Sashe 53
Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ni kuma da na fita rakashi da yi masa godiyan ruwa da maltina da kayan marmarin da ya kawo ma Amma sai yace kada na kara wahalar da kaina.
Na cigaba sa sana'ata in yana so zai aiko a siya mishi.
Lura da na yi bayason gaddama yasa na amsa masa da Toh.
Habiba na Tura kasuwa ta yi mana Cefane tunda da Adda Rukkaya ta zo gida kara Duba Amma dubu biyar ta bani Adda Fati kuma ta kawo mana kayan abimci. to da su na had'a aka siyo kayan Danwake.
Amma na da kwana biyar da Dawowa gida na cigaba da sana'armu ta Danwake ranar farko da ya aiko sai nace a maida masa da kudinsa. Ya ki karba yace a dawomin da shi sai na saka Hijabi na fita da kaina nace masa don Allah ya bar kudinsa.
Kai tsaye yace"Hasiya duk sanda zan aiko siyan danwake ki karbi kudi nace."
Yadda ya yi mganar ne yasa ban isa na yi gaddama ba a muryansa ya na da wani abun da in ya ce abu baka iya masa gaddama.
Ya rage yawan shigowa Duba Amma bai wuce a sati sau daya ba.
Sai dai in ya aiko siyan Danwake sai yace"a gaida masa Hasiya mai Danwake"
In ko bai aiko ba ranar haka zan wuni cewa ma Amma''Yau fa bai zo ba Amma ko lafiya?
Sai Amma tace ya na lafiya kila wani abu ne ya tsaidasa.
Ina jinsa a raina kamar wani yayana Ban ko iya kiran sunansa sai dai nace shi.
Habiba ko Hamma ta ke kiransa Sosai muka saba da shi.
Matan gidanmu har sun fara Tsegumi tunda Kaltume har tareni tayi da tambayan shine Sabon Surukin na su?.
Kai Tsaye nace mata"A'a wannan Dan'uwan mu ne"
Daganan na kashe bakin munafukai ammh nasan ana nan ana lura da ni ana jiran aji wata mgana ne a tare shi da Labarina.
Bai taba tambayanta komai game dani ba, sai dai ya taba cewa"ina baban ku? Nace masa ya rasu da Dadewa."
Sai yace"ina dangin mahaifin na ku?
Sai nace masa suna nan. Daganan bai kara min wata tambaya ba, sai dai suna Hira da Amma har sunan gidanmu ta fad'a masa na Anguwan Kona.
Sannan in suna Hira ta kan fad'a masa ita bafullatanan Gadan mallam mamman ce, aure ya kawota zariya.
Sannan mu mun dauka da gaske Abubakar maraya ne ba shi da kowa.
Ina jin dadi in nagansa ya zo ina jinsa kusa da zuciyata.
Ban san me yasa na Damu da shi Fiye da kaina ba.
Bansan wata irin kaddara ce ke shinshina a tare da Mutumin da ban Dade'da sanin sa ba.
Kaddarace mai girma Hasiya.
Girman kaddaran da zata iya sanadiyar shigan ku Tsaka mai wuya.
.*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*
Albishirinku ya yan'uwana An-Nisa! Ina wacce ta dade tana amfani da Sabaya amma bata ganin aikinsa duk kuwa irin shan da take masa ? To share hawayenki tamu Sabayar ingantacce ne wanda muka sake bakin aljihu muka zuzzuba kayan gyaran jiki wanda bana cutarwa ba infact shi wannan hadin 2 in 1 ne…. Hadin SABAAYA da ADUMULMULA, in kina fama da matsalar zubewar Nono to wannan had'i naki ne, in kinaso ki cicciko fatarki tayi kyau ki koma tamkar ‘yar yarinya to ki riki wannan hadi namu… Aikinsa bai tsaya iya nan ba hatta da kara lafiyar garkuwar jiki yanayi da kuma kara ni'ima…kowa na iya shansa, matan aure, Masu shayarwa in kin kusa yaye, 'yan mata, babba da yaro, maza da mata kowa na iya amfani da wannan hadi namu…. Muna maraba da mai siyan daya ko sari.
Abangare guda kuma muna had'a magani ingantacce na ciwon sanyi da yaki jin magani, in aka daure ana amfani dashi ana dacewa bi'izinillahi ta'ala, kai hatta da maganin hawan jini da diabetes duk muna saidawa kuma ana dacewa in sha Allah.
Atuntubemu tanan whatsApp or call 📞 07065481260.. Don Allah don annabi in kin san ba siya zakiyi ba kar kizo ki bata mana lokaci da tambayoyi please kayayyakinmu original 💯ne babu algus
*Janafty*
*TSAKA MAI WUYA.*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
_Masu bukatar a tallata musu Hajojojinsu cikin Farashi Saukakakke 09069067488_
*16*
*GUSAU.*
Dakyar Innani ta bari Sultana ta yi sati daya a gidan mahaifinta tare da yan'uwanta.
