Sashe 69
Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Shima Sadiq zuwan su wajen Tahir na jinsa ya na waya ya na kuma kwatancen inda su ke
Ba jimawa sai ga wasu samari suma bazasu wuce sa'aninsu ba.
Sadiq ya gabatar da su da cewa abokan aikinsa ne sai Tahir ya Fahimci daga inda ya ke Hidimar kasar sa ne to ammh me ya kawo su nan wajen?
Yaji ana kora jawabin bai tsaya Saurara duka ba ya dai fahimci kamar Aure za'a Daura? Ammh abun mamakin Daurin auran wa?
Ya na cikin wannan Tunanin yaji ana Fadin"Ina Sadakin na ku?
Sadiq ya karkato aljihu ya fiddo kudi ya mika nan da nan aka kirga Dubu Talatin cif.
Baba Tanko ya mika ma Saminu da ke gefensa Lokaci daya ya kallesu ya na Fad'in "Waye zai auri Hasiyan a cikin ku?
Tahir yaji kamar kunnensa ya Toshe ya na shirin mgana Sadiq yace"Ni ne."
Baba Tanko ya kallesa daga sama har kasa kafin yace"To ka dai san komai da ya shafi yarinyar ko?
Sadiq ya gyad'a masa kai batare da ya yi mgana ba.
Baba Tanko yace"Kai ko saurayi a haka kuma zaka zira jikin ka?
Ko baka duba asaran Dukiya ba ka Duba ta lafiyan ka."
Sadiq ya dago ya na kallon Baba Tanko na wani Lokaci kafin yace"Ni ai ba ni da arzikin ma ballatana na duba hakan. Mganar lafiya kuma Allah shi ke da ciwo kuma waraka daga wajensa ta ke."
Baba Tanko ya kalli Baba Saminu shima ya kallesa suka had'a ido.
Kafin Baba Tanko ya yi gyaram murya yace"Shikenan daman shawara ce. Waliyin ka ya matso kusa tare da Shaidun ka."
Sadiq ya nuna Tahir ya na fad'in"Shi ne Waliyina. ya nuna sauran ya na karishe fad'in"Su ne Shaidu na."
Baba Tanko ya kalli Tahir kafin yace"Shikenan daman Uwar ta su ta gayamin kai maraya ne ko?
Sadiq ya kara gyad'a masa kansa.
Tahir magana ya ke so ya yi ammh Sadiq ya hana shi yana ji ya na gani aka fara gudanar da Sigan Daurin aure.
Sadiq ya masa Rad'a a kunnensa da fadin"Kayi abunda ya dace. Zan yi maka karin bayani in muka fita."
Tahir ya na ji ya na gani ya karb'an ma Sadiq auran Hasiya akan Sadaki naira Dubu Talatin auren da ya samu Shaidu sama da Ashirin saboda kafin a Daura auran wasu mutanen sun karu ciki har da Isuhu Yaron Adda.
Domin bayan Fitan su Sadiq ya koma da mai motar domin kwashe kaya Amma tace maza Habiba ta rakasa chan shima.
Adda Rukayya ce ta kasa Hakuri ta kalli Amma ta na fadin"Amma wai me ke faruwa achan gidan Baba Tankon ne?
Amma ta juya ta na fadin
"Auran HASIYA za'a daura"
Ba ita kadai ba hatta mu sai da muka girgiza gabadaya muka juyo muna kallonta bakina ya fara rawan da na gaza Furta komai.
Inna Talatu ne tace"Da wa kuma? Sannan ba mu da labari?
Amma tace"Abun ne yazo a lokaci kurare."
Yadda na sandare a zaune haka su Adda Rukayya suka sandare sun kasa mgana Amma ko sai kasa Minti ta ke yi da Cimgam hankalinta kwance.
Muna nan zaune muna kallo kallo Ramatu ta kalleni yafi sau goma ta kasa mgana.
Sai kawai ga wayar Adda Fati a wayar Adda Rukayya ta na Dauka sai ta saka a Amsa kuwwa cikin mamaki tace"Rukayya Auran Hasiya fa aka Daura yanzu nan"
Adda Rukayya taja Numfashi kafin tace"Uhmm da wa?
Adda Fati tace"Da wanda in nayi miki bayani bazaki gane shi ba. Wani SADIQ ne, Wanda ya taba kai Amma asibiti kwanaki da Ciwonta ya tashi."
Gabana ya fad'i ras!
"ASSADIQ.."
naji zuciyata ta bani, Wani Dum naji acikin kaina ina jin suma mganganu ammh kuma bana fahimtar abunda suke fad'a.
