek murmushi yayi ya nufi kofar fita daga falon, harabar gidan ya fito gurin motoci ya tsaya yana ta kallon taurarin dake samaniya, yana jin kamar bashi da damuwa ko daya. Can kuma ya sauke kai yana tuna sallah da ya tarar Waira na yi a dazun abu ne mai kyau domin haka na nuna sha'awarta ga addinin musulumci ne. Wayarsa dake hannunsa ya taba ya shiga sashen hotuna ya kama hotonta da ya dauke ta tana bachi yayi ta kallo kamar ba gobe.
A daren Ummi kasa bachi ta yi saboda tunanin da ya zame mata biyu ta rasa ina zata bullo, wane zata dauka wanne zata aje. Sai kusan asuba ta samu runtsawa asuba na yi kuma ta farka ta yi sallah ta fito dakinta kamin ta kawo kasa ta hango mijinta dake kokarin hauro stairs din.
“Na san baki yi bachi ba yau, zaki takura kanki da tunani ne kawai na raya haka saboda ba zo kin kwanta a bangarena ba”
Kamin ta karaso inda yake har hawaye ya cika idonta.
“Ba ni da sauran karfi a yanzu Abiey, dukansu yayana ne, ban san wa zan goyawa baya ba, a zan iya zaba a tsakaninsu ba, kuma na san hakan zai haifar da matsala da karin rashin fahimta ne a tsakaninsu, a maimakon a samu mafita sai abun ya kara lalacewa”
“Ina ganin kamata yayi ki fito fili ki fadawa Ameer gaskiya nima zan sanar da Maleek”
“Ba lallai ne ya fahimta ba, Ameer yana da wuyar sha'ani, yar alakar dake tsakaninmu zata yi tsami, da ma ace zan iya tankura Maleek wata kila shi zai iya hakura, domin Ameer yana son Waira sosai fiye da tunaninka, yadda kike ganin kamar cutar da ita zai yi ba zai yi haka ba, na ga kaunarta idonsa”
“Amman kuma kika kasa ganin hakan a idon Maleek karki zama selfish mana Zahra, ni ma ina son farinciki ďana fiye da yadda kike son Ameer, ina bin komai a hankalin ne saboda Matsalar da kike ciki... Dan haka ina ganin abun da ya dace kawai a fitar da yarinyar nan waje ta yi karatu kamin mu ga abun da Allah zai yi”
Ummi bata da karfin cewa komai a yanzu, ta san Abiey ba zai fahimce ta, haka ma Ameer ba fahimtar da zai yi ba.
“Allah ya zaba mana abun da ya fi zama alheri, bari na shiga kitchen”