Sashe 40
Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read
Karfe sha d'aya da wani abu na isa gidan Ramatu na iske Nura na gidan ashe ya dawo yana gari.
Na ganshi sai fama ya ke da Noor itama kuma Ramatu na ciki ta na Shiryawa. Shigowata na karb'eshi ina Fadin"Kawata muguwa ce. Shikenan sai ta barka da reno kai da ka dawo ka na Bukatar Hutu."
Yana dariya yace"Yauwa Hasiya ki yi mata Fad'a bata Tausayamin da na dawo kamar ta samu D'an reno"
Ramatu na daki ta daga Murya ta na Fad'in"In baka nan zan rena ammh fa in ka dawo kaima zaka Tab'a"
Kai ya girgiza kafin yace"Kin ji ta ko?
Ina sabata saman kafad'ata nace"Kyaleta da ni, zan yi maka mganinta."
Ramatu ta fito cikin Shirin Fita ta wurgamin zanin goyo tana Fad'in"Goya yarki mu tafi mun yi rana."
Ba musu ko na goyata Nura kuma ya shige ciki Ramatu ta bi bayansa sai chan suka fito tare.
Tunda yana nan shi ta bar ma gidan Ammh har bakin Titi ya rakomu muka samu abun hawa zuwa gaskiya Bayan Ramatu ta kira Adda Rukayya ta yi ma mai adaidaita kwatance wajen.
Cikin Lokaci ko sai gamu a sababbin anguwannin Gaskiya ne gida mai suna gida Baban su Amna ya gina Tunda babba ne a ma'aikatan MBAIS.
ko da muka isa mun iske gida cike da yan'uwa kamar ana wani Biki Adda Rukayya daga ita sai Habiba ne sai makotanta inda suka taso.
Gidan Babba ne shashen Adda Rukayya dakuna Hudu ne kowanne da Bayuka sannan ga Falo ga kitchen. shashen mai gidan ma babban waje ne sai kuma wani bangare da ba'a gama ba.
Tunda muka shigo na lura da yanayin yan'uwan Mijin sai faman nuna ni suke yi ana kus kus. Wanda ma bai sanni ba duk an gayamasa komai a kaina ban maida kai ba muka wuce cikin Dakin da Adda Rukayya take.
Abun mamaki ta yi maraba damu sosai ta saka wani leshi sabo ta ci kunshi da kitso kamar wata Amarya.
Kai tsaye ta kalleni tace"Hasiya sai yanzu.? Ba fa kowa sai ni kad'ai Allah yasa ma Habiba na nan"
Mirmishi kawai na yi ban ce mata komai ina ta kallon wajen gadajen duk Sabbi ne falon ne bakomai Kila ba'a kawo kayan ba ne. kafin ma mu tambayeta ta shiga gayamana masu kujrun ne ba su kawo ba sai an juma Gadaje kawai aka kawo sai kayan kitchen data siya tunda munzo muje mu tayata jera komai.
Hijabina na cire ban sauke Noor ba Duk da tayi barci yanzu ina Sauketa zata Farka. Habiba sai faman mopping din Tayels ta ke yi ta gama wankin bayi wai a hakama sun Rage ayyukan tunda tun jiya da Daddare duka dawo nan suka kwana.
Dangin mijinta kuwa suna tsakar gida ba abunda suke yi sai shewa da Hira.
Tare da Adda Rukayya da makotanta muka gyara mata kitchen d'inta wasu kayan duk Sabbi ta siya muna ji suna hira da makociyarta adashen dubu Dari Biyu ta shiga aka bata kwasan farko.
Kallona ta yi kafin tace"Hasiya na ware muku wasu kaya suna chan gidan. Har da wasu kayan amfani na cikin gida in Habiba zata dawo zata Taho muku da shi."
Kai na jinjina kafin nace"Mungode Adda Congrat Allah ya sanya alheri yasa an yi ma rai ne."
Ta amsa da Ameen cikin Fara'a kafin tace"Ina Adda Fati ne wai?
Kai tsaye nace"Suna tafe sai da ta biya ta gida ita da Inna Talatu da mutan gidanmu ne su Maman boy."
Adda Rukayya tace"Munafukai za'a zo ganin kwaf."
Ramatu tace"Su zo ai arziki ne sai su dagwala su kara gaba"
Adda Rukayya cikin Farinciki ta saka Shewa suka kashe da Ramatu ta na Fadin"Wlh kuwa su zo su sha kallo."
Nan suka cigaba da Hirar su da Ramatu tare da makotanta ni nawa kawai Mirmishi da eh ko a'a.
Babu wani sakin jiki ko shakuwa Tsakanina da Adda Rukayya yau ma na Fahimci tana cikin Tsananin Farinciki ne shiyasa.