Naji dai sanda Amma tace a fara fita da kaya ita kuma ta fita tsakar gida ta na Rabon minti lokaci d'aya ta na fad'in"Na daurin Auran Hasiya ta ne, yanzu aka Daura mata aure a gidan babansu na Dirimi."
Ni ko ina zaune rike da Hanifa na kasa tashi sai da naji Ramatu ta jijjigani ta na fad"in"Hasiya me na ke ji haka?
Na bita da kallo da idanuwana da suka Juye kamar yar maye.
Sai kuma na koma ina bin Dakin namu da kallo da yara ke ta shiga suna fita da kaya.
Yanayin da na ke ciki yasa na kasa ma yin wani kakkwaran motsi.
******
Kamar yadda Ramatu ta jijjigani haka Tahir ya Jijjiga Sadiq bayan sun fito daga Falon da aka Daura aure.
Cikin Fitan Hayyaci yace"Sadiq me na ke ji haka ne? Na kasa Fahimtar komai ka yi min bayani."
Sadiq ya kasa mgana sai da komai ya tabbata kuma ya fara jin wani irin Nadama da Tsoro.
Aure fa ya yi batare da sanin Abba da Umma ba. ba tare da sanin wasu daga cikin Ahalinsa ba.
Anya bai yi kuskure ba? Tabbas bai yi Tunanin faruwar haka ba sai yanzu ya zai yi da ita? Wannan shi ake kira Halin Tsaka mai wuya.
Sadiq ya Runtse ido ya bude shiyasa yasa ka bakin glass saboda kalan idanuwansa sun sauya daga fari zuwa Jajaye.
Tahir ne ya kara masa wani jijjiga mai yawa ya na kara fad'in"Sadiq aure ka yi? Aure ka yi batare da sanin Yan'uwan ka ba?
Kasan me ka aikata kuwa Sadiq?
Sadiq ya kwace jikinsa da Sauri ya na Fadin"Na sani..na sani Tahir Aure na yi. Aure na yi batare da sanin kowa ba"
Ya fad'a cikin karaji, Tahir ma cikin karajin yace"meyasa ka yi haka?
Kasan ko me ka aikata? Kasan wani irin girman zunubi ka aikata?
Sadiq ka na cikin hayyacinka kuwa?
Sadiq ya ji kansa ya sara ya Dafe kanshi lokaci d'aya ya na fad'in"Na sani Tahir na auri Hasiya saboda ina jin Tausayinta. Sai dai ban aureta domin na yi zaman aure da ita ba. Zan SAKE TA da zarar na inganta Rayuwarta ta yi tafiyarta ni kuma salin alim ba wanda ya sani zan koma gida na auri zabin iyayena."
Ya na mgana ne Ammh Tahir ya saki baki kawai ya na kallonsa ya fara Tunanin kamar Sadiq ya zare ko ya Haukace.
Daman shi ya sani wani abu zai faru mutanenan ba su bar Sadiq haka ba.
Ganin al'amarin ya yi kamar almara kamar a mafarki.
Sadiq ya yi aure? Kuma ba Sultana ya aura ba wata zabiyar yarinya mai mummuna kaddara a cikin Rayuwarta.
Yana tunanin Sadiq ba kanshi daya ba gaskiya to ko ya na sane ya aikata haka bakin Alkalami ya riga da ya Bushe.
ba bu wanda ya isa ya sauya wannan Kaddaran.
Kaddaran SADIQ ya auri HASIYA.
Alhamdulillah.
*Karshe littafi na d'aya*
Turka turka kenan, Miye makomar auran Hasiya da Sadiq?
Ina sultana?
Iyayensa fa?
Tahir zai rufa masa asiri?
Zai saki Hasiya kamar yadda yace?
Ko zai gayama iyayensa labarin Hasiya?
Hasiya zata samu daidatan kaddaranta tare da Assadiq?
Zata samu farincikin?
Shin za su yi zaman aure?
Ko zata kara zama bazawara a karo na uku?
Daga karshe wani irin Kalubale da TSAKA MAI WUYA ke jiran Sadiq, ga shi dai ya tabbata MIJIN HASIYA?
Sadiq zai auri Sultana? In ya aureta ya matsayin Hasiya a wajensa?
*Duk tarin wad'anan tambayoyin suna cikin Littafi na biyu da na uku, zaku same shi a kan manhajar AREWABOOKS#Jamilaumarjanafty 09069067488*
*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*
*Zamu fara littafi na biyu gobe in sha Allahu a Arewabooks, yan WhatsApp kuma sai kun cike limit din mutane 300 in sha Allahu sannan zamu dora, Nagode kwarai da soyayyarku Allah ya Hore ma kowa halin biya Amin.*
*Janafty*
*12/01/2024*
Ba jimawa sai ga wasu samari suma bazasu wuce sa'aninsu ba.
