← Book details Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 69

Sashe 36

Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

Shi kuma abu na biyun da ke damuna Salisu ne! Ya na yawan Fad'omin a rai a kwanaki nan jiya har mafarkin sa nayi. Wai mun had'u na gaishe shi ya ki amsawa naga Musabahu a wajen da ya ce masa"Salisu Hasiya ce fa ke gaisheka ka yi kamar baka ji ba."
Kai tsaye naji muryan Salisu na Fad'in"Bazan amsa mata ba Musbahu koma miye faru. Bai kamata na kwanta Jiya Hasiya taki gaisheni ba."
Daganan na farka ina ta faman zufa. Tun daga lokacin zullumi na ya karu akan na baya. A bakin Mamam boy nake jin sun koma asibiti an kara Dubashi an ce sai karfen jikinsa ya shekara za'a cire masa.
Maman boy Idon gari ce ka rasa ina take samun wasu labaran, ko da ya ke Gantali ce da ita ba inda kafarta baya shiga da mijinta ya fita itama ta ke saka kafa ta fita kusfa kusfa a samaru nan anguwar Tsamiya Da'i da'i kun gidaje ne Maman boy ba ta shiga ba. shiyasa akwai labaran gidajen mutane da dama abakinta.
Nasan ko giyan wake na sha ban isa na dauki Siraran kafafuwana zuwa gidan Salisu da sunan gaishe shi ba. na tabbata Sahura sai ta kasheni kamar yadda ta kudurta in kuma ban mutu ba to tabbas zan samu manyan Rauninka da zan jima cikin Doguwar suma. tuna haka kad'ai kan kwabar da Niyyata ko Amma na kasa gayamata zuciyata duk da ta ganni suku suku da ta tambayeni sai na ce mata ban jin dad'i da Safen ne.
Amma na da  wani irin hali ko ya ya na ke cikin damuwa ta sani sai da ta kalleni cikin Nazarina kafin ta kad'a kai tana fadin"Ko ulcer d'in ki ce zata tashi?
Kai tsaye nace mata"In ma itace ina da Sauran magunguna na ruwa da na kwayar sai na sha."
Kai tsaye itama tace min"In bazaki Jefa Danwaken nan ba a hakura yau Hasiya."
Ban bari ma na ja mganar da ita ba. Taga na mike na fara had'a kayan yin Danwaken sai ba ta kara mgana ba Ammh ta jima ta na kallona ta kuma san tabbas wani abu na Damuna to ta ina ma zatayi Tunanin bazan damu ba. Damuwa a gareni ta zama Tilas ko domin yadda na zama abun gudu da kyama wajen jama'a.
Ramatu na ke son gani ko zan gayamata cikina ta ba ni shawara, Shiyasa ina gama wanke wanken kayan da na bata, bayan na kai Daki na zo na saka ruwan zafi a rushin da na rage na leka Dakin Maman Boy nace ta aramin wayarta zan kira Ramatu.
Kai tsaye tace min"Gaskiya ba kudi acikin wayar"
Cikin mamaki nace mata"Ba kud'i? Ba shekaranjiya na saka Dari da zan kira Adda Fati ba? Kuma ba mu jima mu na mgana ba. Na dai san ban isa cinye wannan Darin ba."
Cikin tabe baki tace"To ni dai bansani ba, ban kira kowa da shi ba."
Ban kara mgana ba Na karb'i wayar na juya ban ko tsaya duba kudin wayar ba na leka kofar gida na kira Salihi na Dauki Naira dari da goma cikin cinikin Danwake na ce ya ruga ya siyomin Katin Mtn ya yi Sauri.
Sanin Halin Salihi da aikensa da sai ka mamta da shi ya ke dawowa yasa na koma Daki na fara kanta shi zan gyara Amma na saman gadonta barci ya kwasheta itama duk sai a hankali kwanaki nan da zazzabi ta ke kwana.
Har sai da na gama na share daki na wanke bayi saboda bazan iya shigarsa haka batare da na wanke ba. Na juye ruwa na yi wanka na fito na sauya kaya sannan Salihi ya dawo, Allah ya taimakeni ma ya kawomin katin lafiya.
Ina gama Loda katin na kira Ramatu daman na Haddace lambarta bayan ta Dauka mun gaisa da tambayan su Amma da Noor nace"Ke ina son ganinki kina gida gobe..?
Da zumud'i tace"To ni kuma ai goben nake shirin zuwa miki Yini ni da Noor. Gidan Inna zan kwana da Sassafe tahowa kawai zan yi"
Cikin jin dad'i nace"To shikenan ma sai kin zo d'in. Ki gaida inna Talatu"
Kai tsaye tace"Zata ji nima ki gaidamin da Amma da Habi auta."
Daganan muka yi sallama. Jin tace zata zo sai naji dadi a raina.
Ban koma na zauna ba sai da na Mayar ma Maman boy wayarta sannan na dawo na saka Danwake da manja da maggi naci.

Ganin Amma nata barci yasa na kwashe yan kayanta da suka yi datti na Daureye mata da nawa na aikin Danwake. Kayan ba su da yawa tunda wanchan Sati Habi ita tayi mana wankin kayan duka ranar Sati tunda ba makaranta.
Su datti na bama goma goma suka Debemin ruwa a waje. Ina mamakin yadda matan gidanmu ba su damu da sanya yaransu a makaranta ba sai dai su bar su su yi ta gararamba a gari ba arabi ba boko. Na taba yin musu mgana Maman Salihi tace min da na abinci za su ji ko da na kudin makarantarsu daganan sai na Rufe bakina. Duk da sai ayi abu Dari ban saka bakina ba yanzu sai kiji gori na tashi ni da ke da ababen gori gasusan kaca kaca.
Kwanakin nan ma da na ga Kaltume na jin Haushina daga ni har Amma bata kulamu kawai saboda mijinta na son Danwake na,ya kan siya ya ci kafin ya fita sai ta fara adawa da ni kai Tsaye kuma ta same ni ta min mgana cewa bata son na kara saida ma Mijinta Danwaken mu in tace bata so kawai a barshi kada rayuka su baci.
Amma na jin haka tace a barshi kawai saboda Kaltume ba ta tsoron Tijara Tundaga ranar ban kara saida masa ba ko ya aiko zan ce gabadaya an siye shi ba bu. Daganan na samu lafiya,ammh har alokacin bata daina min gani gani ba ita a tunaninta kada Mijinta yace ya na sona na saka ta uku ni kam a raina nace ta ya ya zai ce ya na sona? Shi kan shi ai baya so ya shiga cikin ukun ba.

*****
Chapter 36 · 0% Book details