Sashe 55
Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ganin Umma ta yi shuru yasa Innani ta kalleta ta na saussauta Murya ta ce"Kwantar da Hankalin ki salamatu. Nasan sauran ya'yan ku sun haihu ammh su din ya'yan su ba jikokin sulaimamu ba ne halas malak . Duk tsiya suna da wani gidan kakanin na su magajin gida fa? Har abada ya'yan su shi da Sulsana ba su da kamar gidan nan. Duk duniya mu ne na su ba su kuma da kamar mu kuma jokokin ya'ya mata na gidan wasu ne jikan D'a Namiji shi ne Jika Salamatu."
Har ta gama maganata ba wanda ya yi ko tari Abba ne yace"Gaskiya ne Innani.."
Innani ta rausayar da kai kafin tace"Ku tashi ku je na gama mganata bad'i za'ayi auran magajin gida da Sulsana."
Abba ya mike ya na fadin"Allah ya kara girma Innani zan fita."
Kai tsaye tace"Allah ya tsare ka. Allah ya kiyaye min kai. Ya rabaka da Sharrin makiya da Mahassada ya Tsare maka dukiyarka"
Abba na ta amsawa da Ameen.
Ficewa ya yi ya na ce ma su Umma ya fita suka rakasa da Allah ya Tsare.
Su dai suna gaban INNANI sun kasa tashi.
Innani ta gama cin Namanta ta na so ta shiga ciki ta huta ta kalli su Umma ta na fadin"Wai lafiya ku ka sakani a gaba haka? ni ku tafi ku ba ni waje zan Huta ne"
Umma ta marairace kafin tace"Innani Auta bai gama bautar kasa ba. Sultana maka.."
Innani ta katse ta da fad"in"Allah ya tsine ma karatu da bautar kasar. nace Allah ya tsine musu tunda su zasu hana A cika sunar ma'aiki Salamatu."
Umma sai ta yi shuru Mama ko Dariya ta ke ta dannewa sai da Innani tace"Ba Magajin gida ba hatta jikokinsu Sulaimanu na da arzikin da zai yi musu komai a cikin gidan nan."
Dariyan da Mama ke dannewa ta Fito fili Innani ta tsaya ta na kallonta cikin mamaki da takaici.
Da Sauri Mama ta danne bakinta na zare ido.
Innani ta yi kafyci kafin tace"Ki yi dariya mana Tunda kin raina ni baki san Darajan Furfura ba. In wannan gajeran matar ne mai katon hanci zaki yi mata Dariya in ta na mgana? Nace zaki yi mata Dariya in ta na mgana Suwaiba?
Mama sai ta dawo cikin natsuwarta jin Innani ta yi kwantancen Uwarta.
Da sauri tace"Yi hakuri Innani ba da gangan ba ne."
Innani tace"Da hakurin ya mutu sadakan nawa kika ba ni?
Nace sadakan nawa kika bani? Iskancin banza da wofi nasan ai maganinki Allah yasa naga masu faska faskan kafafun dangin ki sun kara zuwa gida d'ana wato ana zuwa aci arziki gida babu ko? to wlh Karnukan nan na Sulaimanu ma su kama da Mutane zan saka mallam Saju ya sakar musu duk su farraka yan banza."
Innani ta fad'a ta na kumfar baki. Tasan karonta da karnukan ranar da likita ya zo duba su aka fito da su Innani ta gansu kamar wasu mutane Saboda girma sai da Suma.
Da ta farfad'o ko Har sulaimanu sai da ya sha Allah ya isa mallam saju da likita kuwa har da tsine musu sai da aka yi ranar.
Jawo sandarta ta yi lokaci d'aya tana mike ta ke fadin"Sai ku bar min falo. Tunda ba Sulaimanu ya gyaramin shi ba. nima mai kudi ce iyayena sun bar min gado Ehe."
Haka suka mike sumu sumu suka fice bayan Umma ta ce"a huta lafiya Innani."
Innani ta amsa a Dakile sai da suka Fice tace a fili"Salamatu ba wayau. Duk ba ta Fahimci bakincikin Suwaiba."
Daga haka ta tabe baki kafin tace"Sai dai ko bakinciki ya kasheta auren magajin gida da Sulsana ba fashi."
Da haka ta dogara sandarta ta shige ciki ta nemi gado ta kwanta da gilashinta a ido tunda tace in ta ijiye bacewa ya ke yi.
Wayarta ma ta gama Tsine tsine tace Allah ya tsine ma barawo da uwar barawo. Ahalin wayar gefen gado ta fad'a shikenan da ta nema bata gani ba tace an sace.