Sadiq ya gabatar da su da cewa abokan aikinsa ne sai Tahir ya Fahimci daga inda ya ke Hidimar kasar sa ne to ammh me ya kawo su nan wajen?
Yaji ana kora jawabin bai tsaya Saurara duka ba ya dai fahimci kamar Aure za'a Daura? Ammh abun mamakin Daurin auran wa?
Ya na cikin wannan Tunanin yaji ana Fadin"Ina Sadakin na ku?
Sadiq ya karkato aljihu ya fiddo kudi ya mika nan da nan aka kirga Dubu Talatin cif.
Baba Tanko ya mika ma Saminu da ke gefensa Lokaci daya ya kallesu ya na Fad'in "Waye zai auri Hasiyan a cikin ku?
Tahir yaji kamar kunnensa ya Toshe ya na shirin mgana Sadiq yace"Ni ne."
Baba Tanko ya kallesa daga sama har kasa kafin yace"To ka dai san komai da ya shafi yarinyar ko?
Sadiq ya gyad'a masa kai batare da ya yi mgana ba.
Baba Tanko yace"Kai ko saurayi a haka kuma zaka zira jikin ka?
Ko baka duba asaran Dukiya ba ka Duba ta lafiyan ka."
Sadiq ya dago ya na kallon Baba Tanko na wani Lokaci kafin yace"Ni ai ba ni da arzikin ma ballatana na duba hakan. Mganar lafiya kuma Allah shi ke da ciwo kuma waraka daga wajensa ta ke."
Baba Tanko ya kalli Baba Saminu shima ya kallesa suka had'a ido.
Kafin Baba Tanko ya yi gyaram murya yace"Shikenan daman shawara ce. Waliyin ka ya matso kusa tare da Shaidun ka."
Sadiq ya nuna Tahir ya na fad'in"Shi ne Waliyina. ya nuna sauran ya na karishe fad'in"Su ne Shaidu na."
Baba Tanko ya kalli Tahir kafin yace"Shikenan daman Uwar ta su ta gayamin kai maraya ne ko?
Sadiq ya kara gyad'a masa kansa.
Tahir magana ya ke so ya yi ammh Sadiq ya hana shi yana ji ya na gani aka fara gudanar da Sigan Daurin aure.
Sadiq ya masa Rad'a a kunnensa da fadin"Kayi abunda ya dace. Zan yi maka karin bayani in muka fita."
Tahir ya na ji ya na gani ya karb'an ma Sadiq auran Hasiya akan Sadaki naira Dubu Talatin auren da ya samu Shaidu sama da Ashirin saboda kafin a Daura auran wasu mutanen sun karu ciki har da Isuhu Yaron Adda.
Domin bayan Fitan su Sadiq ya koma da mai motar domin kwashe kaya Amma tace maza Habiba ta rakasa chan shima.
Adda Rukayya ce ta kasa Hakuri ta kalli Amma ta na fadin"Amma wai me ke faruwa achan gidan Baba Tankon ne?
Amma ta juya ta na fadin
"Auran HASIYA za'a daura"
Ba ita kadai ba hatta mu sai da muka girgiza gabadaya muka juyo muna kallonta bakina ya fara rawan da na gaza Furta komai.
Inna Talatu ne tace"Da wa kuma? Sannan ba mu da labari?
Amma tace"Abun ne yazo a lokaci kurare."
Yadda na sandare a zaune haka su Adda Rukayya suka sandare sun kasa mgana Amma ko sai kasa Minti ta ke yi da Cimgam hankalinta kwance.
Muna nan zaune muna kallo kallo Ramatu ta kalleni yafi sau goma ta kasa mgana.
Sai kawai ga wayar Adda Fati a wayar Adda Rukayya ta na Dauka sai ta saka a Amsa kuwwa cikin mamaki tace"Rukayya Auran Hasiya fa aka Daura yanzu nan"
Adda Rukayya taja Numfashi kafin tace"Uhmm da wa?
Adda Fati tace"Da wanda in nayi miki bayani bazaki gane shi ba. Wani SADIQ ne, Wanda ya taba kai Amma asibiti kwanaki da Ciwonta ya tashi."
Gabana ya fad'i ras!
"ASSADIQ.."
naji zuciyata ta bani, Wani Dum naji acikin kaina ina jin suma mganganu ammh kuma bana fahimtar abunda suke fad'a.