Dafe ta yi ta kasa ta tsare yarinya taje domin ganawa da mahaifinta sannan ta samu zama da yan'uwanta, Ammh innani ba ta bari ba, ta na tare da Sultana kafa kafa kamar wacce za'a yi ma wani abun cutarwa.
Daga matan har shi kan shi Shitun ba su da mafita sun fi kowa sanin Halin Innani don ta fito ta tara su ta tsine musu to abu ba ne da zai zama mai wahala awajenta ba.
Hakanan suka rika Hakuri da ita ammh abu kad'an sai ta yi Allah ya isa akan Bakincikinsa da na matansa ya kashe mata Hauwa kulu akwai Hisabi Tsakaninsu Ranar gobe kiyama.
Sannan ta hana Shitu ya gana da yarsa da ya saka a ka kirata zai ga Innani tare da ita kafa kafa. Sai masifa ta ke yi ta na fad'in uban me zai kuma gayamata? Ba ta son iskanci da neman mgana da munafunci.
Dole Shitu ya kama kansa ya na ji ya na gani Sultana ta koma batare da mgana ta tsakanin Uba da yarsa ta shiga Tsakaninsu ba.
Sannan ranar da zasu koma Gusai Abba ya Turo Direba ya Dauke su Mallam Shitu iya karfinsa ya yi ma Innani da Sultana Hidima ammh sai Innani ta rika fad'in" Dama baka wahalar da kanka ba Shitu. komai da ka sani Sulaimanu na yi ma yarinyar nan babu abunda ta nema ta rasa, Sulaimanu da ka ke gani kudi garesa shiyasa ba mu rasa komai ba."
Ammh ta na jin kannen Sultana na fad'in zasu zo suyi mata Hutu wani Lokacin in suka samu Hutun makaranta karaf Innani ko tace"A'a ku yi zaman ku, wannan ai dora ma mai kokari wahala ne. wato kun ji nace Sulaimanu na da kudi shine za'a zo kwada'yi ko? To shima ba shi da komai Rufin asirin Allah ne ina ma laifi an Dauke muku wani Laluran? Wannan yarinyar Sulsana ko bante ubanku bai taba siya mata ba Sulaimanu ne da Salamatu. Allah dai ya biya su da Aljannah"
Shitu da Matansa da suka amsa da Ameen Innani dai ta rika masifan kada su so zl sulaimanu ba shi da komai sai Rufin asirin Allah.
Ammh tace su bari Bad'i in an tsaida lokacin bikin Magajin gida da Sulsana sai su zo.
Ba wanda yasan da labarin yanzu za'ayi auran Sadiq da Sultana ammh zuwan Innani Shinkafi labari ya bazu a kunnen kowa.
Har gidan su Baba Sammani da ta je duk haka ta rika ce musu bikin Magajin gida da Sulsana bad'i in sha Allahu. Shitu ma daki ta saka shi ta na fad'a mai cewa gwara ya fara Tanadi tun yanzu Sulaimanu dai ya yi masa na Allah ya yi masa na Annabi. In kuma ba na Shed'an ya ke jira ba sai ya nemi kudin aurar da yarsa Ina za su iya? Tunda shi Ubanta ya na raye? Daman ya mutu ne sai su Dauki na Musulunci su yi."
Shitu dai mamaki ya kamasa ya san da mganar auran Abubakar da Sultana ammh bai san da mganar nan kusa ba. Suna yawan mgana da Abubakar yaro ne mai hankali natsuwa da sanin yakamata wanda ko Alhaji Sulaiman ba su cika mgana da shi kamar yadda suke yawan mgana da Sadiq ba.
Ya na da tabbacin Innani ta zauna ta Tsara mganarta. Shiyasa a lokacin ya kalli Innani ya na fad'in"Ammah Innani Alhaji Ya fad'amin sai Sultana ta gama makaranta za'ayi bikin Lokacin shima Abubakar din ya gama karatunsa har ya kama aiki."
Ai sai Innani ta Zabga masa Dakuwa kafin tace"Allah ya tsine ma karatun albarka. Ka ji min ja'iran ci da lalacewa irin ta Shitu? A na mganar sunnar ma'aiki ka na mganar karatun Bokon tusa da tsiya? Maza ka yi istigifari domin ka yi sabo wajen Ubangiji."
Na cigaba sa sana'ata in yana so zai aiko a siya mishi.
Lura da na yi bayason gaddama yasa na amsa masa da Toh.
