← Book details Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 176

Sashe 7

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Daga inda take kwance gindin ruwan ta hango yara suna hawan bishiya suna tsinkar yayan itatuwanta, kamar an cikareta haka ta tashi tsaye da sauri tana kallonsu, daman can babu abun da ta aje a ranta sai keta da son azabtarwa, itacen dake kusa da ita ta kama ta hau fir sai gata ta dale kan itacecen haka ta rika bin itacen tana sauka saman wannan ta hau wannan har ta isa gurin da yaransu, bata tsaya yi musu cewa su sauko ko su daina ba, saboda tana da hurumin hana su domin itacen ba na gidansu ba ne, ko da na gidansu ne bata da wannan damar balle na wajen gidan.
Sai da ta kalli yaron da ta fi girma ta turashi da karfi ya fadi kasa, sai ta fara dariyar mugunta haikam, sauran yaran na ganin haka suka sauka daga kan itatuwan suka ranta a ana kare suka bar yaron daya fado kasa yana ta ihu da neman ceto. Mikewa ta yi tsaye saman itacen ta tsinki ganyensa da wani gafe na reshen itacen ta fado tun daga kan itacen zuwa kasa ta tsaye, ta nada itacen da ganyen ta dora a kanta sannan ta dauki fruit din daya fado ta fara ci tana yamutsa fuska saboda tsami, hango mutane tafe ya saka ta gudu ta boye a bayan wasu itatuwan tana leke har aka dauke yaron, sannan ta zauna a gurin tana ta dariya.
Daga zama sai gata kwance ta daga kafafuwanta sama ta jingina su da itacen tana kallon sama, labarin da Eid ya bata take tunawa, akwai wasu mutane masu abun hawa da rayuwa da ba irin na su ba, abincinsu da yarensu da addininsu ba irin nata ba.

“Kuma suna jin dadi rayuwa?”

Ta tambayi kanta da yaren da shi aka haife ta kuma shi ta iya, zuciyarta ta raya mata babu wani jindadi ga wanda yake rayuwar da ba irin ta su ba, a gurinta hawan tsaunuka da itace da manyan duwatsu ya fi komai dadi, ka shiga lambu ka tsinki abun kake so ka ci ya fi komai saka nishadi.

“Outarrr”

Ta maimaita tana dariyar sunan da ya fada na abun hawansu Mota take kokarin iyawa. Kamar daga sama ta ji muryar Eid, da sauri ta tashi zaune tana kallonsa har ya karaso. Tada ita yayi tsaye ta cire mata ganyen data saka a kanta ta jefar ya rike kafadunta.

“Me kika aikata?”

“Ban yi komai ba”

Ta bude hannayensa zata tafi ta dauko ganyen ya riketa.

“Sarki yace a zo da ke, kin jefar da yaro”

A take ta saka dariya, duk kuwa da kasancewar bata ga wasa a fuskarsa ba, sai dai ta san ba a yau ta saba irin wannan ba kuma kowa be tana ce mata komai ba, sai dai Eid yana yawan nuna mata abun da take yi ba shi da kyau, yana daga cikin dalilin da ya saka bata da kawaye kuma kananan yara basa matsawa kusa da ita.

“Na sha fada miki ki daina wannan halin”

“Su suka ja ni”

“Karya kike yi, ba za su ja ki haka nan kawai ba”

A karo na biyu ta buge masa hannu saboda ya karyatata, sai ya sake rike kafadarta gam.

“Muje Sarki yana son ganinki”

Ya saki kafadar ya rika hannunta ya ja kamar wata kuya yana gaba tana baya har suka isa cikin fadar, tsananin girmamawa da ganin kimar sarki ko yayan mulki a garin ba a hada ido da su sai idan ta kama dole, idan za a gaishesu kuma sai an risina. Eid ya gaishe da sarkin dake zaune tare da jama'arsa sannan Waira ta risina ita ma ta kwashi gaisuwa, Sarkin dake cike da far'a da murnar bikin da aka yi ya kalli Waira da idonta ke kasa hannunta ke rike cikin na Eid yayi murmushi.

“Ranar yau rana ce mai girma da muhimmanci a garemu, be kamata ace kin kuntatawa wani ba, ba wannan ne karo na farko da aka kawo min kararki ba, amman wannan ne karo na farko da ya kamata na gargade ki, kuma ya yafe miki, kar ki yarda a sake kawo kararki akan kin zalinci wani, zan yafe miki iya na yau kawai saboda albarkar ranar yau da kuma kasancewar ban taba gargadin ki ba sai a yau, ke ta dabam ce a cikin yara sa'aninki Waira, matsayinki da na su ba iri daya ba ne, kina jiran wani matsayi da su har su mutu ba za su iya hawansa ba, ya kamata ki banbanta kanki da sauran yara”

Ta risinar da kanta kamar yadda ta san na amsawa Shugaba idan yana magana.

“Na gode”

Hannun sarki ya daga mata, sannan ya kalli Eid ya ce.

“Wannan ya zama karo na karshe da zaka rike hannunta a gaban idona”

Shi ma ya amsawa sarki da kai.