Wasa wasa karamar mgana ta zama Babba Domin washegari Innani Sashen Umma ta yini ta rika sata ta na kiran mata su Surayya da kanta ta ke musu mgana ta na fad'in su fara shiri auran Kaninsu da kanwarsu bad'i kowacce haka taji mganar Daga sama ba sanarwa.
Sai bayan Innani ta koma Shashenta suke ta kara kiranta suna Tambayan ba'asi ta na kora musu jawabi.
Surayya tace"Umma gaskiya abun bai yi ba me sultana ta sani na aure yanzu? Sadiq ma nasan ba shi da Ra'ayin aure yanzu."
Umma tace"To ya muka iya. Kun san dai Halin kakar ku."
Surayya tace"Umma kin gayama Sadiq?
Umma tace"A'a na kasa gayamasa ko yau mun yi waya da Safe. Tsoro na ke ji Innani ko Abban ku susan ni na Fad'a masa."
Surayya tace"Ummi ni zan kirasa na fad'a masa gwara ya dakatar da abun kafin ya yi nisa."
Umma tace"To Allah yasa kada sunan ki ya fito."
Surraya tace"ban damu ba Umma. Bikin Kaninmu so mu ke a yi shi one in Gusai in sha Allahu."
Surayya ita ta kira Sadiq ta gayamasa Halin da ake ciki.
Bai yi wani mamaki ba sai dai ya tausayama Innani da ta ke masa shisshigi a rayuwarsa.
Mgana ta waya bazai yuyu ba yasa ranar asabar ya ce ma Tahir zai je Gusai Tafiyan Ujila ya taso masa.
Tahir ya tambayesa kwana nawa zai yi? Yace daya gobe lahadi zai dawo.
Tahir ya yi masa fatan dawowa lafiya.
Domin kwanaki nan fad'a su ke yi akan mutanen da Sadiq yaga ya daukesu da Muhimmanci Fiye da Sauran mutanen da yasan ya na taimako.
In yau bai je gidan ba to gobe sai yaje bayan kullum ya na hanyar zuwa siyan Danwake da ya ke da tabbacin in ma wani tsafin ne ta nan aka saka masa.
Tunda har ka taimake su kuma matar nan ta samu lafiya ka rabu da su mana ammh ya lura Sadiq na so ya saka kanshi a abunda zai zo ya na danasani daga baya.
Shi fa tsoronsa kada Sadiq ya fara son zabiyar yarinyar nan. Tunda yaji Sadiaq din na fadin"kamar kanwarsa ya ke ganinta sannan suna ba shi Tausayi."
Tunda suna son su jaawosa a jiki ne komai ma zasu iya yi. Haka kurum ya ke jin baya son wannan alaqar ta Sadiq da Sabbin mutanen da garin Tausayinsa ya jajibo ma kansa.
Har Sadiq ya tafi shi kad'ai ya rika Tunanin hanyar da zai raba wannan Alaqar da ta fara kulluwa.
Ammh kuma ya kasa samun mafita in dai ta mgana ce har ya yi ya gaji Sadiq bai sauraresa ba.
******
Ba wanda yasan da zuwan magajin gida sai da aka ganshi kawai.
Kuma zuwan daman na Innani ne wanka kawai ya yi ya sauya kaya ko Shashen Umma bai shiga ba ya yi ma Falon Innani Tsinke da ta Rud'e da jin zuwansa
Yana shigowa ta fara
"Maraba maraba da Magajin gida."
Fuskar nan ba Fara'a Siyama da Sultana ne tare da Innani lokacin ma mganar auran ta ke karanta musu. sannan kuma wai ta na koyama Sultana Dubarun zama da miji Siyama na gefe ta na shan Dariya.
Fuskarsa ba Fara'a suna gaishe shi bai amsa ba yace"Ku ba ni waje zan yi mgana da Kakar ku."
Jin sunan da ya kira Innani yasa suka san ba lafiya da sauri suka fice.
Suna Fita Siyama ta kalli Sultana ta na Fadin"Sultana ko Ya Sadiq zai ce ba za'ayi auran ku yanzu ba ne?
Sultana a sanyaye ta ce"Bansani ba. Ammh da hakan ta faru da zan so haka."
Siyama tace"Me yasa kika ce haka?
Kai Tsaye Sultana tace"Na fi so sai na gama makaranta Siyama. na kara wayau tukunna"
Siyama ta jinjina kai kafin tace"Eh kuma fa hakane gwara da wayan ka an fi sanin Darajan ka."
