← Book details Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 54 OF 69

Sashe 54

Tsaka Mai Wuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shitu dai ya ga abun mamaki ta wani bangaren kuma bai yi mamaki ba Tun kuluwa na raye sun sha zuwa Innani ta saka su a gaba ta yi masa wankan Tsarki. Wani lokacin tun Safe ta ke musu Dirar mikiya ka yi mgana ta tattara Tsinuwan bakinta a kanka shiyasa da yasan halinta sai yaci mganin zama da ita. Haka sauran matan masa ma tunda ba yau suka san Innani ba.
Haka suna mota da zasu koma Innani sai faman ciye ciye ta ke yi. ta na cewa su Hassu ba su da kirki sai ga shi ita ba ta kai musu komai ba ammh duk abunda suka bata sai da ta amsa. Aya ko ta yi tiya uku Wacce Innani ta zo da shi. Tsohuwar nan yar bala'i ce ba ta da hakora ammh sai Uban kwad'ayi da son abun duniya. Innani fa har goriba da rake ta ke sha, Wuka ta ke samu ta yi ta kankarewa ta na afawa a baki da hakoranta na Roba ta ke Taunawa.
Yanzu ma Aya ta ke ci sai faman mayau mayau ta ke da baki Direba ya fara Gudu Innani ta fara salati ta na Ihun ya rage gudu. Kuma ba fa gudu ya ke yi ba. Innani ta rika masifa har ta na kukan sai ta gayama Sulaimanu zai kashe masa uwa.
Sai Direba ya juyo ya na fad'in"Innani ba fa gudu na ke yi ba. a tamanin fa na ke tafiya."
Innani ta dake ta karfi tace"Allah ya Tsine ma maka kai da tamanin din. ni zaka raina ma wayau? In ni ba tsohuwar ka bace ka raina ni ai ka Daraja Furfuran tsohon ka ko?
Ya na jin haka bai kara mgana ba Sultana da ke ta kuka tun tahowarsa ta kallah cikin kufuluwa tace"Ke kuma kukan Uban me ki ke yi?
Sultana ta kalli Innani cikin Takaicinta kafin tace a hankali"Sati uku Fa Umma ta ce zan yi Innani.."

Innani sai ta saki baki ta na kallonta cikin mamaki kafin ta Dungure mata kai lokaci daya ta na fadin"Ta fi chan mara wayau ni gata na yi miki baki sani ba. Shitu da ki ke gani mugun bawa ne, da matan nan nasa ina barin ki cikin su sai kuma abunda Allah ya yi." Sai ta fara kuka ta na fad'in ke kad'ai kuluwa ta mutu ta barmin ta ina zan bari a nakasa min ke."
Bakinciki suka Hana Sultana mgana.
Ko da ta ke da kananun Shekaru ta san Ubanta ta kuma san yan'uwanta kuma ta na son su da kaunar su ba tun yau ba tasan Innani ba ta kaunar Abbanta ta sha zaginsa a gabanta tun bata damuwa har ta kai ga yanzu abun na yi mata ciwo.
Har suka iso Gusai Innani sai mugun Mgana ta ke fad'i akan Shitu har da tsohon Labarin aura auren da ya kara Saboda Kuluwa bata Haihu ba. Sultana kunnenta ta toshe ba ta son ji.
Saboda in dai Hadda ce ta rika gama haddace wad'anan Labaran.
Ko su kan su Umma sun sha mamakin ganin dawowarsu Sati d'aya kacal.
Da Umma ta yi mgana Innani ta harzuka tace"To uban me zamu tsaya yi!? Ina laifi ma an yi zumunci."
Daganan ta kama bakinta Mama ko tak bata ce ba Tunda taga yar gaban goshi Umma ta samu rabonta ta tabbata ta yi mgana sai Innani ta Taso mata.

Da Abba ya dawo bai ko yi mgana ba. Shi fa Ra'ayin Innani ne na sa Ra'ayin Magajin gida ne kawai cewarsa da Ra'ayinsa ke kan na Innani.
Innani bata yi mganar bikin Magajin gida da Sultana da ta gama bazawa a Shinkafi ba. Ta bari ne sai ta samu zama da Sulaimanu kawai ta gayamasa bad'i ta ke son ayi auran nan ta matsu ta ga ya'yan Magajin gida hakanan
Umma ta fara ji tunda Matar Baba Sammani Madiha ta kirata ta ke tambayan ya su Innani su ka koma gida? Daganan kuma sai ta ke tambayan Umma ashe biki kuma ya zo.
Cikin mamaki Umma tace bikin wa? Madiha tace na Magajin gida da Sultana mana, nan ta kwashe mganar Innani ta fad'aa mata Umma tace to bata san da mganar ba ammh za ta yi ma Abba mgana in ma da bikin za su fad'a musu.
To shima Abba Shitu ya kirasa ya masa zencen yace masa sai ya koma gida sun yi mgana da Innani Tukunna.
Sai a kayi sa'a Umma ke da Turaka ranar sai ta samu lokacin Tambayansa ko sun yi mgana da Innani? Abba yace a'a. Me ya faru? Sai da ta gayamasa ne shima yace sun yi mgana da Shitu.
Umma ta yi shuru kafin tace"Abban Siyama ka na ganin in muka ce Auran nan ya taso ba mu yi gaggawa ba? Sannan ba mu ji Ra'ayin Auta akan mganar ba."
Abba yace"Kada ki damu. Abunda Innani ta ke so shi za'ayi Salamatu. Innani ta tsufa a kwai rikicin Tsufa tare da ita gwara na samu na Rabu lafiya da ita."
Umma ta jinjina kai kafin tace"Duk na san da wannan. Ammh ta ya ya za su yi aure Sultana karamar yarinya ce. sannan Auta bautar kasa ya ke yanzu bai ko kama aikinsa a hannu ba. Sannan bamu san Wani Tsari ya ke da shi nan gaba ba. ni na dauka sai ta gama makaranta shima kafin lokaci ya san in da ya kama Abban Siyama."
Abba ya yi mirmishi kafin yace"Nima haka na so da farko. ammh ya zan yi da Innani salamatu?
Umma sai ta yi shuru ammh tasan in su ba su isa ba. Wanda ya isan zai ji kuma zai dakatar da ita, Shiyasa ta bar mganar.