“Za'a kiyaye”

Sannan ya saki hannun nata ya juyo ya fito sai ta biyo bayansa, a yanzu kuma fushi take da shi saboda shi ya kawo ta gaban Sarkin, har aka mata gargadi abun da ba a taba yi mata ba, suna fitowa ta sauya hanya ta nufi inda dakinsu yake, tana shiga ta shige dakinta ta kwanta daga bakin kofa tana kallon waje, fuska murtuk babu annuri, zakarun da suke gidan suka taso suka tare a bakin kofar suna kallonta, tana ganin haka ta san abun da suke bukata, sai ta tashi ta bude inda take aje musu abunci ta dauko ta zuba musu su ka ci, ta bude wani karamin rame ta dauko beranta ta dawo bakin kofar ta zauna tana shafa shi, a gurin ta yi ta zama har hudu yayi sannan ta tashi ta koma kan shimfidarta ta kwanta ba tare da ta kunna fitilar aci balbal da ta saba kunnawa ba.
Kamar wata gawa tun da ta kwanta bata farka ba sai da hasken rana ya keto dakin, sannan ta tashi zaune tana murza ido, ta dade a zaune sannan ta tashi ta fita ta yi fitsari, ba musulma bace balle ta san wanke fuska da yin alwala ayi sallah, ba mai tsabta ba ce balle ta san wanke baki da hannu kamin aci wani abu, tana dawowa dakin ta nufi inda ta saba aje ayabar ta sai ta samu an huda ta kasa an ci ayabar an ja wata a zubar, a fusace ta juyo ta kalli beranta dake kwance akan gado yana sharbar bachi ta watsa masa wata uwar harara. Gurin da ta saba aje bulala ta dukan beran da zakarun da suka mata laifi ta nufa ta dauko ta labta masa daya, da gudu ya shige cikin katifar ta kada yana tsuwa kamar wani karamin tsuntsun, haka take a duk lokacin da suka mata laifi sai ta zanesu da bulala haka kuma baya hana anjima ko gobe su sake yin barna. Zaunawa ta yi a gurin ta fara kuka domin fushin da take na jiya ta farka da shi a yau wannan ya saka na ayyana a ranta ba zata fita ko'ina ba balle ace ta yi laifi, gashi bera ya cinye ayabar data aje, ya lalata sauran.

MALEEK POV.

Yana jin lokacin da aka kwankwasa kofar dakin, amman ya kasa amsawa sai juyi yake akan gado gaba daya yau ya farka jikinsa babu dadi kamar wani mai laulayi.
Ya kusan minti talatin saman gadon yana ta juyi sannan ya sauko ya shiga bathroom yayi wanka da ruwan zafi mai zafi sosai wai ko zai jidadin jikinsa ya fito ya shirya kansa sannan ya bude kofar dakin ya fita, kamin ya karasa saukowa ya aikawa mahaifiyarsa da gaisuwa domin baya son karasawa kusa da dinning dinta ma saboda kanensa da suke gurin, a ko wace safiya idan za a karya a tare da juna to ana rabawa ne ita ta yi breakfast dinta tare da yan matanta Twins Nimra da Namra shi da kanensa Mahmood su karya a dinning din Babansu. Can kasan makoshinta ta amsa masa ta kawarda kai daga barin kallonsa ta cigaba da cin abincinta, a yanzu kokari take ta sabawa kanta da sabuwar dabi'ar yaye Maleek a zuciyarta, so take ta saba da halayensa da dabi'unsa so that ta samu peace of mind, ta samu natsuwa ta cire shi da damuwarsa a ranta. Sai da ya fice daga falon ya shiga bangaren mahaifinsa sannnan Nimra ta tashi tsaye ta dauki jakarta dake gefenta.

“Ummi na tafi kar nayi latti”

“To a dawo lafiya”

Hajiya Zahra ta fada ba tare da ta kalleta ba, fuskarta da muryarta suka kasa boye damuwarta, Nimra ta zagaya ta dayan side din mahaifiyarta take ta yi hugging dinta ta sumbanci gefen fuskarta.

“Ummi we love you dan Allah ki daina damuwa”

Ummi ta dago ta kalleshi da murmushi a fuskarka, sai ta ji abun da ke tsaye a tsakanin kirjinta da zuciyarta yana sauka kasa kamar suncewar tayar motar.

“Na gode Allah daya ba ni ku, Allah muku albarka ya ba ku mazaje na gari”

A tare suka hada baki suka amsa da Ameen, sannan Nimra ta fice daga falon tana ta sauri kar ta yi latti.

Maleek yaja kujera ya zauna yana murmushi ganin kanensa Mahmood da Mahaifinsa suna dariya.

“Ni na fada maka wannan ka bari idan aka siyo wannan dan wasan ka ga yadda zai gyara muku team”

Mahmood ya girgiza kai shi har yanzu be yardar team dinsa ya kasa ba.

“Babu wani gyara da zai mana, daman matsalar mu wannan couch din ne kuma yanzu mun sauya shi”

“Ai idan kana neman team din banza idan ka kai ga Man U ka saka aya, ku Manchester United daga manyanku har kanana ba ku iya komai ba sar shirme, gashi ba ku iya cire kudi su siye manyan yan wasa, idan kana son team mai kyau Malam je Arsenal”

Cewar Maleek Abiey ya saka dariya, ba team din Arsenal yake ba amman yana supporting dinsu domin sun san abun da suke yi ba kamar Manchester United ba.

“Kuma Arsenal din idan aka cire manyan yan wasanku biyu sauran ba za su iya yin komai da kansu ba”
Chapter 7 · 0% Book details