Suna tafe suna Hira har shashen Umma taga gansu ne ta ce suka bar Innani ita kadai Siyama tace suna mgaana da Ya Sadiq ne.
Umma ta yi mirmishi a ranta ta na jin Dadi tasan Dole kanwar naki Innani ta bar mganan auren nan.
Ilai kuwa Sadiq achan Falon Innani Wuta ya bud'e mata.
Kamar bai taba saninta ba sai ta fara kuka ta na fadin"Ni daman in ga ya'yan ku ne kafin na mutu."
Sadiq yace"Duk ya'yan su big sis da ki ke da shi baki godema Allah ba.! In kuma nazo Allah bai bani haihuwan ba fa ya zaki yi.?
Da Sauri Innani tace"Allah ba amin ba. Da ikon Allah sai ka tara zuru'a"
Tsaki ya yi kafin yace"To tunda kinsan Allah me yasa kike yi ma Allah Shisshigi? Aure da mutuwa da Haihuwa al'amarinsa ne na kuma sha miki gargadin cewa in kina so ki Mutu cikin salama ki kiyayi shiga Hurumin Allah."
Innani tace"Na bari alqur'an bazan kara shiga ba."
Kai Tsaye yace"Kin shiga mana. Ina ruwan ki da mganar aurena. Ke zaki zauna da matar in kika aura min ita yanzu? Ko ce miki akayi na gama karatun kenan? Ina gama bautar kasata zan dora masters dina. Mganar aure kuma na Soketa sai ranar da na Shirya Innani."
Innani ta yi shuru bata yi mgana ba.
Ganin haka yasa ya taso daga in da yake zuwa gabanta ya zauna ya rike Hannayenta ya na fadin"Innani ki kwantar da Hankali in sha Allahu ke zaki rakani Dakin Sultana ranar angwancina."
Jin haka yasa Innani ta washe baki ta na fadin"Allah ya nuna min wannan ranar. Allah yasa ina raye ban mutu ba."
Hawayenta ya ke share mata da Hannunsa Lokaci d'aya ya na fadin"In sha Allahu bazaki mutu yanzu ba Innani sai kin Dauki ya'ata ko d'a na ni da Sultana."
Sai Innani ta Rumgumesa ta na fad'in"Idon makiya a tsiyaye a kan jikana. Yadda kace haka za'ayin magajin gida"
Shima Rumgumeta ya yi ya na fadin"Yauwa Kakata mai kyau."
Shikenan mgana ta mutu murus. Kwana daya ya yi washegari lahadi ya Dawo zariya.
Har ta gama maganata ba wanda ya yi ko tari Abba ne yace"Gaskiya ne Innani.."
Innani ta rausayar da kai kafin tace"Ku tashi ku je na gama mganata bad'i za'ayi auran magajin gida da Sulsana."
Abba ya mike ya na fadin"Allah ya kara girma Innani zan fita."
Kai tsaye tace"Allah ya tsare ka. Allah ya kiyaye min kai. Ya rabaka da Sharrin makiya da Mahassada ya Tsare maka dukiyarka"
Abba na ta amsawa da Ameen.
Ficewa ya yi ya na ce ma su Umma ya fita suka rakasa da Allah ya Tsare.
Su dai suna gaban INNANI sun kasa tashi.
Innani ta gama cin Namanta ta na so ta shiga ciki ta huta ta kalli su Umma ta na fadin"Wai lafiya ku ka sakani a gaba haka? ni ku tafi ku ba ni waje zan Huta ne"
Umma ta marairace kafin tace"Innani Auta bai gama bautar kasa ba. Sultana maka.."
Innani ta katse ta da fad"in"Allah ya tsine ma karatu da bautar kasar. nace Allah ya tsine musu tunda su zasu hana A cika sunar ma'aiki Salamatu."
Umma sai ta yi shuru Mama ko Dariya ta ke ta dannewa sai da Innani tace"Ba Magajin gida ba hatta jikokinsu Sulaimanu na da arzikin da zai yi musu komai a cikin gidan nan."
Dariyan da Mama ke dannewa ta Fito fili Innani ta tsaya ta na kallonta cikin mamaki da takaici.
Da Sauri Mama ta danne bakinta na zare ido.
Innani ta yi kafyci kafin tace"Ki yi dariya mana Tunda kin raina ni baki san Darajan Furfura ba. In wannan gajeran matar ne mai katon hanci zaki yi mata Dariya in ta na mgana? Nace zaki yi mata Dariya in ta na mgana Suwaiba?
