← Book details Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 156 OF 176

Sashe 156

Wani Gari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Namra ta saki Ummi ta nufi bangaren Abiey da gudu. Duk yadda Abiey ya so Ummi ta zauna a gida, shi da Mahmood su tafi asibiti bata yarda ba, ganin take kamar ma ya mutu ne gaba daya, ko kuma zai mutu idan bata kusa da shi. Abiey ya karbi wayarta ya sake kiran number Ameer din police din da suka yi jagorancin kai shi asibiti suka amsa wayar suka fada masa asibitin da suke. Ummi gaba daya hankalinta a tashe yake son kawai take ta ga Ameer a dole tare da ita suka je asibitin. Ko da suka isa asbitin har likitoci na masa dressing guraren da ya samu rauni, kirjinsa sai kafarsa sai kuma gefen kafadarsa. Sai dai ba abar Ummi ta ganshi ba sai da aka gama masa komai aka ware masa dakinsa sannan Ummi ta shiga tare da Namra da Humairah Mahmood da Abiey. Tana ganinsa ta isa gurinsa da sauri ta kama hannunsa ta rike tana ta kuka.

“Haba Ameer miye haka? Police sun fada mana gudu kake yi sosai ana daga maka hannu ka tsaya amman baka yi ba har ka bugu wasu motocin? So kake ka kashe kanka? Saboda me Ameer”

Cikin wani yanayi na rashin lafiya da azababen ciwon kai Ameer ya kalli Ummi yana murmushin karfin hali ya ce.

“Ba haka ba ne, jikina ne yayi nauyi burki kuma ya cige”

“Gudu yake sosai ni ma dazun har tsoro ya ba ni, baya duba kowa idan hankalinsa ko ransa ya bace”

Humairah ta fada tana share hawayenta ganin babu ko riga a jikinsa sai bandeji. Abiey ya ce.

“Rayuwa guda ce dai, kuma yanzu girma kake yi ya kamata ka rage wasu abubuwan ko dan mahaifiyarka da ka ga yadda ta tashi hankalinta a yanzu nan muma yadda hankalinmu ya tashi da baka aikata haka ba, Alhaji Bashir ma yanzu na kira na fada masa da sauki amman hankalinsa duk ya tashi, kana da mutane masu son rayuwarka ya kamata ka tausaya musu ka kula da kanka”

“Zan kiyaye gaba Abiey i promise”

Ya fada sannan ya kalli mahaifiyarsa da har lokacin hawaye take yayi murmushi.

“Ummi I'm fine kin gani, dan Allah ki daina kuka”

“Ka yi alkawari ba zaka sake irin wannan abun ba? Idan ma kashe kanka kake son yi ka bari sai na mutu, amman a yanzu babu abun da nake bukata sai rayuwarka”

“Hakan ba zai sake faruwa ba Ummi na miki alkawari”

Namra ta masa hannu ya amsa Mahmood ma yayi masa kamin ya amsa Mr Bashir ya shigo dakin hankali tashe baya ganin kowa sai Ameer Mommy tana bayansa ita kan sai hawaye take kasancewarta mace bata iya rike kuka ko damuwa. Abiey na gama fadawa Mr Bashir abun da police din suka fada masa ya zabura ya rufe Ameer da fada kamar zai doke shi har sai da Ummi ta shiga tsakiya ta tare Ameer.

“Ni ma na masa fada, ai that's enough”

“No it's not enough duk wani iskanci da yake ina jurewa ina dauka amman ban da wasa da rayuwa, idan kuma ka ce haka zaka yi to sai mu saka kafar wando daya da shi”

“Daddy I'm sorry it wasn't intentionally”

“Na dai fada maka”

Daddy ya fice a fusace, Abiey ma fita yayi domin ya san Ummi ba zata yarda ta bishi su tafi gida a yanzu ba. After like 5 minutes Doctor ya shigo ya bukaci kowa ya fita a bar Ameer shi kadai ya huta suka saka masa drip tare da magani sannan suka fice within seconds bachi yayi gaba da shi.
[8/12, 8:57 PM] 🦋-🦋: 78

Skylines Hospital aka kwantar da ita shi da abokin aikinsa Dr George suka dubata duk wani abun da ya kamata ayi mata suka mata sannan ya fito daga asibitin ya nufo gida. Yana fakawa harabar gidan ya ji wata mahaukaciyar yunwa ta sako shi gaba, kusan haka ya wuni kamar mai azumi sai da ya shigo falon Ummi ya nufi kitchen dinta ruwan zafi ya fara zubawa ya sirka da na sanyi zafin ya ragu ya dauka ya sha be ko iya jira ya hada tea ba.

“Waye a kitchen?”

Namra ta fada a lokacin da take saukowa stairs domin ga ga wulgawar mutum amman bata tantance ko waye ba, kai tsaye ta nufi kitchen din ta leka sai ta yi arba da Maleek with surprised ta ce.

“You...? Yanzu ka shigo?”

Ya daga mata kai kawai ya dauki plate ya fito daga kitchen din ya aje plate din a dinning.

“Zuba min abinci kamin na sauko”

Ya nufi upstairs, dakinsa ya shiga ya tsabtacen jikinsa ya canja tufafi ya fito ba tare da ya shafa komai a jikinsa ba, domin yunwar cikinsa ta kusan firgitashi. Spoon ya dauka da sauri ya fara cin abincin hannu baka hannu kwarya.

“Baka ci abinci ba since?”

“Gaba daya yau banci komai ba, sai yanzu ma nake jin yunwar Ina Ummi?”

“Tana asibiti?”

Ya kalleta da sauri.

“Nonono ba ciwonta ba ne, Ameer ne?”