Na ganshi sai fama ya ke da Noor itama kuma Ramatu na ciki ta na Shiryawa. Shigowata na karb'eshi ina Fadin"Kawata muguwa ce. Shikenan sai ta barka da reno kai da ka dawo ka na Bukatar Hutu."
Yana dariya yace"Yauwa Hasiya ki yi mata Fad'a bata Tausayamin da na dawo kamar ta samu D'an reno"
Ramatu na daki ta daga Murya ta na Fad'in"In baka nan zan rena ammh fa in ka dawo kaima zaka Tab'a"
Kai ya girgiza kafin yace"Kin ji ta ko?
Ina sabata saman kafad'ata nace"Kyaleta da ni, zan yi maka mganinta."
Ramatu ta fito cikin Shirin Fita ta wurgamin zanin goyo tana Fad'in"Goya yarki mu tafi mun yi rana."
Ba musu ko na goyata Nura kuma ya shige ciki Ramatu ta bi bayansa sai chan suka fito tare.
Tunda yana nan shi ta bar ma gidan Ammh har bakin Titi ya rakomu muka samu abun hawa zuwa gaskiya Bayan Ramatu ta kira Adda Rukayya ta yi ma mai adaidaita kwatance wajen.
Cikin Lokaci ko sai gamu a sababbin anguwannin Gaskiya ne gida mai suna gida Baban su Amna ya gina Tunda babba ne a ma'aikatan MBAIS.
ko da muka isa mun iske gida cike da yan'uwa kamar ana wani Biki Adda Rukayya daga ita sai Habiba ne sai makotanta inda suka taso.
Gidan Babba ne shashen Adda Rukayya dakuna Hudu ne kowanne da Bayuka sannan ga Falo ga kitchen. shashen mai gidan ma babban waje ne sai kuma wani bangare da ba'a gama ba.
Tunda muka shigo na lura da yanayin yan'uwan Mijin sai faman nuna ni suke yi ana kus kus. Wanda ma bai sanni ba duk an gayamasa komai a kaina ban maida kai ba muka wuce cikin Dakin da Adda Rukayya take.
Abun mamaki ta yi maraba damu sosai ta saka wani leshi sabo ta ci kunshi da kitso kamar wata Amarya.
Kai tsaye ta kalleni tace"Hasiya sai yanzu.? Ba fa kowa sai ni kad'ai Allah yasa ma Habiba na nan"
Mirmishi kawai na yi ban ce mata komai ina ta kallon wajen gadajen duk Sabbi ne falon ne bakomai Kila ba'a kawo kayan ba ne. kafin ma mu tambayeta ta shiga gayamana masu kujrun ne ba su kawo ba sai an juma Gadaje kawai aka kawo sai kayan kitchen data siya tunda munzo muje mu tayata jera komai.
Hijabina na cire ban sauke Noor ba Duk da tayi barci yanzu ina Sauketa zata Farka. Habiba sai faman mopping din Tayels ta ke yi ta gama wankin bayi wai a hakama sun Rage ayyukan tunda tun jiya da Daddare duka dawo nan suka kwana.
Dangin mijinta kuwa suna tsakar gida ba abunda suke yi sai shewa da Hira.
Tare da Adda Rukayya da makotanta muka gyara mata kitchen d'inta wasu kayan duk Sabbi ta siya muna ji suna hira da makociyarta adashen dubu Dari Biyu ta shiga aka bata kwasan farko.
Kallona ta yi kafin tace"Hasiya na ware muku wasu kaya suna chan gidan. Har da wasu kayan amfani na cikin gida in Habiba zata dawo zata Taho muku da shi."
Kai na jinjina kafin nace"Mungode Adda Congrat Allah ya sanya alheri yasa an yi ma rai ne."
Ta amsa da Ameen cikin Fara'a kafin tace"Ina Adda Fati ne wai?
Kai tsaye nace"Suna tafe sai da ta biya ta gida ita da Inna Talatu da mutan gidanmu ne su Maman boy."
Adda Rukayya tace"Munafukai za'a zo ganin kwaf."
Ramatu tace"Su zo ai arziki ne sai su dagwala su kara gaba"
Adda Rukayya cikin Farinciki ta saka Shewa suka kashe da Ramatu ta na Fadin"Wlh kuwa su zo su sha kallo."
Nan suka cigaba da Hirar su da Ramatu tare da makotanta ni nawa kawai Mirmishi da eh ko a'a.
Babu wani sakin jiki ko shakuwa Tsakanina da Adda Rukayya yau ma na Fahimci tana cikin Tsananin Farinciki ne shiyasa.