Mama sai ta dawo cikin natsuwarta jin Innani ta yi kwantancen Uwarta.
Da sauri tace"Yi hakuri Innani ba da gangan ba ne."
Innani tace"Da hakurin ya mutu sadakan nawa kika ba ni?
Nace sadakan nawa kika bani? Iskancin banza da wofi nasan ai maganinki Allah yasa naga masu faska faskan kafafun dangin ki sun kara zuwa gida d'ana wato ana zuwa aci arziki gida babu ko? to wlh Karnukan nan na Sulaimanu ma su kama da Mutane zan saka mallam Saju ya sakar musu duk su farraka yan banza."
Innani ta fad'a ta na kumfar baki. Tasan karonta da karnukan ranar da likita ya zo duba su aka fito da su Innani ta gansu kamar wasu mutane Saboda girma sai da Suma.
Da ta farfad'o ko Har sulaimanu sai da ya sha Allah ya isa mallam saju da likita kuwa har da tsine musu sai da aka yi ranar.
Jawo sandarta ta yi lokaci d'aya tana mike ta ke fadin"Sai ku bar min falo. Tunda ba Sulaimanu ya gyaramin shi ba. nima mai kudi ce iyayena sun bar min gado Ehe."
Haka suka mike sumu sumu suka fice bayan Umma ta ce"a huta lafiya Innani."
Innani ta amsa a Dakile sai da suka Fice tace a fili"Salamatu ba wayau. Duk ba ta Fahimci bakincikin Suwaiba."
Daga haka ta tabe baki kafin tace"Sai dai ko bakinciki ya kasheta auren magajin gida da Sulsana ba fashi."
Da haka ta dogara sandarta ta shige ciki ta nemi gado ta kwanta da gilashinta a ido tunda tace in ta ijiye bacewa ya ke yi.
Wayarta ma ta gama Tsine tsine tace Allah ya tsine ma barawo da uwar barawo. Ahalin wayar gefen gado ta fad'a shikenan da ta nema bata gani ba tace an sace.
Wasa wasa karamar mgana ta zama Babba Domin washegari Innani Sashen Umma ta yini ta rika sata ta na kiran mata su Surayya da kanta ta ke musu mgana ta na fad'in su fara shiri auran Kaninsu da kanwarsu bad'i kowacce haka taji mganar Daga sama ba sanarwa.
Sai bayan Innani ta koma Shashenta suke ta kara kiranta suna Tambayan ba'asi ta na kora musu jawabi.
Surayya tace"Umma gaskiya abun bai yi ba me sultana ta sani na aure yanzu? Sadiq ma nasan ba shi da Ra'ayin aure yanzu."
Umma tace"To ya muka iya. Kun san dai Halin kakar ku."
Surayya tace"Umma kin gayama Sadiq?
Umma tace"A'a na kasa gayamasa ko yau mun yi waya da Safe. Tsoro na ke ji Innani ko Abban ku susan ni na Fad'a masa."
Surayya tace"Ummi ni zan kirasa na fad'a masa gwara ya dakatar da abun kafin ya yi nisa."
Umma tace"To Allah yasa kada sunan ki ya fito."
Surraya tace"ban damu ba Umma. Bikin Kaninmu so mu ke a yi shi one in Gusai in sha Allahu."
Surayya ita ta kira Sadiq ta gayamasa Halin da ake ciki.
Bai yi wani mamaki ba sai dai ya tausayama Innani da ta ke masa shisshigi a rayuwarsa.
Mgana ta waya bazai yuyu ba yasa ranar asabar ya ce ma Tahir zai je Gusai Tafiyan Ujila ya taso masa.
Tahir ya tambayesa kwana nawa zai yi? Yace daya gobe lahadi zai dawo.
Tahir ya yi masa fatan dawowa lafiya.
Domin kwanaki nan fad'a su ke yi akan mutanen da Sadiq yaga ya daukesu da Muhimmanci Fiye da Sauran mutanen da yasan ya na taimako.
In yau bai je gidan ba to gobe sai yaje bayan kullum ya na hanyar zuwa siyan Danwake da ya ke da tabbacin in ma wani tsafin ne ta nan aka saka masa.
Tunda har ka taimake su kuma matar nan ta samu lafiya ka rabu da su mana ammh ya lura Sadiq na so ya saka kanshi a abunda zai zo ya na danasani daga baya.
Shi fa tsoronsa kada Sadiq ya fara son zabiyar yarinyar nan. Tunda yaji Sadiaq din na fadin"kamar kanwarsa ya ke ganinta sannan suna ba shi Tausayi."