Har yanzu ma kallonta Maleek yake domin jin ba'asin. Namra bata yi kasa a guiwa ba ta karanta masa komai a take ya tsayar da cin abinci yana yawo da idonsa a falon.

“Abiey fa?”

“Yana cikin gida, ina ita Nuwaira?”

“Tana asibiti bata da lafiya, shiyasa na fara aje ta can”

Ya zuba ruwa ya sha ya tashi ta dauki wani cup din ya hada tea ya dauki cup din ya nufi bangaren Abiey rike da cup din tea. Abiey na yi arba da dansa farinciki ya lullube shi ganin dansa lafiya kalau babu rauni a tare da shi sai gajiya da yunwar da ya kwaso har ta saukar masa da rama na wuni daya. Maleek ya zauna cikin jindadin abubuwan da suka faru ya fadawa Abiey komai, take dadi ya lullube Abiey jin yadda dansa ya zama Jarumi cikin birnin matsafa ya rinjayesu da karfin ayar Allah da tsaronsa, kamar wanda ya samu tv haka Abiey ya rika kallon Maleek yana alfahari da shi. After ya gama bashi labarin ya dauko maganar Ameer Abiey ya girgiza kai.

“Namra ta fada maka ko? Umminku ma tana can asibiti ance bachi yake amman tace ba zata dawo ba sai ya farka”

“Daman na yi tunanin haka, shiyasa da yayi ta kirana na ki na daga, saboda ba zan iya masa karya ba, kuma na san gaskiyar zata yi effecting dinsa, and i san Ameer irin mutanen nan da idan rai ya bace basa iya controlling kansu, and zai iya facing komai ba”

“Na dai fada masa, ya kamata ya kiyaye ko dan mahaifiyarsa”

“Yes”

Maleek ya amsa sannan ya mike tsaye ya aje cup din.

“Bari na leka asibitin daga sai an fada mata halin da Nuwaira take ciki, saboda a samu wanda zai kwana a tare da ita asibitin”

“Okay ka cigaba da rike addu'a fiye da da Maleek”

“Dole ai Abiey, ni na ga tasirin addu'a a zahirinta kuma hakan ya kara min kwarin guiwar rike ta da hannu biyu”

“Good Allah ya kara tsarewa, bana shakkar ka shiga ko'ina Maleek I'm proud of you”

“Thank you”

“Idan ta farka Cp yace min za su dauki statement dinka da nata saboda gaba, kuma tsarin haka yake dole san komai ya faru”

Daf da zai fice Abiey ya fada masa haka, sai ya amsa da.

“Okay”

Sai da ya sake komawa bangaren Ummi ya shiga dakinsa ya dauko keys da waya sannan ya dauko ya fice daga falon. Wata motar ya dauka ta dabam ba wadda ya dawo da ita ba, sai da yayi warming dinta sannan yayi reverse masu gadim suka bude masa gate. Tun da ya kama hanyar asibitin yake tunani daya har ya isa, a harabar asibitin ya faka ya fito ya nufi masallacin yayi alwalar Magariba ya shiga ya gabatar da sallah tare da mamu sannan ya fito ya kira wayar Ummi tana ganin kiransa ta daga da sauri.

“Maleek I'm sorry na manta ban kira ba how are you?”

“I'm fine Ummi kuna ina? Na shigo asibitin”

Yana tafiya tana fada masa har ya isa. Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya tura kofar dakin ya shiga sai ya samu Ummi da Fiyya zaune akan carpet din dake shimfide kasa Ameer kuma yana kan gadon goshinsa da kasa, da alama taimama yayi kamin Sallah Magariba a madadin alwala. Tun da ya dago ya kalli Maleek sau daya ya sauke kai be sake kallonsa ba har Maleek ya iso kusa da shi.

“Ya jikin?”

Maleek ya tambaya.

“Alhamdulillah, ya hanya? Hope kun iso lafiya”

“Lafiya kalau nake ni, ita dai Nuwaira tana asibiti amman ita ma da sauki ina tunanin ciwon da ta ji ne sai gajiya da tsoro”

Ummi ta mike tsaye cikin karfin hali ta nufi inda yake tsaye tana taba jikinsa ta duba wai ko ya ji ciwo sai kawai ya saka dariya.

“Lafiya ta kalau fa Ummi sai da muka gama magana da Abiey sannan na iso nan I'm fine”

“Zaka iya boye min ai”

“Amman kin san idam ba lafiya nake ba Abiey ba zai bari na zo nan ba”

Sai ta sake shi.

“Ita kuma fa?”

“Tana asibitin da nake aiki, amman da sauki Abiey ya fada min tun da rana kike nan, ya kamata ki tafi ki duba Nuwaira daga nan sai ki wuce gida Hanne ko Namra su je su kwana da ita, karki ce min zaki kwana a nan please”

Ameer ya ce.

“Ni ma ba zan bari ba, ta ga jikin nawa ai da sauki maybe ma su sallame ni soon”

“Toh wa zai kwana da kai, Mommy ka tafi fa, Humairah kuma na ce Mahmood ya aje su gida ita da mahaifiyarta da Hajiya, kuma mun yi da su gobe yaje ya dauko ta tare da Hajiya ta sake dubaka saboda na fada musu zan kwana a nan”

“Ga Fiyya zata kwana a nan”

Maleek ya kalleta. Sai ta ce

“Yes I'm his sister zan iya kwana a nan, ina wuni”

“Shut up mace da ke? Duka zaku iya tafiya zan kwana a nan”

Da mamakin Ummi da Ameer suka kalleshi sannan suka kalli junansu. Fiyya ta dan turo baki daman tana yaba masa a rashin mutumci gashi yau ma ya gwatsaleta.
Chapter 156 · 0% Book details