Naji dai sanda Amma tace a fara fita da kaya ita kuma ta fita tsakar gida ta na Rabon minti lokaci d'aya ta na fad'in"Na daurin Auran Hasiya ta ne, yanzu aka Daura mata aure a gidan babansu na Dirimi."
Ni ko ina zaune rike da Hanifa na kasa tashi sai da naji Ramatu ta jijjigani ta na fad"in"Hasiya me na ke ji haka?
Na bita da kallo da idanuwana da suka Juye kamar yar maye.
Sai kuma na koma ina bin Dakin namu da kallo da yara ke ta shiga suna fita da kaya.
Yanayin da na ke ciki yasa na kasa ma yin wani kakkwaran motsi.
******
Kamar yadda Ramatu ta jijjigani haka Tahir ya Jijjiga Sadiq bayan sun fito daga Falon da aka Daura aure.
Cikin Fitan Hayyaci yace"Sadiq me na ke ji haka ne? Na kasa Fahimtar komai ka yi min bayani."
Sadiq ya kasa mgana sai da komai ya tabbata kuma ya fara jin wani irin Nadama da Tsoro.
Aure fa ya yi batare da sanin Abba da Umma ba. ba tare da sanin wasu daga cikin Ahalinsa ba.
Anya bai yi kuskure ba? Tabbas bai yi Tunanin faruwar haka ba sai yanzu ya zai yi da ita? Wannan shi ake kira Halin Tsaka mai wuya.
Sadiq ya Runtse ido ya bude shiyasa yasa ka bakin glass saboda kalan idanuwansa sun sauya daga fari zuwa Jajaye.
Tahir ne ya kara masa wani jijjiga mai yawa ya na kara fad'in"Sadiq aure ka yi? Aure ka yi batare da sanin Yan'uwan ka ba?
Kasan me ka aikata kuwa Sadiq?
Sadiq ya kwace jikinsa da Sauri ya na Fadin"Na sani..na sani Tahir Aure na yi. Aure na yi batare da sanin kowa ba"
Ya fad'a cikin karaji, Tahir ma cikin karajin yace"meyasa ka yi haka?
Kasan ko me ka aikata? Kasan wani irin girman zunubi ka aikata?
Sadiq ka na cikin hayyacinka kuwa?
Sadiq ya ji kansa ya sara ya Dafe kanshi lokaci d'aya ya na fad'in"Na sani Tahir na auri Hasiya saboda ina jin Tausayinta. Sai dai ban aureta domin na yi zaman aure da ita ba. Zan SAKE TA da zarar na inganta Rayuwarta ta yi tafiyarta ni kuma salin alim ba wanda ya sani zan koma gida na auri zabin iyayena."
Ya na mgana ne Ammh Tahir ya saki baki kawai ya na kallonsa ya fara Tunanin kamar Sadiq ya zare ko ya Haukace.
Daman shi ya sani wani abu zai faru mutanenan ba su bar Sadiq haka ba.
Ganin al'amarin ya yi kamar almara kamar a mafarki.
Sadiq ya yi aure? Kuma ba Sultana ya aura ba wata zabiyar yarinya mai mummuna kaddara a cikin Rayuwarta.
Yana tunanin Sadiq ba kanshi daya ba gaskiya to ko ya na sane ya aikata haka bakin Alkalami ya riga da ya Bushe.
ba bu wanda ya isa ya sauya wannan Kaddaran.
Kaddaran SADIQ ya auri HASIYA.
Alhamdulillah.
*Karshe littafi na d'aya*
Turka turka kenan, Miye makomar auran Hasiya da Sadiq?
Ina sultana?
Iyayensa fa?
Tahir zai rufa masa asiri?
Zai saki Hasiya kamar yadda yace?
Ko zai gayama iyayensa labarin Hasiya?
Hasiya zata samu daidatan kaddaranta tare da Assadiq?
Zata samu farincikin?
Shin za su yi zaman aure?
Ko zata kara zama bazawara a karo na uku?
Daga karshe wani irin Kalubale da TSAKA MAI WUYA ke jiran Sadiq, ga shi dai ya tabbata MIJIN HASIYA?
Sadiq zai auri Sultana? In ya aureta ya matsayin Hasiya a wajensa?
*Duk tarin wad'anan tambayoyin suna cikin Littafi na biyu da na uku, zaku same shi a kan manhajar AREWABOOKS#Jamilaumarjanafty 09069067488*
*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*
*Zamu fara littafi na biyu gobe in sha Allahu a Arewabooks, yan WhatsApp kuma sai kun cike limit din mutane 300 in sha Allahu sannan zamu dora, Nagode kwarai da soyayyarku Allah ya Hore ma kowa halin biya Amin.*
*Janafty*
*12/01/2024*