Tunda suna son su jaawosa a jiki ne komai ma zasu iya yi. Haka kurum ya ke jin baya son wannan alaqar ta Sadiq da Sabbin mutanen da garin Tausayinsa ya jajibo ma kansa.
Har Sadiq ya tafi shi kad'ai ya rika Tunanin hanyar da zai raba wannan Alaqar da ta fara kulluwa.
Ammh kuma ya kasa samun mafita in dai ta mgana ce har ya yi ya gaji Sadiq bai sauraresa ba.
******
Ba wanda yasan da zuwan magajin gida sai da aka ganshi kawai.
Kuma zuwan daman na Innani ne wanka kawai ya yi ya sauya kaya ko Shashen Umma bai shiga ba ya yi ma Falon Innani Tsinke da ta Rud'e da jin zuwansa
Yana shigowa ta fara
"Maraba maraba da Magajin gida."
Fuskar nan ba Fara'a Siyama da Sultana ne tare da Innani lokacin ma mganar auran ta ke karanta musu. sannan kuma wai ta na koyama Sultana Dubarun zama da miji Siyama na gefe ta na shan Dariya.
Fuskarsa ba Fara'a suna gaishe shi bai amsa ba yace"Ku ba ni waje zan yi mgana da Kakar ku."
Jin sunan da ya kira Innani yasa suka san ba lafiya da sauri suka fice.
Suna Fita Siyama ta kalli Sultana ta na Fadin"Sultana ko Ya Sadiq zai ce ba za'ayi auran ku yanzu ba ne?
Sultana a sanyaye ta ce"Bansani ba. Ammh da hakan ta faru da zan so haka."
Siyama tace"Me yasa kika ce haka?
Kai Tsaye Sultana tace"Na fi so sai na gama makaranta Siyama. na kara wayau tukunna"
Siyama ta jinjina kai kafin tace"Eh kuma fa hakane gwara da wayan ka an fi sanin Darajan ka."
Suna tafe suna Hira har shashen Umma taga gansu ne ta ce suka bar Innani ita kadai Siyama tace suna mgaana da Ya Sadiq ne.
Umma ta yi mirmishi a ranta ta na jin Dadi tasan Dole kanwar naki Innani ta bar mganan auren nan.
Ilai kuwa Sadiq achan Falon Innani Wuta ya bud'e mata.
Kamar bai taba saninta ba sai ta fara kuka ta na fadin"Ni daman in ga ya'yan ku ne kafin na mutu."
Sadiq yace"Duk ya'yan su big sis da ki ke da shi baki godema Allah ba.! In kuma nazo Allah bai bani haihuwan ba fa ya zaki yi.?
Da Sauri Innani tace"Allah ba amin ba. Da ikon Allah sai ka tara zuru'a"
Tsaki ya yi kafin yace"To tunda kinsan Allah me yasa kike yi ma Allah Shisshigi? Aure da mutuwa da Haihuwa al'amarinsa ne na kuma sha miki gargadin cewa in kina so ki Mutu cikin salama ki kiyayi shiga Hurumin Allah."
Innani tace"Na bari alqur'an bazan kara shiga ba."
Kai Tsaye yace"Kin shiga mana. Ina ruwan ki da mganar aurena. Ke zaki zauna da matar in kika aura min ita yanzu? Ko ce miki akayi na gama karatun kenan? Ina gama bautar kasata zan dora masters dina. Mganar aure kuma na Soketa sai ranar da na Shirya Innani."
Innani ta yi shuru bata yi mgana ba.
Ganin haka yasa ya taso daga in da yake zuwa gabanta ya zauna ya rike Hannayenta ya na fadin"Innani ki kwantar da Hankali in sha Allahu ke zaki rakani Dakin Sultana ranar angwancina."
Jin haka yasa Innani ta washe baki ta na fadin"Allah ya nuna min wannan ranar. Allah yasa ina raye ban mutu ba."
Hawayenta ya ke share mata da Hannunsa Lokaci d'aya ya na fadin"In sha Allahu bazaki mutu yanzu ba Innani sai kin Dauki ya'ata ko d'a na ni da Sultana."
Sai Innani ta Rumgumesa ta na fad'in"Idon makiya a tsiyaye a kan jikana. Yadda kace haka za'ayin magajin gida"
Shima Rumgumeta ya yi ya na fadin"Yauwa Kakata mai kyau."
Shikenan mgana ta mutu murus. Kwana daya ya yi washegari lahadi ya Dawo zariya.