Habiba na Tura kasuwa ta yi mana Cefane tunda da Adda Rukkaya ta zo gida kara Duba Amma dubu biyar ta bani Adda Fati kuma ta kawo mana kayan abimci. to da su na had'a aka siyo kayan Danwake.
Amma na da kwana biyar da Dawowa gida na cigaba da sana'armu ta Danwake ranar farko da ya aiko sai nace a maida masa da kudinsa. Ya ki karba yace a dawomin da shi sai na saka Hijabi na fita da kaina nace masa don Allah ya bar kudinsa.
Kai tsaye yace"Hasiya duk sanda zan aiko siyan danwake ki karbi kudi nace."
Yadda ya yi mganar ne yasa ban isa na yi gaddama ba a muryansa ya na da wani abun da in ya ce abu baka iya masa gaddama.
Ya rage yawan shigowa Duba Amma bai wuce a sati sau daya ba.
Sai dai in ya aiko siyan Danwake sai yace"a gaida masa Hasiya mai Danwake"
In ko bai aiko ba ranar haka zan wuni cewa ma Amma''Yau fa bai zo ba Amma ko lafiya?
Sai Amma tace ya na lafiya kila wani abu ne ya tsaidasa.
Ina jinsa a raina kamar wani yayana Ban ko iya kiran sunansa sai dai nace shi.
Habiba ko Hamma ta ke kiransa Sosai muka saba da shi.
Matan gidanmu har sun fara Tsegumi tunda Kaltume har tareni tayi da tambayan shine Sabon Surukin na su?.
Kai Tsaye nace mata"A'a wannan Dan'uwan mu ne"
Daganan na kashe bakin munafukai ammh nasan ana nan ana lura da ni ana jiran aji wata mgana ne a tare shi da Labarina.
Bai taba tambayanta komai game dani ba, sai dai ya taba cewa"ina baban ku? Nace masa ya rasu da Dadewa."
Sai yace"ina dangin mahaifin na ku?
Sai nace masa suna nan. Daganan bai kara min wata tambaya ba, sai dai suna Hira da Amma har sunan gidanmu ta fad'a masa na Anguwan Kona.
Sannan in suna Hira ta kan fad'a masa ita bafullatanan Gadan mallam mamman ce, aure ya kawota zariya.
Sannan mu mun dauka da gaske Abubakar maraya ne ba shi da kowa.
Ina jin dadi in nagansa ya zo ina jinsa kusa da zuciyata.
Ban san me yasa na Damu da shi Fiye da kaina ba.
Bansan wata irin kaddara ce ke shinshina a tare da Mutumin da ban Dade'da sanin sa ba.
Kaddarace mai girma Hasiya.
Girman kaddaran da zata iya sanadiyar shigan ku Tsaka mai wuya.
.*Littafin TSAKA MAI WUYA paid book ne, iya Book 1 ne free Pay N500 For BOOK 2,3. Regular group or VIP GROUP N1000. Via 0552179550 Jamila Umar gt bank.*
*Shedar biya ta wad'anan lambobin 09069067488 or 08032773332.*
*SPECIAL GROUPS Follow@Jamilaumarjanafty On AREWABOOKS mutanen mu na Niger za su Tuntubi Kausar Aglan nissa +22796562223 Nagode*
Albishirinku ya yan'uwana An-Nisa! Ina wacce ta dade tana amfani da Sabaya amma bata ganin aikinsa duk kuwa irin shan da take masa ? To share hawayenki tamu Sabayar ingantacce ne wanda muka sake bakin aljihu muka zuzzuba kayan gyaran jiki wanda bana cutarwa ba infact shi wannan hadin 2 in 1 ne…. Hadin SABAAYA da ADUMULMULA, in kina fama da matsalar zubewar Nono to wannan had'i naki ne, in kinaso ki cicciko fatarki tayi kyau ki koma tamkar ‘yar yarinya to ki riki wannan hadi namu… Aikinsa bai tsaya iya nan ba hatta da kara lafiyar garkuwar jiki yanayi da kuma kara ni'ima…kowa na iya shansa, matan aure, Masu shayarwa in kin kusa yaye, 'yan mata, babba da yaro, maza da mata kowa na iya amfani da wannan hadi namu…. Muna maraba da mai siyan daya ko sari.
Abangare guda kuma muna had'a magani ingantacce na ciwon sanyi da yaki jin magani, in aka daure ana amfani dashi ana dacewa bi'izinillahi ta'ala, kai hatta da maganin hawan jini da diabetes duk muna saidawa kuma ana dacewa in sha Allah.