Washegari da Safe gabadayansu a Shashen Innani suka karya daman Haka suke yi ranar aikin Umma. Salima ce kad'ai ke zuwa makaranta ita Direba ya dauka Sultana kuma da Siyama SS1 zasu shiga Tukunnah.
Bayan sun gama Sultana da Siyama suka kwashe komai suka fita suka bar iyayen na su su zanta.
Innani tun safiyar Allah sai Bare naman kaza take sala sala ta na ci Kai Tsohuwar nan akwai rikici a lamarinta.
Gabadaya a gabanta suka Durkushe Umma da Abba sai Mama achan gefe. Abba ne ya fara kora mata jawabin kiran Shitu Innani ta saki naman kazan hannunta ta na salati har da tafa Hannu ga gilashinta da ya kusa cika mata Fuska ta na fadin"Na shige su ni Dije? Ashe Shitu Annamimi ne ban sani ba? ni zai yi ma makirci da Tuggu?
Umma tace"Subhanallah Innani ba Makirci ba ne ya kira ne yaji tabbaci."
Innani tace"Tabbacin Uban me? Zan masa karya ne shi Sulaimanun ina ce ba ni ce uwarsa ba?
Umma tace"ke ce Innani har mu ma ke ce mahaifiyar mu ba mu da kamar ki."
Sai Innani ta ji sanyi ta Sassauta Murya ta na fad'in"To shi ne shi ya ke Tunanin na yi masa karya ko? To ba karya ba ne da gaske ne Bad'i na ke son a yi auran magajin gida da Sultana."
Falon na Innani ya Dauki Shuru Umma ta kalli Abba ta na masa inkiyar ya yi mgana.
Sai ya muskuta ya na fad'in"Innani..Dama.."
Innani ta Dakatar da shi da Fad'in"Sulaimanu nace bad'i uwar haka naga Yarinyar nan Sulsana a dakin magajin gida ba na son wata mgana."
Da Sauri yace"Shikenan Innani yadda kika ce haka za'a yi."
Umma ta kallesa shi kuma sai ya kasa kallonta. Mama ta matsonta mata mgana a Hankali" Umman su ki yi mgana mana."
Karaf ko Innani ta gani ta balla mata Harara ta na fadin"wata gulmar kuma ki ke gayamata? Kin ga Suwaiba ki Fita idona kafin na ci miki Mutumci."
Da Sauri Mama tace"A'a Innani ina ce mata ne ta tambayeki wani wata ne za'a saka na bikin?
Innani ta kura mata ido kafin ta tabe baki tace"ke dai kika sani."
Daga haka ta cigaba da zare sala salan kazanta ta na tura a baki ta na ci.
Umma taga gwara ta yi mgana kafin komai ya zo ya kwabe.
Sai ta gyara zama ta na fadin"Innani.."
A Fusace tace"Mi ye wai ku ke ta kiran Sunana.?
Umma tace"Daman naga kin sauya ra'ayi ne. ni dai nasan a baya mun gama sai Sultana ta gama makaranta lokacin ta kai shekara sha takwas shima Auta ya gama bautar kasarsa har kila ma ya fara aiki kafin mganan auran na su ya taso."
Innani ta rika ballama Umma Harara ta na tabe baki kafin tace"Suwaiba ce ta kitsa miki ki ce min haka ko Salamatu?
Mama ta zaro ido ta na kallon Umma ita kuma da Sauri tace"Wlh a'a. innani."
Innani kamar bazatayi mgana ba Abba ta kallah kafin tace"Baka gayama matanka Umarnina na gaba da Umarnin kowa ba ne?
Da Sauri yace"Haba sun sani Innani. Su san Umarnin ki shine nawa Umarnin."
Kai ta gyad'a kafin tace"To ashe sun sani ke salamatu ban san me ya shiga kanki ba ki ke biyema Suwaiba da Munafuncinta ba, Ki yi ma murna magajin gida zai yi aure ko kema zaki ga jokokin ki."
Umma tace"Innani jikoki nawa garemu a gidan nan?
Kai Tsaye Innani tace"Ban gan su baa"
Mama ta yi karaf tace"Innani ba ki gan su ba? Kaf ya'yaan mu duk sun haiyyafa. Suma ai jokokin ki ne.".
Innani ta Daka mata tsawa ta na fadin"Ke ne zaki wani gayamin ya'yan ku sun haiyayyafa ce miki na yi ban san sun haihun ba ne? Ba na son tsirfa da Tsugudidi Suwaiba ba na so na gaya miki.
Sai Mama ta koma gefe ta na fad'in"Allah ya baki hakuri Innani."
A fusace tace"Ameen in da gaske kike yi."
Sai falon ya Dauki Shuru Umma na Tsoron sake mgana a taso mata Abba kuma na zaune kanzil bai kara cewa ba.
Chapter 54 · 0% Book details