Atuntubemu tanan whatsApp or call 📞 07065481260.. Don Allah don annabi in kin san ba siya zakiyi ba kar kizo ki bata mana lokaci da tambayoyi please kayayyakinmu original 💯ne babu algus
*Janafty*
*TSAKA MAI WUYA.*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
_Masu bukatar a tallata musu Hajojojinsu cikin Farashi Saukakakke 09069067488_
*16*
*GUSAU.*
Dakyar Innani ta bari Sultana ta yi sati daya a gidan mahaifinta tare da yan'uwanta.
Dafe ta yi ta kasa ta tsare yarinya taje domin ganawa da mahaifinta sannan ta samu zama da yan'uwanta, Ammh innani ba ta bari ba, ta na tare da Sultana kafa kafa kamar wacce za'a yi ma wani abun cutarwa.
Daga matan har shi kan shi Shitun ba su da mafita sun fi kowa sanin Halin Innani don ta fito ta tara su ta tsine musu to abu ba ne da zai zama mai wahala awajenta ba.
Hakanan suka rika Hakuri da ita ammh abu kad'an sai ta yi Allah ya isa akan Bakincikinsa da na matansa ya kashe mata Hauwa kulu akwai Hisabi Tsakaninsu Ranar gobe kiyama.
Sannan ta hana Shitu ya gana da yarsa da ya saka a ka kirata zai ga Innani tare da ita kafa kafa. Sai masifa ta ke yi ta na fad'in uban me zai kuma gayamata? Ba ta son iskanci da neman mgana da munafunci.
Dole Shitu ya kama kansa ya na ji ya na gani Sultana ta koma batare da mgana ta tsakanin Uba da yarsa ta shiga Tsakaninsu ba.
Sannan ranar da zasu koma Gusai Abba ya Turo Direba ya Dauke su Mallam Shitu iya karfinsa ya yi ma Innani da Sultana Hidima ammh sai Innani ta rika fad'in" Dama baka wahalar da kanka ba Shitu. komai da ka sani Sulaimanu na yi ma yarinyar nan babu abunda ta nema ta rasa, Sulaimanu da ka ke gani kudi garesa shiyasa ba mu rasa komai ba."
Ammh ta na jin kannen Sultana na fad'in zasu zo suyi mata Hutu wani Lokacin in suka samu Hutun makaranta karaf Innani ko tace"A'a ku yi zaman ku, wannan ai dora ma mai kokari wahala ne. wato kun ji nace Sulaimanu na da kudi shine za'a zo kwada'yi ko? To shima ba shi da komai Rufin asirin Allah ne ina ma laifi an Dauke muku wani Laluran? Wannan yarinyar Sulsana ko bante ubanku bai taba siya mata ba Sulaimanu ne da Salamatu. Allah dai ya biya su da Aljannah"
Shitu da Matansa da suka amsa da Ameen Innani dai ta rika masifan kada su so zl sulaimanu ba shi da komai sai Rufin asirin Allah.
Ammh tace su bari Bad'i in an tsaida lokacin bikin Magajin gida da Sulsana sai su zo.
Ba wanda yasan da labarin yanzu za'ayi auran Sadiq da Sultana ammh zuwan Innani Shinkafi labari ya bazu a kunnen kowa.
Har gidan su Baba Sammani da ta je duk haka ta rika ce musu bikin Magajin gida da Sulsana bad'i in sha Allahu. Shitu ma daki ta saka shi ta na fad'a mai cewa gwara ya fara Tanadi tun yanzu Sulaimanu dai ya yi masa na Allah ya yi masa na Annabi. In kuma ba na Shed'an ya ke jira ba sai ya nemi kudin aurar da yarsa Ina za su iya? Tunda shi Ubanta ya na raye? Daman ya mutu ne sai su Dauki na Musulunci su yi."
Shitu dai mamaki ya kamasa ya san da mganar auran Abubakar da Sultana ammh bai san da mganar nan kusa ba. Suna yawan mgana da Abubakar yaro ne mai hankali natsuwa da sanin yakamata wanda ko Alhaji Sulaiman ba su cika mgana da shi kamar yadda suke yawan mgana da Sadiq ba.
Ya na da tabbacin Innani ta zauna ta Tsara mganarta. Shiyasa a lokacin ya kalli Innani ya na fad'in"Ammah Innani Alhaji Ya fad'amin sai Sultana ta gama makaranta za'ayi bikin Lokacin shima Abubakar din ya gama karatunsa har ya kama aiki."
Ai sai Innani ta Zabga masa Dakuwa kafin tace"Allah ya tsine ma karatun albarka. Ka ji min ja'iran ci da lalacewa irin ta Shitu? A na mganar sunnar ma'aiki ka na mganar karatun Bokon tusa da tsiya? Maza ka yi istigifari domin ka yi sabo wajen Ubangiji."